Sashe 96
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wadinnan kalamai na Hajia sun karra rikita duniyar Nana,
takan ji a duniya ta fi kowa asara a da dan ta zamto mace wace ba zata yi mulki ba kuma ƴaƴanta ba zasu yi mulki ba, sai dai a kwanakin nan da take fuskantar tsantsan tashin hankalin duniya daga kowa ya sa ta fara manta abinda ya jaza mata bakin jinnin ta dawo ta ringa fuskantar rayuwa da abinda ake kira shiga ukun duniya da lahira, domin ko mahaifiyar da ta kawo ta duniya basu da wata hulda ta kusancin da ta wuce hangen nesa da kiyayewa gudun kar ta cutar da ita
Tana gaba, Dayana na biye da ita kamar zata fadi suka fito suka nufi bangaren su
sunna shiga Dayana murya a bude kamar yadda shaye shaye ya bude mata ita ta dubi mahaifiyarta ta ce" Mama, yanzu yaya zan yi kennan?"
Murya na rawa, tana daf da fashewa da kuka ta ce"Hakuri zaki yi, nace hakuri zaki yi kamar yadda kowa ke yi idan ya rasa wani abin, ki yi hakuri da shi, ki yi hakuri nace Dayana!"
Dayana ta sake kallonta kirjinta na dokawa ta ce" Mama, idan ban same shi ba, ina iya mutuwa"
Nana ta kafeta da ido, ido cikin ido ta ce" Sai ki maida hankali!"
Daga nan ta barta nan tsaye ta nufi dakinta ta fada saman gado ta fashe da matsanancin kukan da ta kasa hanna fitowar amon sa, kuka mai gunji da tashin hankali.....
TABAS maganar YUSUF ta tabata a lokacin da yace da ita sai ya adabeta, gashi kuwa yana adabar Tata da muguwar adabar da ko kallo bata ishe shi ba, yana kona duniyarta da shiru da kyautatawa, bai fito ya yi fito na fito da ita ko wata fitinar ba, ama a haka ita ke wahala fiye da kowa a rayuwar nan ta yanzu, ita ta san an gama gamawa da ita, ba ɗan uwanta, ba mahaifiyarta ba mutanen gida da na waje sai daidaikun dake karra tunzurata zuwa karra tsanar YUSUF din, su dinma tana iya rantsewa ingiza wawa suke yi mata
.......wannan kennan.....
Bayan fitar su Nana da kusan minti ashirin ya shigo falon Hajia
gannin bata falo ya karasa dakinta yana salama, kana ganninsa zaka gane yana dauke da magana ne wace ba zai bari ta kwana ba
Hajia dake kwonce saman gadonta ta kama ta zauna tana kallonsa ta ce" MALEEK ne ? Barka da warhaka ina fatan lafiya kake?"
Baki ya fara cunowa, kafin ya jingina da bango yana kallonta ya ce" Shikenan Ni kennan sai a ringa yi min auren dole kina kallo ba zaki hanna ba?"
Hajia ta kafe shi da ido, a hankali ta ce " Auren dole kuma?"
YUSUF ya gyada kai tana kallonta ya ce" TABAS!"
Hajia ta dauko hannunta ta dage habarta ta ce" Da RAUDA din aka yi maka auren dole MALIK?"
YUSUF ya kuma gyada mata kai ya ce" Gaskiya ya isheki hakanan, kin ga daga wannan a barni na zaba, dama shi na shigo in fada maki!"
Har ga Allah Hajia sai ta rasa amsar bashi, ya zamo ta rakashi da ido har ya bar dakin nata ya rufo mata ya tafi sannan ta sauke ajiyar zuciya tana girgiza kai, sai kuma ta saki murmushi ta yi addu'a ta sake komawa ta kwonta dan sarai zata nuna masa auren dole, ba dai auren yace ba ko? hum!
