Sashe 3
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da wannan direban gidan su Bara'atu ya ja motar ya nufi gidan su angon da su da niyar kaiwa angwayen abincinsu kamar yadda al'adunmu suke a garinmu, ranar wunin biki yan matan amarya na yiwa angwaye girki gwargwadon iyawarsa su tafi su kai su zuzuba masu idan aka ci aka gama sai a basu tukwuicinsu mai tsoka mai kashi😂
Gaban wani makeken vila suka ja suka tsaya a Anguwar kwaliya dake cikin Damagaran
Tunda suka tsaya yan matan nan hankalinsu ya rabu gida biyu, domin ta yadda suka ga jikakun motocin dake parker a kofar gidan nan hankalinsu ya karra tashi, nan fa kan mai fitar da jan baki da madubi daga jaka sai mai fitar da hoda suka shiga sake gyagyarawa, dama kwaliyar yau ta musamman ce, mijin Bara'atu dan kasuwa ne sun san ko ba komai sa jimki kudade da kuma nasu summa abokin rayuwar ko abokin shashancin, lokaci ne Alkali, abinda suka sani a fitowar nan tasu sai sun yi wufff da ɗan wata ko uban wata
Ficewa direban ya yi ya je ya bubuga bisa umarnin RAUDA wace kasa kasa sosai ta ce" Baba buga masu kofar Atu tace Akoy kare , idanma daga nan zamu sauke masu mu juya fine"
Tana kiransa da baba ne saboda yana dauke da sunnan mahaifinta, sannan mutun ne mai daraja dan Adam, a kulun idan ya dauki Atu sai ya biya ya daukota ya ajiye su a makaranta, tun tana kiyawa har Atun ta kai kararta wajen Mamanta sai ta mata fadan a kan me zata ki shiga a kaisu da kawarta? A dole take shiga har ya zamo kamar yar gidan du inda zasu je tare ake kai su a motar
Bugawa ya yi ya fi a irga , gannin ba'a bude ba ya dawo yana fadin" HAJIA Rauda Inaga sai an yi kira ko kawai mu tura mu shiga?"
Rauda ta girgiza kai ta ciro karamar wayarta tana masa alamun tana zuwa
Numbar mijin Atun ta dannawa kira
Wayar na fara ringin ya daga yana fadin" Da girman kujerarki aminiyar aminiyata"
Murmushi ta yi , da salon muryarta ta ce" Muna kofa fa aminin aminiyata"
Mikewa ya yi da wayar a hannunsa daga cikin mutanen da basu wuce su shida ba, dan kuwa a dole ya tsame daga cikin taron hayaniyar jama'a ya kilace Wadinnan, domin mutanensa ne na kusa sannan abincin da za'a kawo daga gidan su amaryarsa yake so a kawo masu su, dan na jama'ar da aka yi ya tabbata da wahala a dadada masa rai, duba da ba kowa ke maraba da auren nasa ba
Da kula ya masu ja gaba har baban falon, yan matan amaryar saura sunne a gaba, sai Rauda dake rike da wani kula madaidaici tana tafiya cikin yannayinta na sanyi sanyi da kuma tsarin salon tafiyar da Allah ya haliceta da shi har ta karaso kan dokin kofar daidai direba zai juya da kula ta ce" Baba kar ka yi nisa, ba jimawa zamu yi ba"
Angon ne da kansa ya juyo yana fadin" Haba aminiyar aminiyata, ya koma idan muka gama ci sai a maidaku gida ko?"
