Sashe 31
Da Ciwo A Zuciyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali ta dan girgiza kanta, tana da niyar fadin laifin ya tsatsareta da ido , a tausashe yana dubanta ya ce" Yumnah, kina zargina ne?"
Da sauri ta zuba masa ido, ta ce" Zargi kuma?"
Idannuwansa ya lumshe matsayin amsa
Da sauri ta girgiza kanta ta ce" Ba, bana zarginka, kawai dai ni abotakarku ce nake gannin bai dace ba, ba abota tsakanin mace da namiji, sam bana son tarayarku da ita, daga min hankali take yi, sai in ga ka fi sonta da ni, bayan nice matarka, sai in ga ka fi darajata a kaina"
Da mamaki yake kallon fuskarta, wannan din itace hujarta kawai?, Eh lalle a jiya Abansa ke cewa wani sain fa magidanci zaka iya tsintar kanka da rarashi a kan abinda bakama aikata ba, ka yi rarashin dan nima shi nake yi nan da ka gani, ita mace tana iya yin fushi a kan abinda baka taba zato ko tsamani ba, in ka ga hankalinta tashe yi kokari ku sasanta dan sasantawar itace zaman lafiyarka a gidanka
"Yumnah, wannan shine dalilinki?" Ya fada yana s9n sake gaskatawa
Kai ta gyafa har tana sauke ajiyar zuciya
Gefe ya kalla kadan yana ta tunanin to kennan ya shigo fagen da nanata zancen da ya san an sani zai zame masa wajibi? Ikon Allah
A tausashensa ya rike hannayenta yana kallonta ya ce" Wannan din, bai dace ya zama abinda zai saka ki bude baki ki yi furuci kamar wace ke zargina da KHausar ba, hakan ba daidai bane sam ba kuma wayo bane, KHausar na santa tun kafin na sanki, a yadda kika ganmu da akoy maganar so da na aureta tun kafin na aureki, ita din tamkar jinnin jikina ce, ina nufin kamar kanaina haka nake dubanta, mu'amalata da ita tsarkakakiya ce, zumuncina da ita mai daraja ne, ina kare mutuncinta dan mai mutunci ce, daga wannan kar ki dada kar ki rage Yumnah, bayan wannan babu wani abu mai iya gigita tunani ko ya saka shaku, na yarda cewa al'adunmu sunna da nasu tafiyar a rashin gannin ire iren haka, hausawa muke, haka adininmu, ama ki yarda tsakanina da KHausar zumunci ne, haka kuma zan iya kare hakinka a gaban kowa...."
Ya dan sasaura , a hankali ya dora da fadin" Ke iyalina ce, maganar sonki ko gannin darajarki kin san ya kai matsayin da na aminta har na saka ki dakina......., Ba zan so mu fara takalar magana irin haka ba, zan kuma so li yi zumunci da Khausar idan har kina ra'ayi, in bakya yi ba zan takuraki ba, ama kar ki wulakantata dan ita din a kulun mutuntaki take yi kin fahimta?"
Ba ainahin fahimtar ta yi ba, ama a yadda yake zaunen nan ya bata dukkan hankalinsa zata iya cewa rigimar ta lafa a irin wannan lokacin
A hankali ta koma jikinsa ta sake makalkale shi hannayenta duka a jikinsa
Idannuwansa ya dan lumshe, karfe bakwai ne duka duka na safe, yana fa niyar fitama, haka kuma wannan yannayi yana tsikararsa sosai
Kasa kasa ya rada mata maganar da ta sakata dan sake shigewa jikinsa tana sakin murmushi
Murmushi ya yi ya sake fadin" ba zaki lafawa tuzurancina bane? Kar fa ki takali dodo ki nemi kumna fitila Yumnah"
A ranta fatanta dodon nan ko mai cin dodo ne irinta ta takale shi, burinta itama ta zama matar aure a yau din nan, dan haka cikin dabara, da koyarwar da ta samu ta ringa dan shafa hannunsa zuwa wuyansa kamar da gangan take yi, bayan tana sane sarai, gashi ta idasa cimuymuye rigarsa da Hajia kakarsa ta bashi ta sallah, ta idasa rike shi iya rikewa
Tun yana sake tunawa cewar ba yanzu ba, sai da ya tsinci kansa tsamo tsamo a aiki irin na musulmai, aikin da ya zamto gagarumi a gareshi shi kansa, aikin da bai taba kwatanta aikatawa da wata y'a mace a kaf fadin rayuwarsa ba, aikin da yake wuni yana kwana da shi wanda yake tunanin idan ya tashi yi ta yiwu ya karya y'ar mutane, da safiyar gari, da yinwa a cikin y'ar mutane, da komai, haka ya riketa riko na firgici da mamaki, tun tana iya gane sarafa junna suke har ta cenza tunani ta fara tunanin sarafa ake yi, harma ta dawo tunanin ko ranta ake nema?