" Baki ji ana fadin karfe duka karfe bane? yi a hankali kar ki jimu, ki kuma cinye sumul ki zo nan ki kwonta!" Mah ke fadawa RAUDA dake kokowa da allura zaune gaban plate din abinci
Dagowa ta yi ta kalli wajen da Mah ke nufin ta kwonta, saman gadonta, sai ta dan yi shiru tana tunanin rabonta da kwana saman gadon an dan jima fa, kuma ita ta so su yi magana da Mah ama gaba daya Mah ta ki bata dama, bata san dalili ba
ajiyar zuciya ta sauke ta shiga cin abincin tana tunani a cikin ranta, ita kadai sai ta jinjina kai ta kuma girgiza ta dantse lebe ta kuma dauke kanta
har ta gama ta kwashe kwanukan ta kai kicin ta darwaye ta dawo da sauri ta shige dakin Mah dan bata so su hadu da Salima a yau, bata san yaya zata iya da tambayoyin Salimar ba, bata san ko tana da amsar ba Salimar ba, dan ita dinma bata da amsar ba kanta
da dan gudu ta shige ciki ta karasa ta yi brush ta fito ta kwonta
ta jima tana juye juye kafin ta yi barci, duka Mah na zaune tana kallonta har sai da barcin ya dauketa sannan ta yi murmushi ita kuma ta mike ta haye salaya ta shiga nafila da Adu'o'in tsari wa ƴaƴanta da fatan Allah ya saka albarka a wannan hadin ya kuma kawo sauki a duk wata fitina dake tafe da hadin.......
____________________________________
Har kusan karfe goma sha daya na dare ya nufi bayan gida, wato wajen sirrin da kuma wajen da suke buyan yan jagaliyansu
Taj dake tsaye kikam ne ya yi gaggawar dukar da ƙafarsa kamar yadda ya saba sannan ya mike bayan ya bashi dama
zama yayi saman kujera yana duban Taj, hakan ya sa Taj din zaunawa yana fuskantarsa a tausashe ya ce" Dangane da ISHAK hakane, aiki aka bashi, kuma yana da vidios da yawa da hotuna da voice note wa'inda na yi mamakin dalilin da yasa bai ba mutanen da suka saka shi aikin ba har aka yi nadin sarauta, kuma duk irin yadda ka ture shi a jikinka dan ka ga iya gudun ruwansa bai falasa ba, ama Ni dai na gaza hakuri sai da na bugar da shi sosai na kwaso komai, gasunnan kai nake jira na kona su "
YUSUF ya yi murmushi yana kallon Taj ya ce" Ya cenza nufinsa a kaina ne, shi yasa ya kasa yada abubuwan da ya dauka, zan karra bashi wata jarabawar idan ya cinye zan yafe masa, dan rayuwa ba zai yiwu mutun yace shi da kowa yana rikici ba, kuma idan kace zaka kasance mai riko wata rana ko da kanka ba zaka yarda ba, Allah shi kyauta "
Taj ya amsa da amen sannan ya dora da fadin" Mutanen nan su biyu ne kawai suka fito da sir, dan daudun nan da dayar matar, mahaifiyar Madame na ciki, na kamo dan daudun har yanzu barci yake yi dan na masa allura ne,"
YUSUF ya kalle shi da dan yannayin mamaki ya ce" Are You sure tana ciki?"
Taj ya tabbatar masa hakan ya sa ya yi murmushi ya mike yana fadin" Dan firgita shi dan ina so daga an tambaye shi ya kai ku wajen bokayen matar Please"
Murmushi shima Taj ya yi yana shafa sabuwar askar da ya siyo, shi fa sai ya yi masa yanka dan ubansa dan ya gani meye damuwar da ta saka shi saka hijab?