Ajiyar zuciya ta sauke ba dan ta so ba tana jin dari darin shiga falon, bata yi tsamanin a falo zasu samu angwayen ba maimakun filin gida, sai dai bata ki shiga ba gannin ba ita kadai bace mace a cikinsu, kuma ita dai ba jimawa zata yi ba gaskiya
Takalminta ta cire a kofar dakin, kasa kasa tana binsu da kallo ta yi salama sannan ta sako kafarta mai haske da tsafta tana taka tiles din ta nufi wajen da aka ajiye abincin ta ajiye coolar ta sake juyowa dan neman wajen zama
Idannuwanta suka sauka cikin na Ishak da Nafisa
Shi Ishak din ba zata iya tantance kallon da yake yi mata ba, ama na Nafisa zata iya ajiye shi a matsayin kallon jin haushi ko na laifi? Allah masani, abinda take hangowa dai kamar tarin jin haushi ne, ta yiwu laifi ta yi mata bata sani ba? Ko ita dinma a wajenta bakin jinnin ta dauko? Dan kuwa ta kasance budurwa mai bakin jini a cikin yan mata, ba kowace budurwa ke mata magana ba, akan ce wai ta cika girman kai , da sauransu, ita kuma tana rayuwarta ne daidai misali
Kujerar da ta nufa da nufin zama ce ta ga wata tanfatsetsiyar waya ajiye, a hankali ta dauke dubanta ta dan juya dan zaunawa a wani wajen tana dan sakin murmushin abokin ango na mata tayin gefensa
Idannuwanta ne suka sake sauka bayan wani saman salaya, hannayensa harde a kirjinsa, kansa sade kasa , a hankali ta dauke dubanta a kansa ta juya ta karasa saman kujerar dake facin din wace ke dauke da wayar ta zauna ta maida dubanta wajen angon dake miko mata ruwa na cikin jarka yana mata fira a ranta kuwa ta ayana' Na tsani na ga namiji har namiji yana Sallah a daki, dan rashin mutunci ko yana aikin uban me aka yi sallar aka barshi?'
Salamce sallarsa ya yi a hankali ya sada kansa yana addu'a har ya gama ya shafa sannan ya mike ba tare da ya kalli kowa ba ya nufi wajen zamansa ya dauke wayar dake ajiye ya zauna yana sake hade rai gannin natacen kallon da yan matan nan suka bi shi da shi, kai subahanalah ya ki jinnin irin wannan hadin da ake yi yan mata da maza, su ba yara ba, ba komai ba ama sai a hadu wai a ci abinci a biya yan matan su tafi, shi kam idan ya tashi dauko hudun nan ba za'a yi wannan badalar da shi ba, yan matan kowace zata yanka ainahin abinda take so a biyata sai a biyata ba sai an zauna ana rainawa junna hankali ba
Dubansa ya kai wajen daya daga cikin abokan ango mai sunna Idriss a lokacin da ya miko masa ruwa yana fadin" Biya maradi Allah dai ya kaimu ranar aurenka, a wannan rana ban san wa zai iya amsa sunnansa ba, Allah ya karra lafiya namu"
Yannayin fuskarsa bai cenza ba daga daurewar ya amshi jus din ba dan zai sha ba ya ajiye gefe kasa kasa ya ce" Ku salame su mana bafa ba son damuwa"
A lokacin da yake furta kalmar "ku salame su mana...." a daidai lokacin ne ya sauke dubansa a kan wace take face da shi tak tak kamar an ajiyeta ne hankalinta sam ba a kan kowa ba, tana rike da goran ruwa bata bude ba , kuma bata ajiye ba
Dubansa ya so daukewa tashi daya daga kanta, sai ya samu idannuwansa da dawowa suka sake sauka a kan fuskarta a daidai lokacin da take karanta sakon Bara'atu wace mijinta ya sanar mata mutuniyarta fa gatanan ta daka fuska bayan harda biya maradi a taron, shine ta mata msg din da ya sakata sakin tautausan murmushin da ya saka gefen idannuwanta kadan suka lotsa hancinta ya sake dan budewa kadan sai kuma ya koma yannayinsa saboda gimtse murmushin da ta yi ta dago dubanta a hankali ta kai kan angon kasa kasa ta ce" Kai ko?"
Dariya angon ya yi yana fadin" Eh, ba zaki dago mu yi fira ba? Zan kuma kai kararki ne "
Murmushi ta yi tana dauke dubanta ta juyo da nufin kallon hanyar kofa, dan mamaki ke neman kasheta na abokanan tafiyar tata, yaya za'a yi su zo waje su wani saki jiki haka a gaban mazan da basu sani ba su ringa fira haka da iya yi? Tun ba'a ce su raba abincin ba har sun bubude sun shiga zubama abokan angon a plate plate sai wani irin iya yi suke yi da Gwali, ita abin har daria ya so bata, ina ajin? Ina jiji da kan? Zamani ya zo mana da sabon salo mai wuyar fasara, ace yanzu mace itace zata yi iya yin da namiji zai gane ta? Lalle wahala bata bar wasu matan ba, WALAHI tsakaninta da namiji sai dai ya bita ba dai ta bi shi ba!
