← Book details Azal Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 117

Sashe 56

Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Metaforce online business ne na crypto
Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai
*METAFORCE*
Yana da level 1_12
Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12
YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE

💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI.....

*Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2*

💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover
Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique)

Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique)

Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?)

Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo

Idannuwansa ya lumshe a hankali bayan ya kalli fuskarsa, a nutse ya fitar da hannunsa daga cikin alkyabarsa mai dumi ya amshi gaisuwar Barka da zuwan da yake yi masa, sai dai yana amsawar da dan sakin fuska ya shige ciki cikin takunsa yadda ya saba, ba zaka taba cankar halin da yake ciki ba a haka, domin sam bai nuna abinda yake ciki ba, kai zaka iya cewa babu abinda ya gani har ya bacewa ganninsu

yannayinta ya nuna tashin hankalinta a bayane har ta zauna ta dafe gaban goshinta ranta na kuna

da dan yannayin damuwa da gannin damuwarta ya karaso kusa da kujerar ya zauna yana fadin" Angel, me yake faruwa?, ko na yi laifi ne?"

rai bace ta dago dubanta tana dubansa ta bude bakinta tana fadin" Na sha fada maka, a nan kasar Hausa kake, na fada maka bayan kasar Hausar ka hadu da wace bata dauki haka matsayin abinda ba laifi ba, ko a larabawan kunna rungume wace ba muharamarku bane? Ni ba muharamarka bace tunda babu wanda ya shaida daurin aure a da kai, me yasa kake son zubar min da mutunci a wajen da aka dauke Ni ake son bani daraja ne? haba dan Allah, yanzu me kake so ya kalle Ni da shi?"
fada ne take yi kamar wanda ya wuce misalin bacin ranta, hakan ya sa ya zuba mata ido har ta dasa aya sannan a sanyaye ya furta" Ki yi hakuri, ban san hakan zai bata maki rai ba, kuma idan kina so sai na nemi alfarmar ganninsa na fada masa tunda kike hakan bai taba shiga tsakaninmu ba, hasalima ina maki haka dan na tsokane ki ne, Please ki yi hakuri"

yannayin fitar amon muryarsa da yadda ya hade hannayensa yana bata hakuri suka ankarar da ita abinda ta aikata

a hankali ta lumshe idannuwanta, wata matsananciyar Kunya na lulube dukkanin gaban jikinta da kofofin hancinta da idannuwanta
ko ba komai ABDALLAH ba yaro bane, kuma kamar abin ya sakata a fushi fiye da misali, domin sai da ta rufe bakinta bayan ya shiga bata hakuri a cen kasan zuciyarta ta ringa tunanin me kennan? ita dake rayuwa da dukan kirjin cewa in dai Allah ya yarda da ita duk wani wanda zai ki yarda da ita ya jima bai ki yarda da ita ba shine zata damu dan wannan mutumen ya wani yi mata kallo kamar ya kama kwartuwa? Kai koda yake walahi bai iya kallo ba, wannan kallon nasa sak irin wanda za'a yiwa wace aka kama da kato ne!

A hankali ta dago dubanta gannin Abdallah na kokarin sake bata hakuri da muryarsa dake karyar mata da zuciya, baban mutun irin wannan, mutun mai alfarma sosai a rayuwar yau da gobe?
a hankali ta dan zuba masa ido, yadda idannuwansa suka rine da abin ciwo da kuma tashin hankalin dake neman damunsa na ya bata mata rai, dan a rayuwa kwarai yana kiran damuwarta tashin hankalinsa dan haka din ne, sai ta ji tausayinsa ya kama mata zuciya

a hankali ta sakar masa murmushi tana kallonsa kasa kasa ta ce" Ka gani ko? ba nace maka mu a nan idan mace na dagawa namiji murya marinta yake yi ba? me yasa kake kyaleni ina daga muryana sama da naka?"

shi dinma murmushin ya ji ya kama shi, yana kallonta ya ce" Anya kin san so kuwa?, na tabata da kina jin abinda nake ji a kanki, da ba zaki taba tunanin Ni zan iya saka hannuna a jikinki ba, yayama zan iya dukan mace sai kace mahaukaci? ba'a dukan mace, mace tana da daraja, duk mai dukan mata jaki ne, jahili ne, mahaukaci ne, dan bai san abinda yake ciki ba!, ba zan taba iya aikata hakan ba because i love You so much "

RAUDA ta sada idannuwanta tana jin sunna ciko mata da kwallah, ita kam me zata cewa wannan bawan Allahn? me zata fada masa ne? a halin kura ya santa, domin a ranar da suka fara haduwa yana bata kudi ta karɓe ta gudu da nufin ta ci banza har tana iƙirarin ire irin su su kama yar mutane su lalata ne a kan yan kudaden da basu taka kara sun karya ba....sannu a hankali ya gwada mata itace bakuwar kudi, shi ba wannan ya kawo shi ba
muryarta a sanyaye ainun tana kallon fuskarsa ta furta" Abdallah yaya zaka ce ban san so ba, bayan i love You too???????"

idannuwansa ya tsura mata
a hankali ya furta" Da gaske kina so na ?"