A hankali ta fara bambance aya da tsakuwa, a hankali ta nemi dna juyo da hankalinsa ko zai dakata tun kafin ya fara mai gaba dayan
Sai dai sani ne bata yi ba, ba sabon shiga ake yiwa fi'ili ba, ba kuma namiji mai sunna namiji ake tsokana a mike ras kamar yadda aka koyar da ita ba
Bata taba tunanin Mijinta ya fi ainahin mijinta girma ba sai da tashin hankalin ya nauje ta ya cakumeta ya nemi karta
Wahala iya wahala ta tsinci kanta a ciki a lokacin da summa ta ki zuwar mata take farke tana sauraron aikin likita
Jigatar shima ya jigata dan yau ya fara sauke nauyin nan kuma a irin lokacin nan da ya dan warci furana wajen hajia cikinsa ya dan dauka kadan
Da wannan suka sasaba har Amarya Yumnah ta samu abinda take nema, sai dai wa ya sani tana kan bakanta na mikewa ta kabe ta kile ?......... (😂 han)
_______________________________
Karfe bakwai na safe ta shirya , shiryawa mai tsafta da tsari daidai da kwaliyarta
Hijab dinta na sallah sabo fil fari kal ta saka sannan ta saka takalmin auren TAUFEEK ta aniya kai kawo sai sakin murmushi take yi
Zazafe da aka zubo ta karewa kallo ta cire kai tana murza dari biyar din da Aba ya wanka mata mari da ita da asubahin Allah, ita ta san yau zata shiga cikin tarihin rayuwarta domin zata ci kwan kifi iya ci a kofar asibiti sannan ta ci dambun nan na kofar asibiti mai dadin balaki, ita kam yau me zai hadata da zazafen Mama? Aa gaskiya, to mema ya hada likitama da zazafe fisabililahi?
Sintirin da take yi yan uwan ke bi da kallo har Mama ta fito daga gyaran dakin abansu domin ita ke gyaran abinta har yanzun bata barwa yayanta wannan ba, ta mikawa Khausar sharar ta kai ta zubar ta dawo ta yi wani kikam ta ki zama sam sai aukin duba agogon da ta daura a hannunta take yi baka yar siririya tun ta sallarsu ta bara da Aba ya siya masu
Mama dake zama saman tabarma ta janyo kwanon abincinta ta sake kallon KHausar ta ce" Ke wai ya hala, ki nemi waje ki zauna mana, ya baki karya ba kuma?"
Khausar ta kalli abincin ta girgiza kai a hankali ta ce" Mama ai yau ba zan ci tuwon laushi ba, kin ga dari biyar Aba ya bani, kuma shiry TAUFEEK din bai zo ba har yanzu kar fa na yi lati, Aisha ke dan bani wayarki na yi kiransa?"
Mama da mamaki take kallonta ta ce" Ke zo nan zauna"
Khausar ta karaso inda Mama ta nuna mata ta zauna tana kallon maman gannin ta sha kunu
Mama ta ce" Dari biyar din duka zaki je ki juyewa ciki sai kace baiwar ciki? Bayan ga abinci a gida? Karma mu fara haka da ke maza ki cire dari biyi ki saka a cikin asusunki, sannan maganar TAUFEEK, Khausar zuwa yanzu fa sai kin kiyaye wasu abubuwan, kamar su yawan kiranshi, kiranshi kowani lokaci, ke harta yawan ganninki tare da shi, dan kin ga yanzun sunnansa mai mace, ba daya bane da da, ita zuciya bata da kashi matarsa na iya jin ba dadi, kuma tana da gaskiya dan ko ba komai hausawa muke ai ba yaren yahudu ba, ke kin san yaya aka yi muka yarda da tarenku sai da muka yarda cewa eh ta zumunci ce, ama duda haka ba wani sakankancewa muka yi da ku ba, dan haka ba zamu yarda yanzu tarenku ya hadasa fitina da matarsa kin gane?"