A hankali idannuwanta suka sauka a kan fuskarsa, sai dai abin mamaki ko second biyar bata yi tana kallon gefen da yake zaune ba ta dauke kanta tare da nunin alamun bata san da zaman dan Adam a wajen Bama bale ya isheta kallo
Mamaki ya kama shi mai girman gaske
Har angon da wanda ya sanarwa a salami yan matan suka dawo dan waje ya ja shi ya sanar masa sakon *YUSEF* din cewar a salami yan matan nan baya son takura
Rasa yadda zai yi ya yi, a dole cikin murmushi da basu daraja ya ce" Amare, har kun fara raba abincin? Ai da baku ba kanku wahala ba, so nake a maida min ku da wuri ku shirya min hajiata a kawota da wuri wuri, sai kuma na ga har kun fara hidima da mu?
Nafisa ce ta yi gagawar dagowa tana sakin fari hadi da murmushi ta ce" Haba elhajinmu, ai ba dawainiya, an riga an zama daya, mun fara ai bari mu gama ku ci idan kun gama sai a maidamu, amaryarka kar ka damu kaima ka san tana hannun manya dole ta sha gyara "
Sai da ta dasa Aya Rauda ta dago da mamaki ta zuba mata ido
A hankali ta lumshe idannuwanta ta maido dubanta kan Elhaji, yannayin muryarta kasa kasa sannan da sanyin nan ta ce" A'a , a maida mu ya fi, sai ku samu sarari ku ci abinci cikin nutsuwa aminin aminiyata"
Da sauri Nafisa ta juyo tana kallonta, duk yadda ta so Hanna kanta nuna bacin ranta sai da ta ce" Mu zamu Hanna su sakewa ne? Ko dama an taba yi basu ci abinci ba mu mu juya? Me muka yi Kennan?"
Rauda ta sake tsareta da duban dake nunin abinda ke cikin zuciyyarta, ama bata yi magana ba, sai da ta sake bude baki zata yi magana sai ta ga Rauda din ta mike hankalinta kacokam a kan angon da ido ta masa alamun ita fa tafia take so bayan fuskarta ta wani irin nuna lalaci irin na shagwababen yaro , sannan ta masa nuni da agogon hannunta siriri mai ruwan zeba cewar lokacin ta tafi ya yi
Gaban wani makeken vila suka ja suka tsaya a Anguwar kwaliya dake cikin Damagaran
Tunda suka tsaya yan matan nan hankalinsu ya rabu gida biyu, domin ta yadda suka ga jikakun motocin dake parker a kofar gidan nan hankalinsu ya karra tashi, nan fa kan mai fitar da jan baki da madubi daga jaka sai mai fitar da hoda suka shiga sake gyagyarawa, dama kwaliyar yau ta musamman ce, mijin Bara'atu dan kasuwa ne sun san ko ba komai sa jimki kudade da kuma nasu summa abokin rayuwar ko abokin shashancin, lokaci ne Alkali, abinda suka sani a fitowar nan tasu sai sun yi wufff da ɗan wata ko uban wata
Ficewa direban ya yi ya je ya bubuga bisa umarnin RAUDA wace kasa kasa sosai ta ce" Baba buga masu kofar Atu tace Akoy kare , idanma daga nan zamu sauke masu mu juya fine"
Tana kiransa da baba ne saboda yana dauke da sunnan mahaifinta, sannan mutun ne mai daraja dan Adam, a kulun idan ya dauki Atu sai ya biya ya daukota ya ajiye su a makaranta, tun tana kiyawa har Atun ta kai kararta wajen Mamanta sai ta mata fadan a kan me zata ki shiga a kaisu da kawarta? A dole take shiga har ya zamo kamar yar gidan du inda zasu je tare ake kai su a motar
Bugawa ya yi ya fi a irga , gannin ba'a bude ba ya dawo yana fadin" HAJIA Rauda Inaga sai an yi kira ko kawai mu tura mu shiga?"
