Sashe 52
Da Ciwo A Zuciyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A dole abin ya mata ciwo mai zafin gaske
A dole abin nan ya taba mata zuciya
Bata san me zata ce ba, yaya zata yi, tana matukar jin ciwo mai girma a zuciyarta na irin yadda mu'alamarsu zata ruguje tana ji tana gani
Sai dai rugujewar shine alkhairi dan bata ga kuma me zasu iya cewa junna a yanzu ba, ya fi karfinta ya fi karfin ajinta shi din ba abokin yinta bane, ta kowani fani idan ta duba a yanzu sai ta ga idan har ta yarda ta sakawa ranta ci gaba da shi din kamar ta cuci kanta da kanta ne
A hankali ta dafe kanta hawaye take yi sosai sannan ta dafe gaban kirjinta a sanyaye ta ce" Ama da wa zan yi fira? Wa zan SANARWA damuwata?, Wa zai rarasheni? Waye zai min fada? Wanene zai ringa sakani ko hannani bayan su Mama?, Me yasa ka saka na sakankance da kai haka? Me yasa ka shiga jikina haka?, TAUFEEK baka min adalci ba, baka min adalci ba TAUFEEK, shin yaya zan ci gaba da walwala ba farin cikinka a tare da Ni? Ya Allah ka bani mafita mai sauki a cikin lamarina.........."
Surutu take yi irin na zafi da ciwo a cen kasan zuciyarta....... Ta shagala sosai yar karamar wayarta ta shiga kuka a cikin aljihun rigarta
Da sauri ta lalubo tana tunanin ko dan sahunta ne da ya ga shiru bata tabo shi ba har yanzu?
Numbar ta zubawa ido tana kallo, domin bakuwar lamba ce a wayar Tata
A hankali ta daga tana dan gyara muryarta hadi da yin salama sannan ta yi shiru
"Amincin Allah ya tabata a gareki kema Likitana....."
Shiru ta yi, jin Muryar namiji ne, da kuma abinda aka fada din
A hankali ta dan budi bakinta ta ce" Ban gane mai maganar ba?"
Dan murmushi ya yi shima ya ce" Allah sarki dama nace akoy sanyin murya matata to be in sha Allah, jiya na turo kanwata Salma ta amsar min numbar dan na yi na yi na tareki na amsa na kula da wahala fa ki saurareni a hanya, karma aje ki ce min bakya so na na suma dan firgici"
A hankali Khausar ke dan sauke numfashinta, lokaci daya ta afka wata sabuwar duniya ta tunani da tarin mamaki
Yayan Salma?, To wane? Salma dai Salma? Kai, anya kuwa? Har yake kiranta da matarsa? Ko dai ya yi batan numba ne?, Da wahala in ba batan numba ya yi ba, ya rab.........,
Sai dai du rikicewar ta wannan karron sai ta ki kashe kiran haka kuma ta kasa yin wata magana da zai iya jin ba dadi
Ko ba komai tana kan gaba ne ta nema irin wannan
A hankali ta dan sauke numfashi jin yana ta afkin fadin ta amsa shi plz
A sanyaye sosai ta dan ja numfashi ta ce" Zan je gida ne na ga dan sahuna na kira"
Shima a sanyayen ya ce" Ba damuwa, sai kin zo, plz ki kular min da kanki, sannan zan yi kira idan kin huta dan ina so ki amsheni, ki dubeni ki bani dama kin ji kanwata????"
Murmushi ta samu kanta da saki a hankali ta furta" Na gode"
Sannan ta kashe kiran tana dan samun kanta da sake sakin murmushi
Yayan Salma? Yayunta maza biyu ta sani.....shin wanene a cikinsu?................haka kawai ta tsinci zuciyarta da jin nutsuwa da farin ciki harma ta wanke fuskarta ta fito ta cire rigarta ta nade ta saka a jaka sannan ta dauki kayanta da mayafin nan nata ta kade ta dora a kafadarta tana turo baki cike da jin haushin furucinsa wai wani bata yi kyau ba, kar ta yin, karma ta yin! Ai dama ba cewa ta yi ita mai kyau bace, kwaliya ne yace itama ta aura irin na yan mata!...........