Tunda ya shigo falon kaurin abubuwan da suka turara ke yi masa maraba, dukda an sa turaran wuta akoy kaurin abin
Dakinsa ya wuce direct ya shige bayi ya bude wata loka ya ciro hade haden wajen Bah ya haɗa ya yi wanka, ya dauro alwallah ya fito ya haye salaya
A kalla ya kai karfe biyu na dare ya sauka daga saman salayar ya nufi dakin nata hankali kwonce ya je ya kama abin budewa ya bude sannan ya kai hannunsa wajen kunna fitila ya kunna, hakan ya sa dakin ya garwaye da haske a lokacin da mahaifiyar Amnah ke kokarin sake hada wani garwashin da boka yace su yi tsakiyar dare su turara a kowani sako da lungun baban falon gidan hakan zai sa ya shaki warin koda baya so, idan har ya shaka an gama shi zai nemeta da kansa ko a gaban waye
A tsorace ta saki kaskon a lokacin da ta juyo da sauri gannin haske ya gama dakin
Shima sai ya yi alamun ya ji mamakin ganninta din nan ya dan juya yana fadin "
shima sai ya yi alamun ya yi mamakin ganninta a irin wannan lokacin, dan haka ya juya da dan saurin magana ya furta" ya Salam, i'm sorry"
Sai kuma ya fice da sauri yana rufo masu kofar
Rikicewa ta karshen tashin hankali sun shiga a wannan lokacin
daga ita har uwar sai suka manta abinda suka so yi, suka shiga kai kawo da tunanin hanyar fita dan a lokacin mahaifiyar ta nuna zata tafi , da kyar suka gane lokaci ya ja komai balakinsu da isar su basu isa su fita a wannan lokacin daga fada ba, a dole suka nemi waje suka yi tsuru tsuru kwanan zaune , dan jira suke yi kiran sallar asubahi ta samu ta fice a gidan, saima suka kasa gane abinda ya zo nema, karshe uwar ta ringa nuna ai kawai kar su daga hankalin su ta yiwu aikin boka tuni ya ci, ya kawo kansa da kansa ne, sai dai tsoro ya hanna su karasa turare turaren nasu da kuma kasa samun bacin kirki har asubahin ta yi suka ringa dako har aka fara fita Masallaci sannan ta samu ta yi wuffff ta fice a gidan
________________________________
Tunda aka yi sallar asubahi Mah ta zaunar da ita a bakin gado tana fuskantar ta ta shiga labarta mata asalin Wacece ita, wanene Bah a duniyarta a da, abinda ya faru da su, irin fitintinnun da ta ringa gani tun daga yan uwanta har zuwa dangin mijinta da wasu mutanen, har zuwa yanzu ire iren abinda ta gani na cenji wanda ya fi rikita mata lissafi, dan a yanzu ana so a cakula ta, a da tana bambance wanda ke sonta da wanda baya son ta, ama a yanzu du an hade mata tunani bata gane komai ƙarara sai dai ta bi da kallo
A hankali ta nisa tana kallon RAUDA dake share yan hawaye lokaci zuwa lokaci tana rike da hannun Mah
takan ji a duniya ta fi kowa asara a da dan ta zamto mace wace ba zata yi mulki ba kuma ƴaƴanta ba zasu yi mulki ba, sai dai a kwanakin nan da take fuskantar tsantsan tashin hankalin duniya daga kowa ya sa ta fara manta abinda ya jaza mata bakin jinnin ta dawo ta ringa fuskantar rayuwa da abinda ake kira shiga ukun duniya da lahira, domin ko mahaifiyar da ta kawo ta duniya basu da wata hulda ta kusancin da ta wuce hangen nesa da kiyayewa gudun kar ta cutar da ita
Tana gaba, Dayana na biye da ita kamar zata fadi suka fito suka nufi bangaren su
sunna shiga Dayana murya a bude kamar yadda shaye shaye ya bude mata ita ta dubi mahaifiyarta ta ce" Mama, yanzu yaya zan yi kennan?"
Murya na rawa, tana daf da fashewa da kuka ta ce"Hakuri zaki yi, nace hakuri zaki yi kamar yadda kowa ke yi idan ya rasa wani abin, ki yi hakuri da shi, ki yi hakuri nace Dayana!"
Dayana ta sake kallonta kirjinta na dokawa ta ce" Mama, idan ban same shi ba, ina iya mutuwa"
Nana ta kafeta da ido, ido cikin ido ta ce" Sai ki maida hankali!"
Daga nan ta barta nan tsaye ta nufi dakinta ta fada saman gado ta fashe da matsanancin kukan da ta kasa hanna fitowar amon sa, kuka mai gunji da tashin hankali.....
TABAS maganar YUSUF ta tabata a lokacin da yace da ita sai ya adabeta, gashi kuwa yana adabar Tata da muguwar adabar da ko kallo bata ishe shi ba, yana kona duniyarta da shiru da kyautatawa, bai fito ya yi fito na fito da ita ko wata fitinar ba, ama a haka ita ke wahala fiye da kowa a rayuwar nan ta yanzu, ita ta san an gama gamawa da ita, ba ɗan uwanta, ba mahaifiyarta ba mutanen gida da na waje sai daidaikun dake karra tunzurata zuwa karra tsanar YUSUF din, su dinma tana iya rantsewa ingiza wawa suke yi mata
.......wannan kennan.....
