Sashe 74
Da Ciwo A Zuciyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gabanta sai da ya yanke ya fadi, a dan rikice take kallon kanta tun daga sama har kasa,
Watau dama aunty ba wani tsayi ne da ita ba, kuma tana da jiki hakan ya sa rigar Tata ta shigi Khausar, sai dai ta je cen daidai da dima diman cinyoyinta ta wani hau take budewa idan tana tafiya
A raunane Khausar ta hadiye yawu mai wahala tana jin nauyin shigar Tata, da dan sauri ta karasa kofar dakin ta ayana magana kamar haka' zan shiga in yiwa marar lafiyan allurar sai in koma gida, idan na je sai in dauki wayar Baba in kirashi mu yi magana kawai, sai ya zo mu daidaita ya bani takardar kawai'
A nutse ta bude dakin bayan ta dan buga kadan sannan ta yi salama kasa kasa sosai, dan wannan din shine dabi'arta, koda tana likita tana kiyaye hakin mutane, bata cika irin shigowar nan kai tsaye fuska daure ba ta wasu likitocin, takan dan buga ta dan yi jim, sannan ta bude ta shiga da sallama a hankali duda ta san nurse zata tarar sai marar lafiyar dan kuwa yanzun ba lokacin shigowa gannin mararsa lafiya bane, sai an jima kusan sha biyu na rana ake budewa a bada damar ziyara, karfe uku kuma a rufe sai shigar sasafe karfe shida zuwa takwas rufe
A hankali ta ja ta tsaya idannuwanta suka sauka a kan fuskarsa da kuma wace ke kwonce tamkar babu rai a jikinta, ga dukkan alamu barci ne take yi mai nauyin gaske
A hankali Khausar ta lumshe idannuwanta gannin shi bashi da niyar kautar da nasa duban a kanta, kamar yadda ya saba a da cen, a kanta yakan dan jima yana kallonta , sai dai a da din bata dauki haka a bakin komai ba, yanzu kuwa sai take gannin hakan bai dace ba
A hankali ya dan yi gyaran murya ya mike daga saman kujerar da hannunsa ya mata alamun ta yi aikinta sannan ya koma bayanta sosai ya tsaya ya dauke kansa a kanta dan ya san wacece ita, bale sabon yannayin da ya ga ta ara tsaf take iya juyawa ba tare da ta yi aikin da ya kawota ba
Jiki ba karfi ta ajiye kwanon, sannan ta duka ta tsayar da gudun karin ruwan, ta daidaita allurar da ruwanta ta bude wajen da aka jona karin ruwan a hankali ta rike tsintsiyar hannun Yumnar ta shiga zuba mata ruwan allurar a hankali a hankali tana dan duba yannayinta domin allura ce mai zafi ba'a zugata zuuuuuuu ta tafi, kuma tana iya taba numfashin mutun ko ta saka shi amai ko muguwar juwa shi yasa ake yi a hankali ana hankalce da motsin mutun
Sai da ta gama saka mata ruwan allurar sannan ta maida mata karin ruwan
A hankali ta juya tana dan duba dakin dan gannin abin auna bugun zuciya
Dayan nan dai na wuyansa shine, ita kuma nata yana cikin rigarta da ta yar a cikin lft
Ajiyar zuciya ta sauke bayan ta karfafawa kanta gwuiwa cewar Besty ne fa, TAUFEEK ne fa, dilla menene a ciki
Ba tare da ta sake saka tsoro ba ta nufe shi tana aro jarumta tana yafawa kanta ta ce" Shin me yake damun Yumnah ne? Ban san bata da lafiya ba, dan bani abin nan na ga bugun zuciyarta"
Maimakun ya bata abinda take nuna masan sai kawai ya kama hannunta kiiiii ya fice da ita daga dakin
Jefa kafa take yi gabanta na faduwa domin bata san ina suka nufa ba, kuma irin yadda fuskarsa ta dauki ja alamun ransa a bace ko menene sai ta sake tsorata ainun har suka shiga lft suka sake hawa sama cen wajen office dinsa
Ko da lft din ya tsaya hannun nata ya cika ya yi gaba yana kunce abinda ke daure a jikin rigarsa na wuyansa dan ji yake yi tamkar zai tsaida masa numfashinsa ya dadana code din kofar office dinsa ya shige lokaci daya ya dauki commande din camarar bangarensu ya sakata a halin duhu sannan ya kurawa kofar ido yana jiran shigowar ta
KHAUSAR da ta gama summa a tsaye da kyar ta cira kafarta ta karasa office din
Rana shigowa ta ajiye farar rigar aikin domin itama du a rikice cire rigar ta yi ta tunkaro kusa da table din da yake tsaye kanta tsaye tana dubansa idannuwanta na cikowa da kwallah ta ce" Kana tunanin laifina ne?, TAUFEEK kana tunanin nice na saka su Aba aikata aikin nan?, Walahi walahi ban sani ba, nima na san ai na wani hadi, in kana tune ka min alkawarin kasancewa da Ni har a Daura aurena da .........."