Haka ta yi ta fadanta a zuciyarta har ta samu ta fada adaidaitar, domin ba wani a sake take ba da mayafin nan, kawai rikici ne rigima ce, kuma tunda ta yafa shi mamama da mamaki tace a haka zata tafi ne? Tace eh, mama ta ce da ta bude shi ta dan yafa jikinta duka sai tace ai ba komai , ita dai Mama kallonta ta yi tana jira ta ga da gaske? Sai kuwa ta ga da gasken ta tafi da yafen, jirantama tane yi a gidan ta dawo su zauna dan ba dabiar kirki bane hakan sam
Rai bace Taufeek ya dawo gida, domin kowa bai je nema ba dan a sama sama yake ba zai iya jure wani neman fitinan ba, direct bangarensa ya nufa yana mai kokarin kawar da dukkan wani bacin rai dake taso masa ko dan kar ya shiga hakkin abokiyar zamansa, domin ba ita ta hasala shi ba idan ya sauke mata fushinsa bai yi mata adalci ba
Sai da ya yi wanka ya sauko sakamakon irin yadda ta yi ta kai kawo cewar abincinsa na jiransa
Zama ya yi saman cafet a hankali ya mika hannu ya kashe tv dake yi, domin baya son hayaniya ne sam, kansa na dan masa ciwo, gaba daya ransa a dagule yake, sai dai abu daya da ya sani shine ba damuwa ya kyaleta, zumunci ne tunda ta katse babu yadda zai yi, ba zai saka mata wuka a wuyanta ba kan dole sai ta yi zumunci da shi tunda bata ra'ayi, yaya zata kasa yi masa uzuri a kan abinda yake aiki ne nasa? Idan ta ji cewa Yumnahma bata san komai game da aikinsa ba a matsayin dan kasuwa kuma matashin dan makaranta ta san shi ta ce me kennan? Ya dace ta masa uzuri, yaya take tunanin zai fito ya ringa yayata mata maganar sirrin aikin da yake da girma da daraja irin ta taimakon rayuwar dan adam?, Itama da gangan ta kasa gane cewa ya jima da samun takarda irin tata take tafe a makance, da gangan ta ki fahimta dan kawai ta daga masa hankali, kuma ta taki Sa'a ta daga masan domin ta fado a daidai lokacin da ta riga ta gama zamtowa tamkar jinnin jikinsa, yar uwarsa ta jinni, ama kuma ba komai dan uwankama yana iya kinka ka rayu kuwa !
Abincin ya ba hankalinsa bayan ya budi baki da kula ya ce da ita" Thank you" sannan ya yi bismillah ya dan fara tsakura
Ya koro da tabawar ya ji du ya koshi, a dole ya mayar gefe ya dan dauki jus din kwalba da ta zuba zai kai bakinsa yace" kin je kin wuni a bangaren na Hajia?"
Sai da gabanta ya fadi jin tambayar da ya yi mata, sai dai ta Basar cikin kisarta ta ce" na je , eh na je"
Yannayin da ta dan sosa gaban goshi ya bi da kallo , kasa kasa ya ce" ina nufin kin wuni a cen din ne?"
"Aa ban wuni ba, ama a kalla na kai minti ashirin......." Ta fada cike da tabbatarwa kanta ai ba zai yi fushi ba tunda ta je din
Jus din ya ajiye yana binta da kallon mamaki
A tsanake ya ce" kina so ki ce min umarnin da na baki ki je ki wuni da Hajia baki cika ba?"
Da sauri ta dago dan jin yannayin amon muryarsa ya cenza daga laushi laushi zuwa yannayi mai zafi zafi
Rai bace ya dan sake dubanta ido cikin ido ya ce" Wannan din ya zamto na farko kuma na karshe, da zaki take umarnina, idan nace kaza za'a yi shi za'a yi! Sannan ki kula ki kiyaye mutuncin dangina ta haka ne zan iya mutunta naki, Hajia kakata ce, ki kula, ki bata girman da take da shi idan ba haka ba bana tunanin in har zamu iya fahimtar junna!"
