Sashe 33
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Idannuwansa ya lumshe zazafan hawayen da yake ta danewa suka samu sauka a tafin hannayen nata, a hankali ya sake dora gefen fuskar nasa mai dauke da saje wanda abin rawanin ya rufe a hannun nata yana jin inama zai iya kuka wiwi irin na mata? Da ya yi ya ji sanyi a zuciyarsa
A hankali ya mike ya dawo da ita saman kujerar ya zaunar da ita sannan ya duka ya dago kansa ya sake zubawa ni'imtaciyar fuskarta mai dauke da ni'imar haske irin wace d'a ke gani a duk lokacin da ya ga fuskar mahaifiyarsa ya ce" yaya aka yi kika tashi? Nace kar ki fito fa zan zo na kai ki asibiti"
Murmushi ta sauke masa a hankali ta ce" Kai, yaya zaka duka , so kake a leko a dakeni ace na saka Sarki sun dukawa?""
Murmushin da bai yi niya ba ya yi, sai dai ba irin mamakeken murmushin nan bane, kadan ya yi mata ko zata ji sanyi, domin ya kula abinda take so ta gani a fuskarsa kennan, a hankali ya ce" Anya akoy wanda zai hannani dukawa a gabanki a nan duniya kuwa?......"
Sai kuma ya sake dubanta ya sauke ajiyar zuciya, so yake ya tambayeta shin yaya zai yi ne yanzun? Sai kuma ya kasa, saboda ya sani ko a yanzu tana da bukatar hutawa, sannan ya san irin tashin hankalin da take ji na rashin lafiyar mahaifinsa shi yasa ya yi shiru sai ajiyar zuciya sai kuma ya dubeta ya sake jimkar hannunta
A tausashe Mah ta ce" Bari in je wajen abanka, ka ga mutane zasu shigo wajenka yanzun, Please take care"
Kai ya gyada mata , ta mike ta hanna shi yi mata rakiya kamar yadda ya saba a da , dan ta riga ita ta yarda dole ne yanzun cenji ya samu ta kowane fanni a rayuwar yaron nata da ita din kanta, ama duda haka tana kallo bai zauna ba sai da ta ja baban kofar ta madubi ta rufe yana tsayensa ta shiga neman y'ar amanarta
A lokacin ne yan uwanta suka kuma zuwa, dan babu wanda ya tafi ashe, hakan ya bata mamaki gannin basu tafi ba, su uku rigis, maza biyu, mace guda
Da wata irin mutatawar da suka jima rabonsu da yi mata irinta ko magana irin haka suka shiga yi mata barka ba tare da sun kireta da sunnan da suka lakaba mata ba tunda Kadara ta sauka a kanta da uban ƴaƴanta wato mamar soyayya
Da kula sosai ƴaƴanta mai suna AGO yace" Mu karasa daga cen mu yi magana ko Andiya"
A yanzunma abin kallo ta maida su, ama bata ki binsu ba dan ta sakawa ranta su je su mata wankin baban bargo ne kamar yadda suka saba
Sunna zuwa da kula sosai Herde ta ce" Andiya, dangane da shirin gagarumin bikin da ya dace mu yiwa Malik da kuma nunawa duniya eh danmu yau ya kai matakin sarauta ne su yaya suka ce mu yi shawara mu ga nawa nawa ya dace mu hada sai a shiga shiri dan Bama so mu amshi ko sisin kwabo din Sarki, mune nan zamu masa matsayin iyayensa, ke a ganninki nawa nawa ya dace?"