"Khausar Please cn U be quiet?!" TAUFEEK ya fada a kasashen da ya saka Khausar zuba masa ido tana jin tamkar zata kifa a tsayen da take , shin yaya zata kwatanta masa cewar ba fa ita tace a daura mata aure da shi ba?
A nutse yana binta da kallo ya ce" sai yaushe zaki fara jin maganana ne? Menene wannan shigar? Ina hijab dinki? Me yasa kike son daukan dabi'ar da zata ringa bata min rai? Babu ruwanki a gaban kowa sai ki arta a guje ? Kina kallo muna tare da docter kika wani fita da gudu menene haka ne?"
Da mamaki take kallonsa, sai kuma ta kalli jikinta
A hankali ta shiga juyawa a gaban nasa har sai da ta juyo tana fuskantarsa a sanyaye ta ce" Menene laifin shigata? Me yasa kake son min fadan shigata ne bayan na san cewa harda ita a tsaikon samun mijina yanzu na kare da ......"
Ta yi shiru sakamakon zuba mata jajayen idannuwansa da ya yi yana sauraronta
Gannin ta yi shiru a hankali ya ce" Kika kare da me?"
Khausar ta dafe gaban goshinta, a hankali ta ja kujera ta zauna sannan ta mika hannunta ta kama bayan hannunsa dake jimke saman table din a tausashe dayan hannun nata kuwa ta bude abinda ke ajiye ta ciro tisu fari ta nufi gaban goshinta da shi a hankali tana share zufar da ta karyo mata kasa kasa ta ce" Dan Allah ka zauna, ka san ba son rikici nake ba, kuma baka san abinda ya faru ba ga dukkan alamu, ka zauna dan ina tsoron in na fada maka yanzu ka fadi, Taufeek its vry srius , ka zauna Please"
Hannunsa ya janye daga jikin nata, domin tunda ta dora din tana magana ne tana dan shafa bayan hannun nasa da sigar rarashi ba da wata manufa ba, wace sshi kuwa hakan ba daidai da yannayin da yake iya dauka bane
Da ƙafarsa ya dan tura kujerar baya ya zauna yana kallonta , a hankalin da sam bata so yana mata magana ya ce" Kika kare da me? Tl me"
"Na kare da auren aminina, abokina, freind dina, TAUFEEK basu fada maka aurena da aka daura da kai bane ko menene na ga ba maganar kake min yanzu ba?, TAUFEEK ka san cewa wai ashe Ni aka aura maka.....?" Ta fada tana watsa hannayenta hadi da dan zarro idannuwanta alamun ta fada masa tashin hankalin nan
Bakinsa ya dan tabe yana kauda dubansa ya ce" Eh haka na ji"
Khausar ta girgiza kai ta ce" Ka ji? Kennan ka ji? Ya Allah, da ka san irin yadda na yi ɓaci a kwana biyun nan da ka sha mamaki, TAUFEEK aminina?"
TAUFEEK ya zuba mata ido, ya dora hannayensa duka biyu yana dubanta ya ce" Eh, sai aka yi yaya?"
"ka kuwa ji me nace ne?" Khausar ta fada tana dubansa
TAUFEEK ya dan dantse lebensa da dan jin yana daf da kowa a wannan dogon maganar da tarin raini ke jagoranta tsakaninsa da Khausar ya ce" Eh na ji me kika ce, an daura maki aure da Ni, Ni amininki, nace eh sai mene kuma?"