Daga haka ya mike ya bara mata jus din gaba dayama ya fice a falon
Hankalinta sosai ya nemi barin jikinta, lokaci daya jikinta ya dauki rawa ta rasa yaya zata yi, ya fi a irga tana gwada bin bayansa tana komawa dan ta ga ya nufi bangaren Hajia, karshe dai nan ta zauna ta zuba uban tagumi tana gadin dawowarsa dan ta bashi hakuri, in dai wajen hajia ne zata je zata je ta labe har yama ta yi ta dawo dan ba zata iya zama su shaki iska daya da hajiar nan ta kasheta a banza a wofi ba
Tunda ya shigo bangaren Hajia ya nemi waje ya zauna ya hade gabas da yama bai ce da ita ufan ba har ta zo da kaskon turare turaranta ta ce" Gaba daya ka fara aiki irin na wa'inda basu cika jin tsoron Allah ba magidanci, yanzu yau kwana biyu fa ban maka turare ba, Ni kuma ba zan ba wancen muciya da zanin kayan tsarinka ta je ta cenza da yan barbade barbade na matan zamani a malake min jika a sakani uku, gyara zamanka dan dage rigar nan na shafa maka a bayan cikinka wannan akace sunnansa kaikayi koma kan mashekiya, du wanda ya nufeka da asiri in sha Allahu zai kome masa ne, gyara da kyau mana wai meye kake cika kunci uwa balan balan"
Karra hade fuska ya yi ya ce" Kar ki saki ki turara min kaurin nan ke kuma!"
Hajia ta yi turus tana kallonsa, kasa kasa ta ce" Magidanci maganin tsarin ne ya zama kauri kuma?"
Cire kai ya yi bai bata amsa ba, hakan ya sa ta ajiye tana kallonsa ta ce" Kai ko wancen mai kai uwa na ifirutun ce ta bata maka? Ka dan yar nan dan rashin da'a da ta zo gaisheni kafada da kafada muka gaisa? Yar nan ka kuwa san in ta je cen bata zuwa bangaren Mamanka sai dai na kishiyoyi? Ka fa ja mata kunne dan Ni nan ko mai kwanoni ya yi kadan bale matar dansa, aikin banza aikin wofi "
"Ki matsa min da warin abin nan nace, kuma ki daina sako ubana a abinki kin dai ji na fada maki, da kike cewa wai tsoron Allah in tambayekima hijab umarnin Allah ne ko na mutun?"
A dole abin nan ya taba mata zuciya
Bata san me zata ce ba, yaya zata yi, tana matukar jin ciwo mai girma a zuciyarta na irin yadda mu'alamarsu zata ruguje tana ji tana gani
Sai dai rugujewar shine alkhairi dan bata ga kuma me zasu iya cewa junna a yanzu ba, ya fi karfinta ya fi karfin ajinta shi din ba abokin yinta bane, ta kowani fani idan ta duba a yanzu sai ta ga idan har ta yarda ta sakawa ranta ci gaba da shi din kamar ta cuci kanta da kanta ne
A hankali ta dafe kanta hawaye take yi sosai sannan ta dafe gaban kirjinta a sanyaye ta ce" Ama da wa zan yi fira? Wa zan SANARWA damuwata?, Wa zai rarasheni? Waye zai min fada? Wanene zai ringa sakani ko hannani bayan su Mama?, Me yasa ka saka na sakankance da kai haka? Me yasa ka shiga jikina haka?, TAUFEEK baka min adalci ba, baka min adalci ba TAUFEEK, shin yaya zan ci gaba da walwala ba farin cikinka a tare da Ni? Ya Allah ka bani mafita mai sauki a cikin lamarina.........."
Surutu take yi irin na zafi da ciwo a cen kasan zuciyarta....... Ta shagala sosai yar karamar wayarta ta shiga kuka a cikin aljihun rigarta
Da sauri ta lalubo tana tunanin ko dan sahunta ne da ya ga shiru bata tabo shi ba har yanzu?
Numbar ta zubawa ido tana kallo, domin bakuwar lamba ce a wayar Tata
A hankali ta daga tana dan gyara muryarta hadi da yin salama sannan ta yi shiru
"Amincin Allah ya tabata a gareki kema Likitana....."
Shiru ta yi, jin Muryar namiji ne, da kuma abinda aka fada din
A hankali ta dan budi bakinta ta ce" Ban gane mai maganar ba?"
