Sashe 1
Da Ciwo A Zuciyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
*DA CIWO A ZUCIYATA*
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 1️⃣
LITATAFAN MARUBUCIYAR
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Tunda suka yi sallar asubahi suka yi aduo'insu kamar yadda suka saba ita ta koma ta dan kwontar da hakarkarinta, domin dama ta cika dare ne sosai tana bitar karatun jarabawar da zata gabatar a yau din a makaranta wace daga ita in sha Allah kuma sai ta karshe wace sunna yi zasu samu damar fara zuwa asibiti dan kula da mararsa lafiya ko nace koyon aikin jinya kafin su rike makamin kula da marar lafiya........., Yan uwanta kuwa su biyun watau RUKAYA da AISHA sai suka shiga hana habarsu kamar yadda ya zame masu jiki kama daga gurje tafin kafa, wanka da wuri dan gyara fuska da dai sauransu a matsayinsu da matasan yan mata masu ji da kansu da tsarin kyau daidai nasu da kuma iya wanka dan samun cikar burinsu watau birge wanda suka san sunna iya birgewa a hanyarsu ta zuwa ko ta dawowa daga makarantar summa
Sai da karfe bakwai ta yi mahaifiyarsu ta dage labule sanye cikin zumbulelen hijabinta wanda ke yi kamar zai tadeta ta fadi ama kuma baya tadetan dan damatsunnan hannayenta ke dauke shi da zarar ta motsa ta fan leka kanta tana kallonsu da dan murmushi ta sake amsa gaisuwarsu sannan ta ce" Oh Allah, ana nan ana fama da hodar ? Ina ita dayar take ban ji motsinta ba bayan tace jarabawa ne da ita yau din?"
Firgigit ta farka a barcin da take yi, mundul taundula daga saman shamakakiyar katifarta wace kwonciyar da ta yi a sama ta sake matse katifar sosai ya zamto ta takure sosai katifar dan dama ba wani auki ne da katifar ba gashi kuma ta hayeta ba ko dan juyawan nan
Hularta ta laluba ta warto ta kabeta ta dora saman gashinta da bai fi kamu biyu ba dan bata da tsayin gashi sai cika sosai a kanta sannan ta kama ta mike daga zaunen da ta yi da abin magagin barci ta kalli Aisha ta ce" Karfe nawa ne Aishe?"
Aisha ta duba yar karamar wayarta ta sanar mata bakwai ta yi, ta dora da fadin" Bamu tasheki ba dan ko takwas saura kika farka ba lati kike yi ba tunda wankan kawai ne kike yi"
Ita dai da sauri cikin yannayin halitarta wace kana iya tunanin idan har ta motsa to fa da shasheka zata yi motsin, sai dai abin mamaki jikinta da ya fi shekarunta bai hanna mata motsawa da kaza kaza ba ta yi bayi tana hangen Mamanta na batse mata bokicin da ta ajiye dan jan ruwa a rijiyar gidansu ta duba sabulunta yana nan dan haka da gudu ta fito ta kinkimi ruwan ta yi bayin da shi ta ajiye abinta sannan ta shiga tubewa dan yin wankan
A wajen wankan ne kawai ta dan dauki lokaci, dan akoyta kale kalen jiki irin na tsaftar jiki, koda yake sai ta yi anfani da lemun tsami ta darji hamatarta da du wanu lungu na jikinta wanda ke iya daukan gumi har ya bada wani wari daban irin na jikin dan adam bale ita mai tsoka a jiki masha Allah, kafin take yin wankan ta fito cikin sauri ta yi dakinsu ta warci uniforme dinta dake saman kujera ta kabe ta shiga zurawa bayan ta saka rigar mamanta da kafcecen pant dinta sannan ta zumbula hijabinta ta sake tsalake yan uwanta da har yanzun basu gama nasu shirin ba tana murmushi ta daga masu hannu da fadin" By sisters, sai mun hade"
Rukaya ta dago ta fara zuba idannuwanta a takalman da yar uwar tata ta saka takalma ne yan soso plat sun shamuge abinsu , bayan tana da takalma taki biyu bayansu ama dan yau tana jarabawa abin ya karra kwabewa takalmin kirkima ba zata tsaya ta saka ba haka zata tafi