RAUDA ta yi murmushi dan yadda ya yin ya bata dariya sosai

Kai ta sada a hankali ta gyada masa ta shiga wasa da yan yatsunta tana tambayar zuciyarta to mema zai hannata son sa? ai wannan din shine daidai da RAUDA shine daidai da zamanin RAUDA

a tausashe bayan ya dan sake matsowa dan daf da ita kadan ya furta" Alhamdulilah, kin san ko yanzu take so ta buga!, ta samu farin ciki, yau kin fada min kina so na, alhamdulilah, abinda ya rage min mallakar ki, ki fadawa Mah a bani abata mu tafi, ki sanar mata ta taimaka min na mori lokacin da nake da shi da wace nake so, Please ki min wannan aikin "

RAUDA ta dan zarro ido tana dan matsawa dan bata so sunna irin zaman nan ta ce" Wannan kam Ni dai ba aikina bane, abinda na san aikina ne idan an tambayeni Rauda kina son dan saurayin balaraben nan? Sai na ce na'am ya ummmih......"

Dariya ya kubce masa wace ya jima bai yi ba, har yana nuno mata hannunsu dan bata daina bashi dariya idan tace masa dan saurayi, yakan yi dariyar hakan sosai ......
da wannan firar suka samu zuciyoyinsu suka yi sanyi, sannan bai dauki lokaci ba da kansa ya nuna mata zai tafi dan sun gama magana da Mah, ta sanar masa in sha Allah da zarar sun yi maganar da BAH , ko da MALIK za'a neme shi dan bincike sannan a saka ranar aure, dan itama ba laifi ya birgeta tana fatan ya rike mata yarinya da kyau da amana

dakin Mah ta nufa ta sanar mata zai tafi, Mah din ya fito suka yi salama sannan ta nunawa RAUDA ta je ta taya Salima kula da bakin yayansu, hakan ya sa ta tafi shima ya wuce ba tare da Mah ta yarda ta yi masa Rakiya ba,

Mah dakinta ta koma ta yi kwonciyarta, ita kuma RAUDA ta nufi wajen da muryoyin maza ke tashi sunna dan zantawa ta ja ta tsaya tana tunanin shiga ko komawa?

dan kwallin nan ta warware ta yafa saman kan nata, sannan ta saka hannunta ta tura kofar ta madubi ta baban falon

wani irin sanyi ne ya yi mata bismillah, sai kanshin turarukan da ta kasa gane wane ya fi dukan zuciyarta, na wutar da ya gama kama ko'ina ko na ruwan , ko na bakin da suka gama garwayuwa suka bada kanshi daban

kasa duban mutanen falon ta yi, abu daya ta gane shine matan na gefe ne mazan na gefe, tafiyar ta mata da maza ce kennan, bayan wannan sai Muryar Salima da ta yi kiranta kasa kasa sosai domin dama itama tamkar tana cikin kaya, ji take yi wajen ya girmi tsayuwarta, sai dai kasancewar ya nuna baya son bayin gidan su kula da bakinsa dole ita baba kuma kanwarsa ita zata kula da su din, domin Mah na gannin sauran ta ki turo su ta tabbata da dalili

a sanyaye ta karasa kusa da Salima dake saka kankara da abin daukan kankarar a cikin baban jug na kwalba sai da ta cika shi sannan kasa kasa ta ce" Gwara da Allah ya kawo ki, dauki wannan bari na dauko sauran kofunnan mu kaima matan, na gama kaima mazan"

RAUDA bata ce komai ba ta saka hannunta ta dauka suka nufi wajen matan nan suka kai suka ajiye

Salima ta fara zubawa , RAUDA na saka kankarar suka ji murya a tausashe sosai an furta" RAUDA?"

Da sauri RAUDA ta dago kanta, domin Muryar nan ai ba Muryar da zata bace mata bace koda a cikin mafarki ne

idannuwansu ne suka sarke da junna ita da Bara'atu
Chapter 56 · 0% Book details