Dan murmushi ya yi shima ya ce" Allah sarki dama nace akoy sanyin murya matata to be in sha Allah, jiya na turo kanwata Salma ta amsar min numbar dan na yi na yi na tareki na amsa na kula da wahala fa ki saurareni a hanya, karma aje ki ce min bakya so na na suma dan firgici"
A hankali Khausar ke dan sauke numfashinta, lokaci daya ta afka wata sabuwar duniya ta tunani da tarin mamaki
Yayan Salma?, To wane? Salma dai Salma? Kai, anya kuwa? Har yake kiranta da matarsa? Ko dai ya yi batan numba ne?, Da wahala in ba batan numba ya yi ba, ya rab.........,
Sai dai du rikicewar ta wannan karron sai ta ki kashe kiran haka kuma ta kasa yin wata magana da zai iya jin ba dadi
Ko ba komai tana kan gaba ne ta nema irin wannan
A hankali ta dan sauke numfashi jin yana ta afkin fadin ta amsa shi plz
A sanyaye sosai ta dan ja numfashi ta ce" Zan je gida ne na ga dan sahuna na kira"
Shima a sanyayen ya ce" Ba damuwa, sai kin zo, plz ki kular min da kanki, sannan zan yi kira idan kin huta dan ina so ki amsheni, ki dubeni ki bani dama kin ji kanwata????"
Murmushi ta samu kanta da saki a hankali ta furta" Na gode"
Sannan ta kashe kiran tana dan samun kanta da sake sakin murmushi
Yayan Salma? Yayunta maza biyu ta sani.....shin wanene a cikinsu?................haka kawai ta tsinci zuciyarta da jin nutsuwa da farin ciki harma ta wanke fuskarta ta fito ta cire rigarta ta nade ta saka a jaka sannan ta dauki kayanta da mayafin nan nata ta kade ta dora a kafadarta tana turo baki cike da jin haushin furucinsa wai wani bata yi kyau ba, kar ta yin, karma ta yin! Ai dama ba cewa ta yi ita mai kyau bace, kwaliya ne yace itama ta aura irin na yan mata!...........
Haka ta yi ta fadanta a zuciyarta har ta samu ta fada adaidaitar, domin ba wani a sake take ba da mayafin nan, kawai rikici ne rigima ce, kuma tunda ta yafa shi mamama da mamaki tace a haka zata tafi ne? Tace eh, mama ta ce da ta bude shi ta dan yafa jikinta duka sai tace ai ba komai , ita dai Mama kallonta ta yi tana jira ta ga da gaske? Sai kuwa ta ga da gasken ta tafi da yafen, jirantama tane yi a gidan ta dawo su zauna dan ba dabiar kirki bane hakan sam
Rai bace Taufeek ya dawo gida, domin kowa bai je nema ba dan a sama sama yake ba zai iya jure wani neman fitinan ba, direct bangarensa ya nufa yana mai kokarin kawar da dukkan wani bacin rai dake taso masa ko dan kar ya shiga hakkin abokiyar zamansa, domin ba ita ta hasala shi ba idan ya sauke mata fushinsa bai yi mata adalci ba
Sai da ya yi wanka ya sauko sakamakon irin yadda ta yi ta kai kawo cewar abincinsa na jiransa
Zama ya yi saman cafet a hankali ya mika hannu ya kashe tv dake yi, domin baya son hayaniya ne sam, kansa na dan masa ciwo, gaba daya ransa a dagule yake, sai dai abu daya da ya sani shine ba damuwa ya kyaleta, zumunci ne tunda ta katse babu yadda zai yi, ba zai saka mata wuka a wuyanta ba kan dole sai ta yi zumunci da shi tunda bata ra'ayi, yaya zata kasa yi masa uzuri a kan abinda yake aiki ne nasa? Idan ta ji cewa Yumnahma bata san komai game da aikinsa ba a matsayin dan kasuwa kuma matashin dan makaranta ta san shi ta ce me kennan? Ya dace ta masa uzuri, yaya take tunanin zai fito ya ringa yayata mata maganar sirrin aikin da yake da girma da daraja irin ta taimakon rayuwar dan adam?, Itama da gangan ta kasa gane cewa ya jima da samun takarda irin tata take tafe a makance, da gangan ta ki fahimta dan kawai ta daga masa hankali, kuma ta taki Sa'a ta daga masan domin ta fado a daidai lokacin da ta riga ta gama zamtowa tamkar jinnin jikinsa, yar uwarsa ta jinni, ama kuma ba komai dan uwankama yana iya kinka ka rayu kuwa !