Kai kawai ta girgiza domin ta san ba sauraronta zata yi ba in dai ta wannan fannin ne , ita a nata tsarin rayuwar tun da ta gama fahimtar rayuwarta ta gane me take ciki ta yi waje ta ajiye abubuwan nan gefe , ta riga ta sani ne bata lokaci ne a gareta ita, dan haka ta fi dauko fannin da zai gyarata wanda zata iya birge kanta da kanta da kuma Wa'inda ke tare da ita, shine karatunta da kuma nema cikin tarin rashin gajiyawa da rashin son jikin da Allah ya yi mata a cikin irin nata ni'imomin itama
Dari biyu yau aka bata, hakan ya sa take tafe tana sakin murmushi da irin tafiyar nan ta gagawa dan a hasashenta in sha Allah minti ashirin da uku zai sadata da ajinta hakan zai yi mata sauran minti goma sha takwas kafin a shiga aji kennan zata karya abinta kafin ta shige, wanda makarantar ke dan nesa da gidansu kadan ama kuma baya mata nisa dan ita a kafa take tafiyarta ta kuma dawo abinta, yan uwanta ne ke bata mamaki, tasu makarantar ta fi kusa da gida fiye da tata , ama idan ka ga sun yi tafiyar kafa ranar tai masu daren kure ba gaba ba baya sai gyaran ubangiji kawai
Cikin saurinta ta karasa wajen aunty mai dambu ta zaro dari biyunta ta mika mata ta sanar mata dambu na saba'in zata maka mata tana ta sakin murmushi tana bin hannun Aunty mai Dambu dake zuba mata da kallo, ta sani ne yau zata kile abinta dan kuwa mai cin na arba'in ya kara talatin ai zai more iya morewa
Zama ta yi nan ta wanke hannu ta maida hankali ta ci dambun nan sannan ta sayi ruwa daya ta shanye tasss kafin ta mike tana sauke ajiyar zuciya hadi da sakin murmushi domin hankalinta ya kwonta bata da matsala da cikinta takarda kuwa a je a gabza cen dama ba matsalarta bace , watau karatu
Kasancewar ranar jarabawa ce, wa'indama basu cika zuwa makarantar ba, da masu zuwa a lati du sun iso tun kafin a shiga, hakan ya sa makarantar ta cika da wuri inda hankalin daliban du ya kakasu gida gida, domin karara zaka ga halaya uku a tare da daliban mabambanta,
Wasu zaka ga hankalinsu Kwonce yake dan sun sani sun dauka sun kuma yi iya kokarinsu sun riga sun sani idan sun shiga ajin nan da izinin Allah ba zasu fito a tutar babu ba, watau ko yayane zasu dauki na dauka ko su cinye baki daya
Wasun zaka ga sunna ta fama da bude litafi sunna ta bitar abinda ba zai zauna masu a kai ba, saima ya zubar da dan wanda suka cika dare sunna dauka domin dama basu cika leka litafin ba sai irin wannan dama ta samu ta jarabawa, sai ko daidaikun da zaka ga wayarsu ce a hannunsu hankalinsu kwonce, yawanci ya'yan baba da rai ne da suke tunanin tunda babansu ya tara to fa basu da matsala da damun kansu da yin karatu ko faman fafutukar samun takarda , wannan din ba shine a gabansu ba, gidansu an tara a yi sama a yi kasa su kam sun san ko abokin baba ne zai basu aiki a wajen da ya dace da su, shi yasa basu da damuwa a abinda zasu tarar na jarabawar su ci ko su ki ci matsalar wanda ya daurawa kansa matsalar ne, kai hasalima sun zo makarantar ne dan kar a yi masu fada a gida dan iyayensu ne ke so su yi karatun ba wai su ba!
Hankali Kwonce ta nufo hanyar ajin nasu, inda yawancin daliban suke, tana tafe tana dan gaisawa da kusan du wanda ta hadu da shi faran faran da murmushinta domin ita dai ba gwali takeda na son birge wani ba, bata kuma zo makaranta dan ta birge wane ko ta bata da wane ba, wannan shiriritar ba da ita ba, to ita batama ga anfanin hakan ba sam, ana ta kai wa yake ta kafa in ba shirmen wasu daliban bama.................
"Abokina, ga fa mutuniyar cen tafe, ka ga kamarma sidar hannu ake ko me aka samu da safiyar nan?" Kamal ya fada yana dan murmushin shakiyanci yana kallonta da irin tafiyar da take yi ba abinda ya dadata da kasa , bata da damuwar komai sai ta abinda yake gabanta, wanda hakan abin mamaki ne a wajen samari da yan matan yanzu, duba da irin yadda kowa ke rike da nasa akidar na kin raini, da ɗorawa kai abinda ya fi karfin kai dai da sauransu...........