Bayan fitar su Nana da kusan minti ashirin ya shigo falon Hajia
gannin bata falo ya karasa dakinta yana salama, kana ganninsa zaka gane yana dauke da magana ne wace ba zai bari ta kwana ba
Hajia dake kwonce saman gadonta ta kama ta zauna tana kallonsa ta ce" MALEEK ne ? Barka da warhaka ina fatan lafiya kake?"
Baki ya fara cunowa, kafin ya jingina da bango yana kallonta ya ce" Shikenan Ni kennan sai a ringa yi min auren dole kina kallo ba zaki hanna ba?"
Hajia ta kafe shi da ido, a hankali ta ce " Auren dole kuma?"
YUSUF ya gyada kai tana kallonta ya ce" TABAS!"
Hajia ta dauko hannunta ta dage habarta ta ce" Da RAUDA din aka yi maka auren dole MALIK?"
YUSUF ya kuma gyada mata kai ya ce" Gaskiya ya isheki hakanan, kin ga daga wannan a barni na zaba, dama shi na shigo in fada maki!"
Har ga Allah Hajia sai ta rasa amsar bashi, ya zamo ta rakashi da ido har ya bar dakin nata ya rufo mata ya tafi sannan ta sauke ajiyar zuciya tana girgiza kai, sai kuma ta saki murmushi ta yi addu'a ta sake komawa ta kwonta dan sarai zata nuna masa auren dole, ba dai auren yace ba ko? hum!
" Baki ji ana fadin karfe duka karfe bane? yi a hankali kar ki jimu, ki kuma cinye sumul ki zo nan ki kwonta!" Mah ke fadawa RAUDA dake kokowa da allura zaune gaban plate din abinci
Dagowa ta yi ta kalli wajen da Mah ke nufin ta kwonta, saman gadonta, sai ta dan yi shiru tana tunanin rabonta da kwana saman gadon an dan jima fa, kuma ita ta so su yi magana da Mah ama gaba daya Mah ta ki bata dama, bata san dalili ba
ajiyar zuciya ta sauke ta shiga cin abincin tana tunani a cikin ranta, ita kadai sai ta jinjina kai ta kuma girgiza ta dantse lebe ta kuma dauke kanta
har ta gama ta kwashe kwanukan ta kai kicin ta darwaye ta dawo da sauri ta shige dakin Mah dan bata so su hadu da Salima a yau, bata san yaya zata iya da tambayoyin Salimar ba, bata san ko tana da amsar ba Salimar ba, dan ita dinma bata da amsar ba kanta
da dan gudu ta shige ciki ta karasa ta yi brush ta fito ta kwonta
ta jima tana juye juye kafin ta yi barci, duka Mah na zaune tana kallonta har sai da barcin ya dauketa sannan ta yi murmushi ita kuma ta mike ta haye salaya ta shiga nafila da Adu'o'in tsari wa ƴaƴanta da fatan Allah ya saka albarka a wannan hadin ya kuma kawo sauki a duk wata fitina dake tafe da hadin.......
____________________________________
Har kusan karfe goma sha daya na dare ya nufi bayan gida, wato wajen sirrin da kuma wajen da suke buyan yan jagaliyansu
Taj dake tsaye kikam ne ya yi gaggawar dukar da ƙafarsa kamar yadda ya saba sannan ya mike bayan ya bashi dama
zama yayi saman kujera yana duban Taj, hakan ya sa Taj din zaunawa yana fuskantarsa a tausashe ya ce" Dangane da ISHAK hakane, aiki aka bashi, kuma yana da vidios da yawa da hotuna da voice note wa'inda na yi mamakin dalilin da yasa bai ba mutanen da suka saka shi aikin ba har aka yi nadin sarauta, kuma duk irin yadda ka ture shi a jikinka dan ka ga iya gudun ruwansa bai falasa ba, ama Ni dai na gaza hakuri sai da na bugar da shi sosai na kwaso komai, gasunnan kai nake jira na kona su "
YUSUF ya yi murmushi yana kallon Taj ya ce" Ya cenza nufinsa a kaina ne, shi yasa ya kasa yada abubuwan da ya dauka, zan karra bashi wata jarabawar idan ya cinye zan yafe masa, dan rayuwa ba zai yiwu mutun yace shi da kowa yana rikici ba, kuma idan kace zaka kasance mai riko wata rana ko da kanka ba zaka yarda ba, Allah shi kyauta "
Taj ya amsa da amen sannan ya dora da fadin" Mutanen nan su biyu ne kawai suka fito da sir, dan daudun nan da dayar matar, mahaifiyar Madame na ciki, na kamo dan daudun har yanzu barci yake yi dan na masa allura ne,"
YUSUF ya kalle shi da dan yannayin mamaki ya ce" Are You sure tana ciki?"