Khausar kallon Mama take yi da mamaki
Ta rage kiran TAUFEEK? Ta rage karfin mu'amalarsu dan ya yi aure? To ita me hadinta da aurensa? Ita ai itacema zata gyara aurensa ba ta hada rikici ba, ama irin yadda Mama ta daure fuska a dole ta amsa da to ta kuma kai dari biyu ta saka a asusu sai cika kunci take ta zo ta zauna ta shiga shakar zazafe bayan ita ta san cewa ba girman likitoci bane daukan tuwo da safiyar gari ( ki rufawa kanki asiri autar Aba, ki ci ki yi nak, aikin asibiti ba'a yi da yinwa bale din nan kar ki je ki baje kina hailala😌)
Wasa wasa sai da ta ba karfe goma sha daya baya na rana tana jiran tsamani, ta ki ko hijab din ta cire a zaunen da take, dan shi yace za'a kaita kar ta je kai tsaye, gashi Mama ta yada dokar kar ta saki ta ringa kiransa yanzun, sai kawai ta ji kamar ta yi ta ihu a zaune
Sai kusan sha biyu aka yi salama aka sanar da ita direba ne daga gidan mai kwanoni ta fito a kaita asibiti
Har gudu gudu take yi wajen saka takalma Mama na yi mata addu'a har ta shige motar tana tambayar ko TAUFEEK ya yi tafia ne? Shi dai direban bai san amsar bata ba ya dai kaita har inda akace ya kaita sannan ya juya
A darare take kale kale a baban filin bangaren Emergency, bata san inda zata nufa ba, bata taba tunanin zata iya tsintar kanta da tsoro da shayi ba sai a yau, kallon mutanen dake kai kawo yake yi zuciyarta cike da tunanin me ya hannata dauko wayarta ne? Tunda suka yi waya da Elhaji jiya ta kashe wayar bata kunnata ba dan yace shi zai kawota asibitin yau, ita kuma bata son takura
Ajiyar zuciya ta sauke ta nufi hanyar shiga emgncy din
Mutumen dake gadin wajen yana tsaye kikam fuskar nan ba annuri ne ya sakata dakatawa tana kallonsa da tunanin anyama bahaushe ne?
So ta yi ta rabe ta shige salim alim, ama kuma ta san waye shi, dan ko kana zuwa dubiya ka san su waye masu tsaron kofofin asibitin, basa sasauci dan bada tsaro a hanyar
Murya na rawa ta ce" Ina yini Baba"
Da sauri ta zuba masa ido, ta ce" Zargi kuma?"
Idannuwansa ya lumshe matsayin amsa
Da sauri ta girgiza kanta ta ce" Ba, bana zarginka, kawai dai ni abotakarku ce nake gannin bai dace ba, ba abota tsakanin mace da namiji, sam bana son tarayarku da ita, daga min hankali take yi, sai in ga ka fi sonta da ni, bayan nice matarka, sai in ga ka fi darajata a kaina"
Da mamaki yake kallon fuskarta, wannan din itace hujarta kawai?, Eh lalle a jiya Abansa ke cewa wani sain fa magidanci zaka iya tsintar kanka da rarashi a kan abinda bakama aikata ba, ka yi rarashin dan nima shi nake yi nan da ka gani, ita mace tana iya yin fushi a kan abinda baka taba zato ko tsamani ba, in ka ga hankalinta tashe yi kokari ku sasanta dan sasantawar itace zaman lafiyarka a gidanka
"Yumnah, wannan shine dalilinki?" Ya fada yana s9n sake gaskatawa
Kai ta gyafa har tana sauke ajiyar zuciya
Gefe ya kalla kadan yana ta tunanin to kennan ya shigo fagen da nanata zancen da ya san an sani zai zame masa wajibi? Ikon Allah
A tausashensa ya rike hannayenta yana kallonta ya ce" Wannan din, bai dace ya zama abinda zai saka ki bude baki ki yi furuci kamar wace ke zargina da KHausar ba, hakan ba daidai bane sam ba kuma wayo bane, KHausar na santa tun kafin na sanki, a yadda kika ganmu da akoy maganar so da na aureta tun kafin na aureki, ita din tamkar jinnin jikina ce, ina nufin kamar kanaina haka nake dubanta, mu'amalata da ita tsarkakakiya ce, zumuncina da ita mai daraja ne, ina kare mutuncinta dan mai mutunci ce, daga wannan kar ki dada kar ki rage Yumnah, bayan wannan babu wani abu mai iya gigita tunani ko ya saka shaku, na yarda cewa al'adunmu sunna da nasu tafiyar a rashin gannin ire iren haka, hausawa muke, haka adininmu, ama ki yarda tsakanina da KHausar zumunci ne, haka kuma zan iya kare hakinka a gaban kowa...."