*DA CIWO A ZUCIYATA*
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 1️⃣
LITATAFAN MARUBUCIYAR
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Tunda suka yi sallar asubahi suka yi aduo'insu kamar yadda suka saba ita ta koma ta dan kwontar da hakarkarinta, domin dama ta cika dare ne sosai tana bitar karatun jarabawar da zata gabatar a yau din a makaranta wace daga ita in sha Allah kuma sai ta karshe wace sunna yi zasu samu damar fara zuwa asibiti dan kula da mararsa lafiya ko nace koyon aikin jinya kafin su rike makamin kula da marar lafiya........., Yan uwanta kuwa su biyun watau RUKAYA da AISHA sai suka shiga hana habarsu kamar yadda ya zame masu jiki kama daga gurje tafin kafa, wanka da wuri dan gyara fuska da dai sauransu a matsayinsu da matasan yan mata masu ji da kansu da tsarin kyau daidai nasu da kuma iya wanka dan samun cikar burinsu watau birge wanda suka san sunna iya birgewa a hanyarsu ta zuwa ko ta dawowa daga makarantar summa
Sai da karfe bakwai ta yi mahaifiyarsu ta dage labule sanye cikin zumbulelen hijabinta wanda ke yi kamar zai tadeta ta fadi ama kuma baya tadetan dan damatsunnan hannayenta ke dauke shi da zarar ta motsa ta fan leka kanta tana kallonsu da dan murmushi ta sake amsa gaisuwarsu sannan ta ce" Oh Allah, ana nan ana fama da hodar ? Ina ita dayar take ban ji motsinta ba bayan tace jarabawa ne da ita yau din?"
Firgigit ta farka a barcin da take yi, mundul taundula daga saman shamakakiyar katifarta wace kwonciyar da ta yi a sama ta sake matse katifar sosai ya zamto ta takure sosai katifar dan dama ba wani auki ne da katifar ba gashi kuma ta hayeta ba ko dan juyawan nan
Hularta ta laluba ta warto ta kabeta ta dora saman gashinta da bai fi kamu biyu ba dan bata da tsayin gashi sai cika sosai a kanta sannan ta kama ta mike daga zaunen da ta yi da abin magagin barci ta kalli Aisha ta ce" Karfe nawa ne Aishe?"
Aisha ta duba yar karamar wayarta ta sanar mata bakwai ta yi, ta dora da fadin" Bamu tasheki ba dan ko takwas saura kika farka ba lati kike yi ba tunda wankan kawai ne kike yi"
Ita dai da sauri cikin yannayin halitarta wace kana iya tunanin idan har ta motsa to fa da shasheka zata yi motsin, sai dai abin mamaki jikinta da ya fi shekarunta bai hanna mata motsawa da kaza kaza ba ta yi bayi tana hangen Mamanta na batse mata bokicin da ta ajiye dan jan ruwa a rijiyar gidansu ta duba sabulunta yana nan dan haka da gudu ta fito ta kinkimi ruwan ta yi bayin da shi ta ajiye abinta sannan ta shiga tubewa dan yin wankan
A wajen wankan ne kawai ta dan dauki lokaci, dan akoyta kale kalen jiki irin na tsaftar jiki, koda yake sai ta yi anfani da lemun tsami ta darji hamatarta da du wanu lungu na jikinta wanda ke iya daukan gumi har ya bada wani wari daban irin na jikin dan adam bale ita mai tsoka a jiki masha Allah, kafin take yin wankan ta fito cikin sauri ta yi dakinsu ta warci uniforme dinta dake saman kujera ta kabe ta shiga zurawa bayan ta saka rigar mamanta da kafcecen pant dinta sannan ta zumbula hijabinta ta sake tsalake yan uwanta da har yanzun basu gama nasu shirin ba tana murmushi ta daga masu hannu da fadin" By sisters, sai mun hade"
Rukaya ta dago ta fara zuba idannuwanta a takalman da yar uwar tata ta saka takalma ne yan soso plat sun shamuge abinsu , bayan tana da takalma taki biyu bayansu ama dan yau tana jarabawa abin ya karra kwabewa takalmin kirkima ba zata tsaya ta saka ba haka zata tafi