Taj ya tabbatar masa hakan ya sa ya yi murmushi ya mike yana fadin" Dan firgita shi dan ina so daga an tambaye shi ya kai ku wajen bokayen matar Please"
Murmushi shima Taj ya yi yana shafa sabuwar askar da ya siyo, shi fa sai ya yi masa yanka dan ubansa dan ya gani meye damuwar da ta saka shi saka hijab?
Tunda ya shigo falon kaurin abubuwan da suka turara ke yi masa maraba, dukda an sa turaran wuta akoy kaurin abin
Dakinsa ya wuce direct ya shige bayi ya bude wata loka ya ciro hade haden wajen Bah ya haɗa ya yi wanka, ya dauro alwallah ya fito ya haye salaya
A kalla ya kai karfe biyu na dare ya sauka daga saman salayar ya nufi dakin nata hankali kwonce ya je ya kama abin budewa ya bude sannan ya kai hannunsa wajen kunna fitila ya kunna, hakan ya sa dakin ya garwaye da haske a lokacin da mahaifiyar Amnah ke kokarin sake hada wani garwashin da boka yace su yi tsakiyar dare su turara a kowani sako da lungun baban falon gidan hakan zai sa ya shaki warin koda baya so, idan har ya shaka an gama shi zai nemeta da kansa ko a gaban waye
A tsorace ta saki kaskon a lokacin da ta juyo da sauri gannin haske ya gama dakin
Shima sai ya yi alamun ya ji mamakin ganninta din nan ya dan juya yana fadin "
shima sai ya yi alamun ya yi mamakin ganninta a irin wannan lokacin, dan haka ya juya da dan saurin magana ya furta" ya Salam, i'm sorry"
Sai kuma ya fice da sauri yana rufo masu kofar
Rikicewa ta karshen tashin hankali sun shiga a wannan lokacin
daga ita har uwar sai suka manta abinda suka so yi, suka shiga kai kawo da tunanin hanyar fita dan a lokacin mahaifiyar ta nuna zata tafi , da kyar suka gane lokaci ya ja komai balakinsu da isar su basu isa su fita a wannan lokacin daga fada ba, a dole suka nemi waje suka yi tsuru tsuru kwanan zaune , dan jira suke yi kiran sallar asubahi ta samu ta fice a gidan, saima suka kasa gane abinda ya zo nema, karshe uwar ta ringa nuna ai kawai kar su daga hankalin su ta yiwu aikin boka tuni ya ci, ya kawo kansa da kansa ne, sai dai tsoro ya hanna su karasa turare turaren nasu da kuma kasa samun bacin kirki har asubahin ta yi suka ringa dako har aka fara fita Masallaci sannan ta samu ta yi wuffff ta fice a gidan
________________________________
Tunda aka yi sallar asubahi Mah ta zaunar da ita a bakin gado tana fuskantar ta ta shiga labarta mata asalin Wacece ita, wanene Bah a duniyarta a da, abinda ya faru da su, irin fitintinnun da ta ringa gani tun daga yan uwanta har zuwa dangin mijinta da wasu mutanen, har zuwa yanzu ire iren abinda ta gani na cenji wanda ya fi rikita mata lissafi, dan a yanzu ana so a cakula ta, a da tana bambance wanda ke sonta da wanda baya son ta, ama a yanzu du an hade mata tunani bata gane komai ƙarara sai dai ta bi da kallo
A hankali ta nisa tana kallon RAUDA dake share yan hawaye lokaci zuwa lokaci tana rike da hannun Mah