Baki da ido da hanci ta bude tana kallonsa har ya mike ya nufi wajen frij din office din nasa ya ciro faro ya bude ya sha ya ajiye sauran cikin abin zuba shara dan bai shanye ba wanda ya rage din kuma kadan ne
Ya karasa ya dauki suturarsa kala blu mai haske wando da riga irin na likitoci wa'inda yake shiga dakin tiyata da su ya bale boturan rigar jikinsa ya cire rigar
A zabure Khausar ta mike tana kawar da kanta, sai kuma ta koma ta zauna ta sada kan nata tana dadana yatsunta tana addu'a kunnayenta na jiyo mata motsinsa alamun harta wandon a nan TAUFEEK ya saka har ta daina ji idannuwanta a rintse zufa na neman karyo mata sai kuma ta ji maganarsa daf da ita , a kamilance harufan bakinsa ke fitowa yana dubanta ya ce" igiyoyin aurena uku ke wuyanki, ina fatan zaki kula ba tare da kin takura min tabatuwarsu a kanki ba!, Ki kula na kasance mai jinkiri sosai, inada hakuri sosai, ama a kanki babu abinda bai sameni ba......Please Khausar ki dan sanyaya mana tafiyar , ko ba komai kin ce auren hadi ne, shi kuma ai sai an zauna shi ko? Kin dai san Ni ba marar kunyar da zan cewa su Aba wai yanzu yanzu zan bijire masu bane, in ke wuyanki ya rika ki je ki fada masu kawai sai a duba a ga abinda ya dace a yi......., Khausar My wife.........
A dan zabure ta dago ta zuba masa ido
TAUFEEK ya dan dantse lebensa kadan ya ce" my wife bata da lafiya, kin san ciki ne da ita, kuma ina tsoron laifinki ne....... ki dan yi zamanki a nan har a tashi kin ji?"
Yana gama fada ya saka hular a kansa ya dauki glasss dinsa ya mayar ya ajiye mata iphone dinsa a gabanta sannan ya wuce a office din, du a kokarinsa kar a fahimci irin takaicin da ta shaka masa, da kuma tunanin mema take nufi ne yarinyar nan da shi har ya karasa dakin tiyatar da ake daf da yiwa marar lafiyan allurar kashe jiki gaba daya a saka shi a duniyar barci dan aiki ne zasu masa su ciro masa ciwon kansar dake kansa
Watau dama aunty ba wani tsayi ne da ita ba, kuma tana da jiki hakan ya sa rigar Tata ta shigi Khausar, sai dai ta je cen daidai da dima diman cinyoyinta ta wani hau take budewa idan tana tafiya
A raunane Khausar ta hadiye yawu mai wahala tana jin nauyin shigar Tata, da dan sauri ta karasa kofar dakin ta ayana magana kamar haka' zan shiga in yiwa marar lafiyan allurar sai in koma gida, idan na je sai in dauki wayar Baba in kirashi mu yi magana kawai, sai ya zo mu daidaita ya bani takardar kawai'
A nutse ta bude dakin bayan ta dan buga kadan sannan ta yi salama kasa kasa sosai, dan wannan din shine dabi'arta, koda tana likita tana kiyaye hakin mutane, bata cika irin shigowar nan kai tsaye fuska daure ba ta wasu likitocin, takan dan buga ta dan yi jim, sannan ta bude ta shiga da sallama a hankali duda ta san nurse zata tarar sai marar lafiyar dan kuwa yanzun ba lokacin shigowa gannin mararsa lafiya bane, sai an jima kusan sha biyu na rana ake budewa a bada damar ziyara, karfe uku kuma a rufe sai shigar sasafe karfe shida zuwa takwas rufe
A hankali ta ja ta tsaya idannuwanta suka sauka a kan fuskarsa da kuma wace ke kwonce tamkar babu rai a jikinta, ga dukkan alamu barci ne take yi mai nauyin gaske
A hankali Khausar ta lumshe idannuwanta gannin shi bashi da niyar kautar da nasa duban a kanta, kamar yadda ya saba a da cen, a kanta yakan dan jima yana kallonta , sai dai a da din bata dauki haka a bakin komai ba, yanzu kuwa sai take gannin hakan bai dace ba