Yanzun kam da tsoron rayuwa da mamaki take binsu da kallo har sai da autansu mai bi mata ya ce" Aunty yi magana mana yanke ko nawa ne mu je mu shiga shiri dan gaskiya Ni wanda zai yi girkima sai na dauko mutun daga waje"
Idannuwanta ta lumshe, ta rasa gane a wani yannayi take ciki, abinda ta sani shine yannayin da take ciki ba na farin ciki bane, dan kuwa wannan yannayi da ta jima tana mafarki a yanzu da yake bayyana kansa a gare ta a dalilin wani baban dalili na rayuwarta sai ta ji bata farin ciki da maraba da shi, a sanyaye ta ce" Biki kuma?, rasuwar da aka yi fa? Kuma kun san mahaifinsa bashi da lafiya , inaga ba wani biki da za'a yi da ya huci a masa fatan alkhairi da nauyin da ya hau kansa da addu'ar Allah yana taya shi riko"
Su Dukansu sai da suka yi jim, sai kuma Herde ta ce" Hakane, an yi rasuwa, ama gaskiya koda a cen baban gida ne idan abubuwa suka lafa zamu yi taron murnar nan , dan abin a yi murna ne, Allah ya ba Honorable lafiya"
A saman lebenta ta amsa, ta shiga alamun tana son tafiya
Ba wani kunya Ago ya ce" Kin ga ku je cikin ku zauna mu bari mu tafi wajen mazan mu zauna , yarenma sun ce gasunnan zuwa ai da iyayensu"
Yanzu kam abubuwan su sun fi karfin tunaninta, bata iya basu amsa ba sai komawar da ta yi ta shiga neman RAUDA, da kyar ta ganta zaune da wayarta a hannunta, yannayinta har yanzun bai koma normal ba dan har yanzu bata san yaya take ciki da batan uncle dinta ba, da kuma halin da kanninta yake ciki shi yasa take jira Mah ta dawo ta fada mata tana so ta je Damagaran dan ta ji halin da ake ciki da uncle dinta da kuma kanninta
A nutse Mah ta yi mata salama
Da sauri RAUDA ta dago, ta mike tana amsawa a hankali gannin wata mai kama da ita sosai a gefenta tana binta da kallo
Kai ta sinne dan sai ta ji kallon wani iri, domin irin kallon nan ne ba karewa mutun kallo tun daga sama har kasa
A tausashe Mah ta ce" Mu tafi ki karya"
RAUDA tun a nan ta so fada mata tana son tafiya, ama ta kasa, ta bi bayanta bayan ta riko hannunta kamar wace ta riko wata mai yan kannanun shekaru suka nufi cen baban bangaren famillyn, sunna tafe ana yi mata gaisuwa ta mamaki, gaisuwar da a da Bata samun rabin rabinta sai idan ta shigo fadar da mijinta ko da danta, sai gashi yau ita daya dinta ana gaisheta da girmamawa ta mamaki
Ajiyar zuciya ta sauke kawai ta girgiza kai, suka shige baban falon da salama a bakinsu
Yaran ne kawai a falon daga mazan har matan , sun yi jigum abinsu dan babu wani mai walwala ko sakewa a cikinsu, saboda rashin lafiyar iyayensu
A tare suka ringa gaishe da su Mah, saboda koda iyayensu na koyar da su wasu halayar a boye sunna da karfin gabatarwa ne a gaban idannuwansu, idan basa nan sunna jin tsoron yayarsu sosai dan bata cika shiga lamarin su ba, halayarta kusan na Bah karami ne, shi idan dai magana ta haɗaka da shi bukatarka ka kai ya gyada kai shikenan, daga nan ba kari ,
Amsawa Mah ta yi ita kadai da kula sosai, taba tambayar su iyayensu
Yayarsu ta sanar mata sunna daki, dan haka ta dubi yayar tasu da yar fara'a a fuskarta ta ce" Salima, Please ga y'ata nan ki saka a yi mata abun kari, sannan ga ky din dakina nan ki saka a tsaftace min na san ba dai dati da kura ba "
Da sauri Salimar ta amsa tana fadin" To Mah, bari in kira masu aiki yanzu a yi, bakuwa zo ki zauna a wancen falon "
Mah ta yi mata alamun ta je, a dole Rauda ta nufi wani falon a zuciyarta tana mamakin fasalin ginnin da irin tsarin furniture din dake ko'ina
Herde ta kasa hakuri bayan sun nufi bangaren Bah da sabon yannayin girmama Mah ta ce" baby wai wannan yarinyar fa wacece?"
Mah ta kama kofar dakin da ta dan juyo da kula ta ce" Bari in ga yaya dakin yake,"
sai kuma ta dan saki murmushi ta ce" Lah wai Raudar ce baki sani ba? Y'ata ce fa"
Daga haka ta yi shiegwarta ta bar yar uwar ta da baki bude cike da matsanancin mamaki da tunanin maganar Tata, kai ina ba gaskiya bane, bayan YUSUF ai Andiya bata kuma haihuwa ba, bata kuma haihuwa ba tabas, tunda ko yanzu ai kamar ta gabatar da wancen yarinyar ne a wajen su Salima ko? Idan yar uwarsu ce har sai an gabatar da ita anya kuwa?