Rauda ta girgiza kai ta ciro karamar wayarta tana masa alamun tana zuwa
Numbar mijin Atun ta dannawa kira
Wayar na fara ringin ya daga yana fadin" Da girman kujerarki aminiyar aminiyata"
Murmushi ta yi , da salon muryarta ta ce" Muna kofa fa aminin aminiyata"
Mikewa ya yi da wayar a hannunsa daga cikin mutanen da basu wuce su shida ba, dan kuwa a dole ya tsame daga cikin taron hayaniyar jama'a ya kilace Wadinnan, domin mutanensa ne na kusa sannan abincin da za'a kawo daga gidan su amaryarsa yake so a kawo masu su, dan na jama'ar da aka yi ya tabbata da wahala a dadada masa rai, duba da ba kowa ke maraba da auren nasa ba
Da kula ya masu ja gaba har baban falon, yan matan amaryar saura sunne a gaba, sai Rauda dake rike da wani kula madaidaici tana tafiya cikin yannayinta na sanyi sanyi da kuma tsarin salon tafiyar da Allah ya haliceta da shi har ta karaso kan dokin kofar daidai direba zai juya da kula ta ce" Baba kar ka yi nisa, ba jimawa zamu yi ba"
Angon ne da kansa ya juyo yana fadin" Haba aminiyar aminiyata, ya koma idan muka gama ci sai a maidaku gida ko?"
Ajiyar zuciya ta sauke ba dan ta so ba tana jin dari darin shiga falon, bata yi tsamanin a falo zasu samu angwayen ba maimakun filin gida, sai dai bata ki shiga ba gannin ba ita kadai bace mace a cikinsu, kuma ita dai ba jimawa zata yi ba gaskiya
Takalminta ta cire a kofar dakin, kasa kasa tana binsu da kallo ta yi salama sannan ta sako kafarta mai haske da tsafta tana taka tiles din ta nufi wajen da aka ajiye abincin ta ajiye coolar ta sake juyowa dan neman wajen zama
Idannuwanta suka sauka cikin na Ishak da Nafisa
Shi Ishak din ba zata iya tantance kallon da yake yi mata ba, ama na Nafisa zata iya ajiye shi a matsayin kallon jin haushi ko na laifi? Allah masani, abinda take hangowa dai kamar tarin jin haushi ne, ta yiwu laifi ta yi mata bata sani ba? Ko ita dinma a wajenta bakin jinnin ta dauko? Dan kuwa ta kasance budurwa mai bakin jini a cikin yan mata, ba kowace budurwa ke mata magana ba, akan ce wai ta cika girman kai , da sauransu, ita kuma tana rayuwarta ne daidai misali
Kujerar da ta nufa da nufin zama ce ta ga wata tanfatsetsiyar waya ajiye, a hankali ta dauke dubanta ta dan juya dan zaunawa a wani wajen tana dan sakin murmushin abokin ango na mata tayin gefensa
Idannuwanta ne suka sake sauka bayan wani saman salaya, hannayensa harde a kirjinsa, kansa sade kasa , a hankali ta dauke dubanta a kansa ta juya ta karasa saman kujerar dake facin din wace ke dauke da wayar ta zauna ta maida dubanta wajen angon dake miko mata ruwa na cikin jarka yana mata fira a ranta kuwa ta ayana' Na tsani na ga namiji har namiji yana Sallah a daki, dan rashin mutunci ko yana aikin uban me aka yi sallar aka barshi?'
Salamce sallarsa ya yi a hankali ya sada kansa yana addu'a har ya gama ya shafa sannan ya mike ba tare da ya kalli kowa ba ya nufi wajen zamansa ya dauke wayar dake ajiye ya zauna yana sake hade rai gannin natacen kallon da yan matan nan suka bi shi da shi, kai subahanalah ya ki jinnin irin wannan hadin da ake yi yan mata da maza, su ba yara ba, ba komai ba ama sai a hadu wai a ci abinci a biya yan matan su tafi, shi kam idan ya tashi dauko hudun nan ba za'a yi wannan badalar da shi ba, yan matan kowace zata yanka ainahin abinda take so a biyata sai a biyata ba sai an zauna ana rainawa junna hankali ba
Dubansa ya kai wajen daya daga cikin abokan ango mai sunna Idriss a lokacin da ya miko masa ruwa yana fadin" Biya maradi Allah dai ya kaimu ranar aurenka, a wannan rana ban san wa zai iya amsa sunnansa ba, Allah ya karra lafiya namu"
Yannayin fuskarsa bai cenza ba daga daurewar ya amshi jus din ba dan zai sha ba ya ajiye gefe kasa kasa ya ce" Ku salame su mana bafa ba son damuwa"
A lokacin da yake furta kalmar "ku salame su mana...." a daidai lokacin ne ya sauke dubansa a kan wace take face da shi tak tak kamar an ajiyeta ne hankalinta sam ba a kan kowa ba, tana rike da goran ruwa bata bude ba , kuma bata ajiye ba
Dubansa ya so daukewa tashi daya daga kanta, sai ya samu idannuwansa da dawowa suka sake sauka a kan fuskarta a daidai lokacin da take karanta sakon Bara'atu wace mijinta ya sanar mata mutuniyarta fa gatanan ta daka fuska bayan harda biya maradi a taron, shine ta mata msg din da ya sakata sakin tautausan murmushin da ya saka gefen idannuwanta kadan suka lotsa hancinta ya sake dan budewa kadan sai kuma ya koma yannayinsa saboda gimtse murmushin da ta yi ta dago dubanta a hankali ta kai kan angon kasa kasa ta ce" Kai ko?"
