Sashe 78
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hajia ta ajiye maganar, Mah da Bah sunna gyada kai alamun hakan ya yi, sai dai shi uncle Umar kansa a kasa yake dai da suka saurara ya dago yana neman damar yin magana, hakan ya sa suka bashi dama
A tausashe sosai ya ce" Ku yi hakuri, ku yi hakuri, ku yi hakuri, ama Ni ba wanda ya dace da rikon dukiya irin wannan bace, san kuwa Ni tsoroma kudaden nan da gidajen nan suka bani, Dan Allah a yi hakuri ama babu wanda ya cencenci ajiyar dukiyar nan sama da HONORABLE ko MALIK, a yi hakuri kar a hadani da rikicin nan dan tsaf barci zai kaurace min " Ya karashe maganar da raha, wace Hajia kadai ta yi yar dariya
Bah shima ya sauke ajiyar zuciya yana dubansu ya ce" Ka san dukiya irin wannan, ajiyar ta ba abu ne mai sauki ba, a wannan zamanin da duniya ta ki gaskiya ko bankin ka kai sai ya zamo ka san me ake ciki me ke shiga yake fita, saboda yanzu duniya ta ki gaskiya sai hamdallah, dukiyar nan in dai ba wata damuwa a sakata a hannun YUSUF , shine zai sakata inda ya dace"
YUSUF kam du sauraronsu yake, bayanan su na saka shi nazartar lamarin har sai da suka gama magana ana ta fadin eh shi zai adana, kanta a kasa ita, shi kuwa yana bin su da kallo sannan ya dan sauke ajiyar zuciya a nutse ya ce" Babu wanda zai ajiye mata dukiyarta sai ita da kanta!"
Gaba dayansu sai da suka dubi fuskarsa, shi kuwa a lokacin da ya ajiye maganar ya dubeta ne, hakan ya sa suka yi ido hudu shi da ita
Kansa ya dauke daga dubanta ya maida kan Hajia, Mah, da su Bah ya ce" Da ace sun haihu, dole za'a yi rabin gado a killace na abinda suka samu har zuwa yadda Allah ya yi, ama a yanzu dukiyar nan tata ce, kuma kudi ne da gidaje, ba zai yiwu a killace su a ajiye har zuwa yaushe? kudi juya su ake yi, saboda komai yawansu idan ba'a juyawa sunna iya zama kadan, gidaje za'a saka mutanen da suka sani su bi daya bayan daya, wa'inda suka zamo ba zasu anfanu yadda ya dace ba za'a saida a gina wasu ko a sayi wasu ginanu, wa'inda zasu anfanu za'a ba manyan ma'aikata haya, ta yadda kudi zasu ringa shigowa a duk lokacin da ya dace kuma in zasu bar gida zasu gyara dukan abinda suka lalata"
Ya dan dakata a nutse ya dora da fadin" Dukiya da ta zama ta kudi za'a yi dogon tunani na abinda za'a dora na kasuwanci, a taba kadan ba da yawa ba a gwada, ta kula da abinta da kanta, ba ina nufin ta je ta tsare ba, daga gida komai ya shiga ya fita tana gani tana kuma bi har a ga abinda ya bada, idan har ya je yadda ake so sai a sake daukan wata hanyar ta yadda kudade zasu ringa shigowa ne yadda ya kamata"
Ya sake dakatarwa da maganar da yake yi, sannan ya dora da fadin" Zai zamo da account daban wanda kudaden kashewarta na abinda ta yi niya ne a ciki, domin rayuwa ce, tana iya son yin wata gwaninta Tata da mutanenta, kuma idan ya zamo tana jin nauyin tambayar mamanta sai kawai ta yi abinta kai tsaye, ama na haramta mata ciyar da kanta ko tufatar da kanta ko yiwa kanta wata hidimar da aljihunta in dai ina ray..."
ya dan dakatar a hankali ya furta" Raye....."
Ya sake dubansu, dan irin yadda fuskokinsu suka yi, ciki harda ita da ta kasa daina kallonsa, dan ko ta dauke idannuwanta sai ta maida kan fuskarsa a nutse ya furta" Babu abinda zata yi da kanta, ama dukkan abinda za'a yi tana wajen da kuma izinin ta, Abubuwan ajiyewa za'a bude wajen ajiya, na rikewa a gida za'a ba Mamanta ta rike mata, Allah ya bamu ikon kiyaye hakin wani"
Kusan gaba daya da amen aka amsa, Hajia kuwa ta wani gyara zama tana murmushi ta ce" gagara kake uban marayu, gagara kake uban talakawa, ja gaba kake uban masu uba, mararsa ubanma kai ne babansu, ka yi naka ka yi nasu ka yi na masu karfi , na mararsa karfinma kai ke yi, Jikan Hajia khadija kake, jika a wajen gagara marigayi d'an Bello da Ameerah ikon Allah...... Dole...."
Kallon da ya dakata yana mata dan niyarsa tafiya saboda yanada abubuwan yi sosai, ama ikon Allah na Hajia ya saka shi yin turus yana kallonta ya sakata dan tsagaitaWa , ama bata yi shiru ba sai da ta kalli Bah ta ce" Yanzu yaya ka ga abinda na fada maka a lokacin da nace maka tabas yadda ka fada MAKIK , MALIK ne?"