Jira ta yi har Mah ta fito daga dakin idannuwanta sun yi wani iri, suka shiga ta masa addu'a ta koma falo ta zauna dan yanzu ta ga wajen zama, Mah kuwa ta komawarta daki wajen Bah
Tana zama da yan mintunna ya'yan yayanta da na kanninta da yarta guda da matansu suka karaso har bangaren dan haka ta mike fuska hade ta ce da ya'yan Bah kowa ya je dakinsa tunda ba komai suke yi a falon ba, ita kuma da isa suka cike falon sunna ta firarsu yan matan kuwa sai selfi din kansu suke dauka, babu mai shiga harkar yar uwarta sunna dane danen wayoyinsu, domin kar ku manta bangaren mahaifinsa babu abinda bai zuba ba, koda mahaifiyarsa ba a nan take ba bai rage su da komai ba saboda mahaifinsa da kanninsa da yake yiwa uzuri ainun,
Raudah
Zuciyarta na cikin hali na damuwa da kunci mai girman gaske
An kawo mata abinci mai rai da lafiya da su lipton, kayan kari dai da zata iya cewa bata taɓa haɗawa kanta su ta ci ba, ama ta kasa ci sai milo ta amsa da Salima ta haɗa mata ta bata sannan ta zauna a dan nesa da ita kadan, da katon hijabinta itama ,
Babu hirar da suke yi, ama Salima bata tafi ta barta ba
Sai da ta gama shan milo din ta sauke ajiyar zuciya ta ciro wayarta daga cikin jakar Mah a hankali ta shiga tunanin numbar da zata kira
Da kyar ta tuno ta Aminu mai adaidaita, dan haka da sauri ta lalubo numbar ta danna masa kira
Bata jima tana ringing ba Umar ya daga kiran yana yi mata doguwar salama
A sanyaye RAUDA ta amsa, ta shiga gaishe shi kamar yadda yake gaisheta
A tausashe ta ce" Aminu, yaya Abanmu an ganshi kuwa?"
A hankali ya mike ya dawo da ita saman kujerar ya zaunar da ita sannan ya duka ya dago kansa ya sake zubawa ni'imtaciyar fuskarta mai dauke da ni'imar haske irin wace d'a ke gani a duk lokacin da ya ga fuskar mahaifiyarsa ya ce" yaya aka yi kika tashi? Nace kar ki fito fa zan zo na kai ki asibiti"
Murmushi ta sauke masa a hankali ta ce" Kai, yaya zaka duka , so kake a leko a dakeni ace na saka Sarki sun dukawa?""
Murmushin da bai yi niya ba ya yi, sai dai ba irin mamakeken murmushin nan bane, kadan ya yi mata ko zata ji sanyi, domin ya kula abinda take so ta gani a fuskarsa kennan, a hankali ya ce" Anya akoy wanda zai hannani dukawa a gabanki a nan duniya kuwa?......"