Ya dan sasaura , a hankali ya dora da fadin" Ke iyalina ce, maganar sonki ko gannin darajarki kin san ya kai matsayin da na aminta har na saka ki dakina......., Ba zan so mu fara takalar magana irin haka ba, zan kuma so li yi zumunci da Khausar idan har kina ra'ayi, in bakya yi ba zan takuraki ba, ama kar ki wulakantata dan ita din a kulun mutuntaki take yi kin fahimta?"
Ba ainahin fahimtar ta yi ba, ama a yadda yake zaunen nan ya bata dukkan hankalinsa zata iya cewa rigimar ta lafa a irin wannan lokacin
A hankali ta koma jikinsa ta sake makalkale shi hannayenta duka a jikinsa
Idannuwansa ya dan lumshe, karfe bakwai ne duka duka na safe, yana fa niyar fitama, haka kuma wannan yannayi yana tsikararsa sosai
Kasa kasa ya rada mata maganar da ta sakata dan sake shigewa jikinsa tana sakin murmushi
Murmushi ya yi ya sake fadin" ba zaki lafawa tuzurancina bane? Kar fa ki takali dodo ki nemi kumna fitila Yumnah"
A ranta fatanta dodon nan ko mai cin dodo ne irinta ta takale shi, burinta itama ta zama matar aure a yau din nan, dan haka cikin dabara, da koyarwar da ta samu ta ringa dan shafa hannunsa zuwa wuyansa kamar da gangan take yi, bayan tana sane sarai, gashi ta idasa cimuymuye rigarsa da Hajia kakarsa ta bashi ta sallah, ta idasa rike shi iya rikewa
Tun yana sake tunawa cewar ba yanzu ba, sai da ya tsinci kansa tsamo tsamo a aiki irin na musulmai, aikin da ya zamto gagarumi a gareshi shi kansa, aikin da bai taba kwatanta aikatawa da wata y'a mace a kaf fadin rayuwarsa ba, aikin da yake wuni yana kwana da shi wanda yake tunanin idan ya tashi yi ta yiwu ya karya y'ar mutane, da safiyar gari, da yinwa a cikin y'ar mutane, da komai, haka ya riketa riko na firgici da mamaki, tun tana iya gane sarafa junna suke har ta cenza tunani ta fara tunanin sarafa ake yi, harma ta dawo tunanin ko ranta ake nema?
A hankali ta fara bambance aya da tsakuwa, a hankali ta nemi dna juyo da hankalinsa ko zai dakata tun kafin ya fara mai gaba dayan
Sai dai sani ne bata yi ba, ba sabon shiga ake yiwa fi'ili ba, ba kuma namiji mai sunna namiji ake tsokana a mike ras kamar yadda aka koyar da ita ba
Bata taba tunanin Mijinta ya fi ainahin mijinta girma ba sai da tashin hankalin ya nauje ta ya cakumeta ya nemi karta
Wahala iya wahala ta tsinci kanta a ciki a lokacin da summa ta ki zuwar mata take farke tana sauraron aikin likita
Jigatar shima ya jigata dan yau ya fara sauke nauyin nan kuma a irin lokacin nan da ya dan warci furana wajen hajia cikinsa ya dan dauka kadan
Da wannan suka sasaba har Amarya Yumnah ta samu abinda take nema, sai dai wa ya sani tana kan bakanta na mikewa ta kabe ta kile ?......... (😂 han)
_______________________________
Karfe bakwai na safe ta shirya , shiryawa mai tsafta da tsari daidai da kwaliyarta
Hijab dinta na sallah sabo fil fari kal ta saka sannan ta saka takalmin auren TAUFEEK ta aniya kai kawo sai sakin murmushi take yi
Zazafe da aka zubo ta karewa kallo ta cire kai tana murza dari biyar din da Aba ya wanka mata mari da ita da asubahin Allah, ita ta san yau zata shiga cikin tarihin rayuwarta domin zata ci kwan kifi iya ci a kofar asibiti sannan ta ci dambun nan na kofar asibiti mai dadin balaki, ita kam yau me zai hadata da zazafen Mama? Aa gaskiya, to mema ya hada likitama da zazafe fisabililahi?