Abincin ya ba hankalinsa bayan ya budi baki da kula ya ce da ita" Thank you" sannan ya yi bismillah ya dan fara tsakura
Ya koro da tabawar ya ji du ya koshi, a dole ya mayar gefe ya dan dauki jus din kwalba da ta zuba zai kai bakinsa yace" kin je kin wuni a bangaren na Hajia?"
Sai da gabanta ya fadi jin tambayar da ya yi mata, sai dai ta Basar cikin kisarta ta ce" na je , eh na je"
Yannayin da ta dan sosa gaban goshi ya bi da kallo , kasa kasa ya ce" ina nufin kin wuni a cen din ne?"
"Aa ban wuni ba, ama a kalla na kai minti ashirin......." Ta fada cike da tabbatarwa kanta ai ba zai yi fushi ba tunda ta je din
Jus din ya ajiye yana binta da kallon mamaki
A tsanake ya ce" kina so ki ce min umarnin da na baki ki je ki wuni da Hajia baki cika ba?"
Da sauri ta dago dan jin yannayin amon muryarsa ya cenza daga laushi laushi zuwa yannayi mai zafi zafi
Rai bace ya dan sake dubanta ido cikin ido ya ce" Wannan din ya zamto na farko kuma na karshe, da zaki take umarnina, idan nace kaza za'a yi shi za'a yi! Sannan ki kula ki kiyaye mutuncin dangina ta haka ne zan iya mutunta naki, Hajia kakata ce, ki kula, ki bata girman da take da shi idan ba haka ba bana tunanin in har zamu iya fahimtar junna!"
Daga haka ya mike ya bara mata jus din gaba dayama ya fice a falon
Hankalinta sosai ya nemi barin jikinta, lokaci daya jikinta ya dauki rawa ta rasa yaya zata yi, ya fi a irga tana gwada bin bayansa tana komawa dan ta ga ya nufi bangaren Hajia, karshe dai nan ta zauna ta zuba uban tagumi tana gadin dawowarsa dan ta bashi hakuri, in dai wajen hajia ne zata je zata je ta labe har yama ta yi ta dawo dan ba zata iya zama su shaki iska daya da hajiar nan ta kasheta a banza a wofi ba
Tunda ya shigo bangaren Hajia ya nemi waje ya zauna ya hade gabas da yama bai ce da ita ufan ba har ta zo da kaskon turare turaranta ta ce" Gaba daya ka fara aiki irin na wa'inda basu cika jin tsoron Allah ba magidanci, yanzu yau kwana biyu fa ban maka turare ba, Ni kuma ba zan ba wancen muciya da zanin kayan tsarinka ta je ta cenza da yan barbade barbade na matan zamani a malake min jika a sakani uku, gyara zamanka dan dage rigar nan na shafa maka a bayan cikinka wannan akace sunnansa kaikayi koma kan mashekiya, du wanda ya nufeka da asiri in sha Allahu zai kome masa ne, gyara da kyau mana wai meye kake cika kunci uwa balan balan"
Karra hade fuska ya yi ya ce" Kar ki saki ki turara min kaurin nan ke kuma!"
Hajia ta yi turus tana kallonsa, kasa kasa ta ce" Magidanci maganin tsarin ne ya zama kauri kuma?"
Cire kai ya yi bai bata amsa ba, hakan ya sa ta ajiye tana kallonsa ta ce" Kai ko wancen mai kai uwa na ifirutun ce ta bata maka? Ka dan yar nan dan rashin da'a da ta zo gaisheni kafada da kafada muka gaisa? Yar nan ka kuwa san in ta je cen bata zuwa bangaren Mamanka sai dai na kishiyoyi? Ka fa ja mata kunne dan Ni nan ko mai kwanoni ya yi kadan bale matar dansa, aikin banza aikin wofi "
"Ki matsa min da warin abin nan nace, kuma ki daina sako ubana a abinki kin dai ji na fada maki, da kike cewa wai tsoron Allah in tambayekima hijab umarnin Allah ne ko na mutun?"