Sai kuma ya sake dubanta ya sauke ajiyar zuciya, so yake ya tambayeta shin yaya zai yi ne yanzun? Sai kuma ya kasa, saboda ya sani ko a yanzu tana da bukatar hutawa, sannan ya san irin tashin hankalin da take ji na rashin lafiyar mahaifinsa shi yasa ya yi shiru sai ajiyar zuciya sai kuma ya dubeta ya sake jimkar hannunta
A tausashe Mah ta ce" Bari in je wajen abanka, ka ga mutane zasu shigo wajenka yanzun, Please take care"
Kai ya gyada mata , ta mike ta hanna shi yi mata rakiya kamar yadda ya saba a da , dan ta riga ita ta yarda dole ne yanzun cenji ya samu ta kowane fanni a rayuwar yaron nata da ita din kanta, ama duda haka tana kallo bai zauna ba sai da ta ja baban kofar ta madubi ta rufe yana tsayensa ta shiga neman y'ar amanarta
A lokacin ne yan uwanta suka kuma zuwa, dan babu wanda ya tafi ashe, hakan ya bata mamaki gannin basu tafi ba, su uku rigis, maza biyu, mace guda
Da wata irin mutatawar da suka jima rabonsu da yi mata irinta ko magana irin haka suka shiga yi mata barka ba tare da sun kireta da sunnan da suka lakaba mata ba tunda Kadara ta sauka a kanta da uban ƴaƴanta wato mamar soyayya
Da kula sosai ƴaƴanta mai suna AGO yace" Mu karasa daga cen mu yi magana ko Andiya"
A yanzunma abin kallo ta maida su, ama bata ki binsu ba dan ta sakawa ranta su je su mata wankin baban bargo ne kamar yadda suka saba
Sunna zuwa da kula sosai Herde ta ce" Andiya, dangane da shirin gagarumin bikin da ya dace mu yiwa Malik da kuma nunawa duniya eh danmu yau ya kai matakin sarauta ne su yaya suka ce mu yi shawara mu ga nawa nawa ya dace mu hada sai a shiga shiri dan Bama so mu amshi ko sisin kwabo din Sarki, mune nan zamu masa matsayin iyayensa, ke a ganninki nawa nawa ya dace?"
Yanzun kam da tsoron rayuwa da mamaki take binsu da kallo har sai da autansu mai bi mata ya ce" Aunty yi magana mana yanke ko nawa ne mu je mu shiga shiri dan gaskiya Ni wanda zai yi girkima sai na dauko mutun daga waje"
Idannuwanta ta lumshe, ta rasa gane a wani yannayi take ciki, abinda ta sani shine yannayin da take ciki ba na farin ciki bane, dan kuwa wannan yannayi da ta jima tana mafarki a yanzu da yake bayyana kansa a gare ta a dalilin wani baban dalili na rayuwarta sai ta ji bata farin ciki da maraba da shi, a sanyaye ta ce" Biki kuma?, rasuwar da aka yi fa? Kuma kun san mahaifinsa bashi da lafiya , inaga ba wani biki da za'a yi da ya huci a masa fatan alkhairi da nauyin da ya hau kansa da addu'ar Allah yana taya shi riko"
Su Dukansu sai da suka yi jim, sai kuma Herde ta ce" Hakane, an yi rasuwa, ama gaskiya koda a cen baban gida ne idan abubuwa suka lafa zamu yi taron murnar nan , dan abin a yi murna ne, Allah ya ba Honorable lafiya"
A saman lebenta ta amsa, ta shiga alamun tana son tafiya
Ba wani kunya Ago ya ce" Kin ga ku je cikin ku zauna mu bari mu tafi wajen mazan mu zauna , yarenma sun ce gasunnan zuwa ai da iyayensu"
Yanzu kam abubuwan su sun fi karfin tunaninta, bata iya basu amsa ba sai komawar da ta yi ta shiga neman RAUDA, da kyar ta ganta zaune da wayarta a hannunta, yannayinta har yanzun bai koma normal ba dan har yanzu bata san yaya take ciki da batan uncle dinta ba, da kuma halin da kanninta yake ciki shi yasa take jira Mah ta dawo ta fada mata tana so ta je Damagaran dan ta ji halin da ake ciki da uncle dinta da kuma kanninta
A nutse Mah ta yi mata salama
Da sauri RAUDA ta dago, ta mike tana amsawa a hankali gannin wata mai kama da ita sosai a gefenta tana binta da kallo
Kai ta sinne dan sai ta ji kallon wani iri, domin irin kallon nan ne ba karewa mutun kallo tun daga sama har kasa
A tausashe Mah ta ce" Mu tafi ki karya"