Sintirin da take yi yan uwan ke bi da kallo har Mama ta fito daga gyaran dakin abansu domin ita ke gyaran abinta har yanzun bata barwa yayanta wannan ba, ta mikawa Khausar sharar ta kai ta zubar ta dawo ta yi wani kikam ta ki zama sam sai aukin duba agogon da ta daura a hannunta take yi baka yar siririya tun ta sallarsu ta bara da Aba ya siya masu
Mama dake zama saman tabarma ta janyo kwanon abincinta ta sake kallon KHausar ta ce" Ke wai ya hala, ki nemi waje ki zauna mana, ya baki karya ba kuma?"
Khausar ta kalli abincin ta girgiza kai a hankali ta ce" Mama ai yau ba zan ci tuwon laushi ba, kin ga dari biyar Aba ya bani, kuma shiry TAUFEEK din bai zo ba har yanzu kar fa na yi lati, Aisha ke dan bani wayarki na yi kiransa?"
Mama da mamaki take kallonta ta ce" Ke zo nan zauna"
Khausar ta karaso inda Mama ta nuna mata ta zauna tana kallon maman gannin ta sha kunu
Mama ta ce" Dari biyar din duka zaki je ki juyewa ciki sai kace baiwar ciki? Bayan ga abinci a gida? Karma mu fara haka da ke maza ki cire dari biyi ki saka a cikin asusunki, sannan maganar TAUFEEK, Khausar zuwa yanzu fa sai kin kiyaye wasu abubuwan, kamar su yawan kiranshi, kiranshi kowani lokaci, ke harta yawan ganninki tare da shi, dan kin ga yanzun sunnansa mai mace, ba daya bane da da, ita zuciya bata da kashi matarsa na iya jin ba dadi, kuma tana da gaskiya dan ko ba komai hausawa muke ai ba yaren yahudu ba, ke kin san yaya aka yi muka yarda da tarenku sai da muka yarda cewa eh ta zumunci ce, ama duda haka ba wani sakankancewa muka yi da ku ba, dan haka ba zamu yarda yanzu tarenku ya hadasa fitina da matarsa kin gane?"
Khausar kallon Mama take yi da mamaki
Ta rage kiran TAUFEEK? Ta rage karfin mu'amalarsu dan ya yi aure? To ita me hadinta da aurensa? Ita ai itacema zata gyara aurensa ba ta hada rikici ba, ama irin yadda Mama ta daure fuska a dole ta amsa da to ta kuma kai dari biyu ta saka a asusu sai cika kunci take ta zo ta zauna ta shiga shakar zazafe bayan ita ta san cewa ba girman likitoci bane daukan tuwo da safiyar gari ( ki rufawa kanki asiri autar Aba, ki ci ki yi nak, aikin asibiti ba'a yi da yinwa bale din nan kar ki je ki baje kina hailala😌)
Wasa wasa sai da ta ba karfe goma sha daya baya na rana tana jiran tsamani, ta ki ko hijab din ta cire a zaunen da take, dan shi yace za'a kaita kar ta je kai tsaye, gashi Mama ta yada dokar kar ta saki ta ringa kiransa yanzun, sai kawai ta ji kamar ta yi ta ihu a zaune
Sai kusan sha biyu aka yi salama aka sanar da ita direba ne daga gidan mai kwanoni ta fito a kaita asibiti
Har gudu gudu take yi wajen saka takalma Mama na yi mata addu'a har ta shige motar tana tambayar ko TAUFEEK ya yi tafia ne? Shi dai direban bai san amsar bata ba ya dai kaita har inda akace ya kaita sannan ya juya
A darare take kale kale a baban filin bangaren Emergency, bata san inda zata nufa ba, bata taba tunanin zata iya tsintar kanta da tsoro da shayi ba sai a yau, kallon mutanen dake kai kawo yake yi zuciyarta cike da tunanin me ya hannata dauko wayarta ne? Tunda suka yi waya da Elhaji jiya ta kashe wayar bata kunnata ba dan yace shi zai kawota asibitin yau, ita kuma bata son takura
Ajiyar zuciya ta sauke ta nufi hanyar shiga emgncy din
Mutumen dake gadin wajen yana tsaye kikam fuskar nan ba annuri ne ya sakata dakatawa tana kallonsa da tunanin anyama bahaushe ne?
So ta yi ta rabe ta shige salim alim, ama kuma ta san waye shi, dan ko kana zuwa dubiya ka san su waye masu tsaron kofofin asibitin, basa sasauci dan bada tsaro a hanyar
Murya na rawa ta ce" Ina yini Baba"