A hankali ya dan yi gyaran murya ya mike daga saman kujerar da hannunsa ya mata alamun ta yi aikinta sannan ya koma bayanta sosai ya tsaya ya dauke kansa a kanta dan ya san wacece ita, bale sabon yannayin da ya ga ta ara tsaf take iya juyawa ba tare da ta yi aikin da ya kawota ba
Jiki ba karfi ta ajiye kwanon, sannan ta duka ta tsayar da gudun karin ruwan, ta daidaita allurar da ruwanta ta bude wajen da aka jona karin ruwan a hankali ta rike tsintsiyar hannun Yumnar ta shiga zuba mata ruwan allurar a hankali a hankali tana dan duba yannayinta domin allura ce mai zafi ba'a zugata zuuuuuuu ta tafi, kuma tana iya taba numfashin mutun ko ta saka shi amai ko muguwar juwa shi yasa ake yi a hankali ana hankalce da motsin mutun
Sai da ta gama saka mata ruwan allurar sannan ta maida mata karin ruwan
A hankali ta juya tana dan duba dakin dan gannin abin auna bugun zuciya
Dayan nan dai na wuyansa shine, ita kuma nata yana cikin rigarta da ta yar a cikin lft
Ajiyar zuciya ta sauke bayan ta karfafawa kanta gwuiwa cewar Besty ne fa, TAUFEEK ne fa, dilla menene a ciki
Ba tare da ta sake saka tsoro ba ta nufe shi tana aro jarumta tana yafawa kanta ta ce" Shin me yake damun Yumnah ne? Ban san bata da lafiya ba, dan bani abin nan na ga bugun zuciyarta"
Maimakun ya bata abinda take nuna masan sai kawai ya kama hannunta kiiiii ya fice da ita daga dakin
Jefa kafa take yi gabanta na faduwa domin bata san ina suka nufa ba, kuma irin yadda fuskarsa ta dauki ja alamun ransa a bace ko menene sai ta sake tsorata ainun har suka shiga lft suka sake hawa sama cen wajen office dinsa
Ko da lft din ya tsaya hannun nata ya cika ya yi gaba yana kunce abinda ke daure a jikin rigarsa na wuyansa dan ji yake yi tamkar zai tsaida masa numfashinsa ya dadana code din kofar office dinsa ya shige lokaci daya ya dauki commande din camarar bangarensu ya sakata a halin duhu sannan ya kurawa kofar ido yana jiran shigowar ta
KHAUSAR da ta gama summa a tsaye da kyar ta cira kafarta ta karasa office din
Rana shigowa ta ajiye farar rigar aikin domin itama du a rikice cire rigar ta yi ta tunkaro kusa da table din da yake tsaye kanta tsaye tana dubansa idannuwanta na cikowa da kwallah ta ce" Kana tunanin laifina ne?, TAUFEEK kana tunanin nice na saka su Aba aikata aikin nan?, Walahi walahi ban sani ba, nima na san ai na wani hadi, in kana tune ka min alkawarin kasancewa da Ni har a Daura aurena da .........."
"Khausar Please cn U be quiet?!" TAUFEEK ya fada a kasashen da ya saka Khausar zuba masa ido tana jin tamkar zata kifa a tsayen da take , shin yaya zata kwatanta masa cewar ba fa ita tace a daura mata aure da shi ba?
A nutse yana binta da kallo ya ce" sai yaushe zaki fara jin maganana ne? Menene wannan shigar? Ina hijab dinki? Me yasa kike son daukan dabi'ar da zata ringa bata min rai? Babu ruwanki a gaban kowa sai ki arta a guje ? Kina kallo muna tare da docter kika wani fita da gudu menene haka ne?"
Da mamaki take kallonsa, sai kuma ta kalli jikinta
A hankali ta shiga juyawa a gaban nasa har sai da ta juyo tana fuskantarsa a sanyaye ta ce" Menene laifin shigata? Me yasa kake son min fadan shigata ne bayan na san cewa harda ita a tsaikon samun mijina yanzu na kare da ......"
Ta yi shiru sakamakon zuba mata jajayen idannuwansa da ya yi yana sauraronta
Gannin ta yi shiru a hankali ya ce" Kika kare da me?"