RAUDA tun a nan ta so fada mata tana son tafiya, ama ta kasa, ta bi bayanta bayan ta riko hannunta kamar wace ta riko wata mai yan kannanun shekaru suka nufi cen baban bangaren famillyn, sunna tafe ana yi mata gaisuwa ta mamaki, gaisuwar da a da Bata samun rabin rabinta sai idan ta shigo fadar da mijinta ko da danta, sai gashi yau ita daya dinta ana gaisheta da girmamawa ta mamaki
Ajiyar zuciya ta sauke kawai ta girgiza kai, suka shige baban falon da salama a bakinsu
Yaran ne kawai a falon daga mazan har matan , sun yi jigum abinsu dan babu wani mai walwala ko sakewa a cikinsu, saboda rashin lafiyar iyayensu
A tare suka ringa gaishe da su Mah, saboda koda iyayensu na koyar da su wasu halayar a boye sunna da karfin gabatarwa ne a gaban idannuwansu, idan basa nan sunna jin tsoron yayarsu sosai dan bata cika shiga lamarin su ba, halayarta kusan na Bah karami ne, shi idan dai magana ta haɗaka da shi bukatarka ka kai ya gyada kai shikenan, daga nan ba kari ,
Amsawa Mah ta yi ita kadai da kula sosai, taba tambayar su iyayensu
Yayarsu ta sanar mata sunna daki, dan haka ta dubi yayar tasu da yar fara'a a fuskarta ta ce" Salima, Please ga y'ata nan ki saka a yi mata abun kari, sannan ga ky din dakina nan ki saka a tsaftace min na san ba dai dati da kura ba "
Da sauri Salimar ta amsa tana fadin" To Mah, bari in kira masu aiki yanzu a yi, bakuwa zo ki zauna a wancen falon "
Mah ta yi mata alamun ta je, a dole Rauda ta nufi wani falon a zuciyarta tana mamakin fasalin ginnin da irin tsarin furniture din dake ko'ina
Herde ta kasa hakuri bayan sun nufi bangaren Bah da sabon yannayin girmama Mah ta ce" baby wai wannan yarinyar fa wacece?"
Mah ta kama kofar dakin da ta dan juyo da kula ta ce" Bari in ga yaya dakin yake,"
sai kuma ta dan saki murmushi ta ce" Lah wai Raudar ce baki sani ba? Y'ata ce fa"
Daga haka ta yi shiegwarta ta bar yar uwar ta da baki bude cike da matsanancin mamaki da tunanin maganar Tata, kai ina ba gaskiya bane, bayan YUSUF ai Andiya bata kuma haihuwa ba, bata kuma haihuwa ba tabas, tunda ko yanzu ai kamar ta gabatar da wancen yarinyar ne a wajen su Salima ko? Idan yar uwarsu ce har sai an gabatar da ita anya kuwa?
Jira ta yi har Mah ta fito daga dakin idannuwanta sun yi wani iri, suka shiga ta masa addu'a ta koma falo ta zauna dan yanzu ta ga wajen zama, Mah kuwa ta komawarta daki wajen Bah
Tana zama da yan mintunna ya'yan yayanta da na kanninta da yarta guda da matansu suka karaso har bangaren dan haka ta mike fuska hade ta ce da ya'yan Bah kowa ya je dakinsa tunda ba komai suke yi a falon ba, ita kuma da isa suka cike falon sunna ta firarsu yan matan kuwa sai selfi din kansu suke dauka, babu mai shiga harkar yar uwarta sunna dane danen wayoyinsu, domin kar ku manta bangaren mahaifinsa babu abinda bai zuba ba, koda mahaifiyarsa ba a nan take ba bai rage su da komai ba saboda mahaifinsa da kanninsa da yake yiwa uzuri ainun,
Raudah
Zuciyarta na cikin hali na damuwa da kunci mai girman gaske
An kawo mata abinci mai rai da lafiya da su lipton, kayan kari dai da zata iya cewa bata taɓa haɗawa kanta su ta ci ba, ama ta kasa ci sai milo ta amsa da Salima ta haɗa mata ta bata sannan ta zauna a dan nesa da ita kadan, da katon hijabinta itama ,
Babu hirar da suke yi, ama Salima bata tafi ta barta ba
Sai da ta gama shan milo din ta sauke ajiyar zuciya ta ciro wayarta daga cikin jakar Mah a hankali ta shiga tunanin numbar da zata kira
Da kyar ta tuno ta Aminu mai adaidaita, dan haka da sauri ta lalubo numbar ta danna masa kira
Bata jima tana ringing ba Umar ya daga kiran yana yi mata doguwar salama
A sanyaye RAUDA ta amsa, ta shiga gaishe shi kamar yadda yake gaisheta
A tausashe ta ce" Aminu, yaya Abanmu an ganshi kuwa?"