Dariya angon ya yi yana fadin" Eh, ba zaki dago mu yi fira ba? Zan kuma kai kararki ne "
Murmushi ta yi tana dauke dubanta ta juyo da nufin kallon hanyar kofa, dan mamaki ke neman kasheta na abokanan tafiyar tata, yaya za'a yi su zo waje su wani saki jiki haka a gaban mazan da basu sani ba su ringa fira haka da iya yi? Tun ba'a ce su raba abincin ba har sun bubude sun shiga zubama abokan angon a plate plate sai wani irin iya yi suke yi da Gwali, ita abin har daria ya so bata, ina ajin? Ina jiji da kan? Zamani ya zo mana da sabon salo mai wuyar fasara, ace yanzu mace itace zata yi iya yin da namiji zai gane ta? Lalle wahala bata bar wasu matan ba, WALAHI tsakaninta da namiji sai dai ya bita ba dai ta bi shi ba!
A hankali idannuwanta suka sauka a kan fuskarsa, sai dai abin mamaki ko second biyar bata yi tana kallon gefen da yake zaune ba ta dauke kanta tare da nunin alamun bata san da zaman dan Adam a wajen Bama bale ya isheta kallo
Mamaki ya kama shi mai girman gaske
Har angon da wanda ya sanarwa a salami yan matan suka dawo dan waje ya ja shi ya sanar masa sakon *YUSEF* din cewar a salami yan matan nan baya son takura
Rasa yadda zai yi ya yi, a dole cikin murmushi da basu daraja ya ce" Amare, har kun fara raba abincin? Ai da baku ba kanku wahala ba, so nake a maida min ku da wuri ku shirya min hajiata a kawota da wuri wuri, sai kuma na ga har kun fara hidima da mu?
Nafisa ce ta yi gagawar dagowa tana sakin fari hadi da murmushi ta ce" Haba elhajinmu, ai ba dawainiya, an riga an zama daya, mun fara ai bari mu gama ku ci idan kun gama sai a maidamu, amaryarka kar ka damu kaima ka san tana hannun manya dole ta sha gyara "
Sai da ta dasa Aya Rauda ta dago da mamaki ta zuba mata ido
A hankali ta lumshe idannuwanta ta maido dubanta kan Elhaji, yannayin muryarta kasa kasa sannan da sanyin nan ta ce" A'a , a maida mu ya fi, sai ku samu sarari ku ci abinci cikin nutsuwa aminin aminiyata"
Da sauri Nafisa ta juyo tana kallonta, duk yadda ta so Hanna kanta nuna bacin ranta sai da ta ce" Mu zamu Hanna su sakewa ne? Ko dama an taba yi basu ci abinci ba mu mu juya? Me muka yi Kennan?"
Rauda ta sake tsareta da duban dake nunin abinda ke cikin zuciyyarta, ama bata yi magana ba, sai da ta sake bude baki zata yi magana sai ta ga Rauda din ta mike hankalinta kacokam a kan angon da ido ta masa alamun ita fa tafia take so bayan fuskarta ta wani irin nuna lalaci irin na shagwababen yaro , sannan ta masa nuni da agogon hannunta siriri mai ruwan zeba cewar lokacin ta tafi ya yi