Khausar ta dafe gaban goshinta, a hankali ta ja kujera ta zauna sannan ta mika hannunta ta kama bayan hannunsa dake jimke saman table din a tausashe dayan hannun nata kuwa ta bude abinda ke ajiye ta ciro tisu fari ta nufi gaban goshinta da shi a hankali tana share zufar da ta karyo mata kasa kasa ta ce" Dan Allah ka zauna, ka san ba son rikici nake ba, kuma baka san abinda ya faru ba ga dukkan alamu, ka zauna dan ina tsoron in na fada maka yanzu ka fadi, Taufeek its vry srius , ka zauna Please"
Hannunsa ya janye daga jikin nata, domin tunda ta dora din tana magana ne tana dan shafa bayan hannun nasa da sigar rarashi ba da wata manufa ba, wace sshi kuwa hakan ba daidai da yannayin da yake iya dauka bane
Da ƙafarsa ya dan tura kujerar baya ya zauna yana kallonta , a hankalin da sam bata so yana mata magana ya ce" Kika kare da me? Tl me"
"Na kare da auren aminina, abokina, freind dina, TAUFEEK basu fada maka aurena da aka daura da kai bane ko menene na ga ba maganar kake min yanzu ba?, TAUFEEK ka san cewa wai ashe Ni aka aura maka.....?" Ta fada tana watsa hannayenta hadi da dan zarro idannuwanta alamun ta fada masa tashin hankalin nan
Bakinsa ya dan tabe yana kauda dubansa ya ce" Eh haka na ji"
Khausar ta girgiza kai ta ce" Ka ji? Kennan ka ji? Ya Allah, da ka san irin yadda na yi ɓaci a kwana biyun nan da ka sha mamaki, TAUFEEK aminina?"
TAUFEEK ya zuba mata ido, ya dora hannayensa duka biyu yana dubanta ya ce" Eh, sai aka yi yaya?"
"ka kuwa ji me nace ne?" Khausar ta fada tana dubansa
TAUFEEK ya dan dantse lebensa da dan jin yana daf da kowa a wannan dogon maganar da tarin raini ke jagoranta tsakaninsa da Khausar ya ce" Eh na ji me kika ce, an daura maki aure da Ni, Ni amininki, nace eh sai mene kuma?"
Baki da ido da hanci ta bude tana kallonsa har ya mike ya nufi wajen frij din office din nasa ya ciro faro ya bude ya sha ya ajiye sauran cikin abin zuba shara dan bai shanye ba wanda ya rage din kuma kadan ne
Ya karasa ya dauki suturarsa kala blu mai haske wando da riga irin na likitoci wa'inda yake shiga dakin tiyata da su ya bale boturan rigar jikinsa ya cire rigar
A zabure Khausar ta mike tana kawar da kanta, sai kuma ta koma ta zauna ta sada kan nata tana dadana yatsunta tana addu'a kunnayenta na jiyo mata motsinsa alamun harta wandon a nan TAUFEEK ya saka har ta daina ji idannuwanta a rintse zufa na neman karyo mata sai kuma ta ji maganarsa daf da ita , a kamilance harufan bakinsa ke fitowa yana dubanta ya ce" igiyoyin aurena uku ke wuyanki, ina fatan zaki kula ba tare da kin takura min tabatuwarsu a kanki ba!, Ki kula na kasance mai jinkiri sosai, inada hakuri sosai, ama a kanki babu abinda bai sameni ba......Please Khausar ki dan sanyaya mana tafiyar , ko ba komai kin ce auren hadi ne, shi kuma ai sai an zauna shi ko? Kin dai san Ni ba marar kunyar da zan cewa su Aba wai yanzu yanzu zan bijire masu bane, in ke wuyanki ya rika ki je ki fada masu kawai sai a duba a ga abinda ya dace a yi......., Khausar My wife.........
A dan zabure ta dago ta zuba masa ido
TAUFEEK ya dan dantse lebensa kadan ya ce" my wife bata da lafiya, kin san ciki ne da ita, kuma ina tsoron laifinki ne....... ki dan yi zamanki a nan har a tashi kin ji?"
Yana gama fada ya saka hular a kansa ya dauki glasss dinsa ya mayar ya ajiye mata iphone dinsa a gabanta sannan ya wuce a office din, du a kokarinsa kar a fahimci irin takaicin da ta shaka masa, da kuma tunanin mema take nufi ne yarinyar nan da shi har ya karasa dakin tiyatar da ake daf da yiwa marar lafiyan allurar kashe jiki gaba daya a saka shi a duniyar barci dan aiki ne zasu masa su ciro masa ciwon kansar dake kansa