Kai kawai ta girgiza domin ta san ba sauraronta zata yi ba in dai ta wannan fannin ne , ita a nata tsarin rayuwar tun da ta gama fahimtar rayuwarta ta gane me take ciki ta yi waje ta ajiye abubuwan nan gefe , ta riga ta sani ne bata lokaci ne a gareta ita, dan haka ta fi dauko fannin da zai gyarata wanda zata iya birge kanta da kanta da kuma Wa'inda ke tare da ita, shine karatunta da kuma nema cikin tarin rashin gajiyawa da rashin son jikin da Allah ya yi mata a cikin irin nata ni'imomin itama
Dari biyu yau aka bata, hakan ya sa take tafe tana sakin murmushi da irin tafiyar nan ta gagawa dan a hasashenta in sha Allah minti ashirin da uku zai sadata da ajinta hakan zai yi mata sauran minti goma sha takwas kafin a shiga aji kennan zata karya abinta kafin ta shige, wanda makarantar ke dan nesa da gidansu kadan ama kuma baya mata nisa dan ita a kafa take tafiyarta ta kuma dawo abinta, yan uwanta ne ke bata mamaki, tasu makarantar ta fi kusa da gida fiye da tata , ama idan ka ga sun yi tafiyar kafa ranar tai masu daren kure ba gaba ba baya sai gyaran ubangiji kawai
Cikin saurinta ta karasa wajen aunty mai dambu ta zaro dari biyunta ta mika mata ta sanar mata dambu na saba'in zata maka mata tana ta sakin murmushi tana bin hannun Aunty mai Dambu dake zuba mata da kallo, ta sani ne yau zata kile abinta dan kuwa mai cin na arba'in ya kara talatin ai zai more iya morewa
Zama ta yi nan ta wanke hannu ta maida hankali ta ci dambun nan sannan ta sayi ruwa daya ta shanye tasss kafin ta mike tana sauke ajiyar zuciya hadi da sakin murmushi domin hankalinta ya kwonta bata da matsala da cikinta takarda kuwa a je a gabza cen dama ba matsalarta bace , watau karatu
Kasancewar ranar jarabawa ce, wa'indama basu cika zuwa makarantar ba, da masu zuwa a lati du sun iso tun kafin a shiga, hakan ya sa makarantar ta cika da wuri inda hankalin daliban du ya kakasu gida gida, domin karara zaka ga halaya uku a tare da daliban mabambanta,
Wasu zaka ga hankalinsu Kwonce yake dan sun sani sun dauka sun kuma yi iya kokarinsu sun riga sun sani idan sun shiga ajin nan da izinin Allah ba zasu fito a tutar babu ba, watau ko yayane zasu dauki na dauka ko su cinye baki daya
Wasun zaka ga sunna ta fama da bude litafi sunna ta bitar abinda ba zai zauna masu a kai ba, saima ya zubar da dan wanda suka cika dare sunna dauka domin dama basu cika leka litafin ba sai irin wannan dama ta samu ta jarabawa, sai ko daidaikun da zaka ga wayarsu ce a hannunsu hankalinsu kwonce, yawanci ya'yan baba da rai ne da suke tunanin tunda babansu ya tara to fa basu da matsala da damun kansu da yin karatu ko faman fafutukar samun takarda , wannan din ba shine a gabansu ba, gidansu an tara a yi sama a yi kasa su kam sun san ko abokin baba ne zai basu aiki a wajen da ya dace da su, shi yasa basu da damuwa a abinda zasu tarar na jarabawar su ci ko su ki ci matsalar wanda ya daurawa kansa matsalar ne, kai hasalima sun zo makarantar ne dan kar a yi masu fada a gida dan iyayensu ne ke so su yi karatun ba wai su ba!
Hankali Kwonce ta nufo hanyar ajin nasu, inda yawancin daliban suke, tana tafe tana dan gaisawa da kusan du wanda ta hadu da shi faran faran da murmushinta domin ita dai ba gwali takeda na son birge wani ba, bata kuma zo makaranta dan ta birge wane ko ta bata da wane ba, wannan shiriritar ba da ita ba, to ita batama ga anfanin hakan ba sam, ana ta kai wa yake ta kafa in ba shirmen wasu daliban bama.................
"Abokina, ga fa mutuniyar cen tafe, ka ga kamarma sidar hannu ake ko me aka samu da safiyar nan?" Kamal ya fada yana dan murmushin shakiyanci yana kallonta da irin tafiyar da take yi ba abinda ya dadata da kasa , bata da damuwar komai sai ta abinda yake gabanta, wanda hakan abin mamaki ne a wajen samari da yan matan yanzu, duba da irin yadda kowa ke rike da nasa akidar na kin raini, da ɗorawa kai abinda ya fi karfin kai dai da sauransu...........