Kai ya girgiza kawai a tausashe ya ce" Shikenan? in tafi?"
Kafin Hajia ta yi magana Mah dake murmushin Hajia ta dago da kula ta ce" AA, kar ka tafi, ina son sannin ina matarka? yaya aka yi wata hudu kennan da aure bata hau abinda ya dace ace ta hau na darajar dake kanta ba?"
A tausashe ta fada, sai dai kana kallo zaka gane abinda ta tambaya amsarsa take so,
RAUDA, kanta ke kasa, a hankali ta samu kanta da jin sarawar kai , a hankali ta lumshe idannuwanta ta ki dagowa , dukda ta so mikewa ta bada waje, ama kuma ta kasa hakan dan haka kawai ta ji dole sai ta ji amsar nan!
Hajia ce ta dauki magana tana mikewa ta ce" Ya Salam, wai dama bata bangarenki yarinyar nan? da bakina na ce da ita bangarenki akace ta je ba na Hajia ba, Ina zuwa"
Ficewa ta yi, Mah kuwa ta dauke dubanta daga fuskar Bah, tana kallon gefe daya, a ranta tana ayana' Ba fa zai yiwu ba, sai dai na ringa tsintar wasu abubuwa dake iya zubar da kimar dana a banza a wofi? a zuwanta gidan nan, ma'aikata uku ta kora dan jin dadi da isa, a cikinsu harda wace tun kafin a haifi YUSUF din take gidan, wai aikin me zata yi ta tsufa ta yi tafiyarta, sai ita ta saka aka maidata bangarenta, dama ba wani aiki ne take yi ba, tana dai dan abubuwan da ana zasu gagareta ba dan da aka nemi ta zauna ta huta ba zata rasa dukkan abinda ya dace na rayuwa ba, ta nuna dan Allah a barta ta yi aikinta dan idan ta zauna zaunewa zata yi .
An dauki mintina kusan sha biyar Hajia ta shigo ranta bace tana tafe a hankali a hankali duba da jikin tsufa , ama muryarta radau tana fada ta dubi Bah dake zaune saman kujera ta kai zaune itama saman kujerar daidai Hajia ta shigo , bayanta kuwa Amaryar da ake nufin tasa ce ta shigo itama , wace shi gaba daya yake mantawa da ita, dan ya yi waje daya ya ajiyeta tuni, Hajia ta ce" BELLO, ya dace ka tsawatarwa iyalinka kan abubuwan da ake son sako min, wa'inda bana tunanin in zan iya hakurinsu, ita a wa zata kai AMNAH bangarenta ta zauna, ? inace nan MALIK yace ta zauna shine zata zaune tsayin watannin nan a bangarenta tana kallo bata zo ta sanar min ba? me kennan? hanyar da za'a saka yarinya ta raina min jika ake nema dan kuwa an saka ta baudewa umarninsa me ake nufi in ba haka ba? a'a fa, Ni dama na so a duba lamarin nan aka dakatar da Ni, bafa zan dauka ba!"
Ta karashe rai a bace, shi kuwa ya ringa kallon Hajia da ta zauna tana sada kanta a nutse ta furta" Allah ya huci zuciyarki Hajia, ban san hakan zai haifar da matsala ba, kuma ban san baki san tana cen ba"
Hajia baba ta ki bata amsa dan ita abin ya bata mata rai, kuma da ta je yanzu yarinyar nan barci take ta yi, a dakinta a saman gadonta, ita dai rabonsu da junna da iyayenta da suka yi maganar wai a kai kayanta bangarensa ta nuna a kawo bangarenta a ajiye wasu, wasu ta ajiye a na Mah din har ya yi magana, ta nuna bata so a kuma dawo mata kan maganar dan ba zata lamunta ba, idan aka matsa kuwa su je da ita kawai zasu waiwayo su, dan ita diris take jira a san yadda aka yi, dan ba zata taba so ace wannan ce matarsa ta farko ba, uwar yayansa, itama tarbiyya bata isheta ba bale ta ba wani!
Bah ya saka baki sosai wajen ba hajia hakurin shima, dan a yanzu abinda zai iya yi kennan, dan a kashe maganar, ama shima zai ganta ta fada masa manufarta
hakurin da Bah ke badawa kuwa sai ya kular da Mah, gani take yi ita da ta fada masa kennan bai yarda ba? gashi kuma da Hajia ta fada yana tarewa kar a yi magana ko? ba laifi su ci gaba da yi, ita dai akoy lokacin da ba zata dauki abubuwan nan ba!
Uncle Umar kuwa gannin abin zai kacame sai ya yi kamar yana amsa waya ya fice a falon, yana son ya kirayi RAUDA ta basu waje itama, ama kuma ya ga kanta a kasa bata dago ba ko kadan, kuma ya sha mamakin gannin bata fita ba, ko me yasa?
Da kyar Hajia baba ta yi hakurin, Hajia ta mike ta tafi, zuciyarta cike da farin cikin ko ba komai a irin turbar da ta karra dora yarinyar ko a yanzu da wahala su ji dadinta, kuma zata ci gaba dan walahi bakin rai bakin fama ita da ANDIYA, ba zata taba jin dadin sarakuwa ba!
Bayan hajia ta nunawa Amnah wajen da ta zata zauna, ta zauna din sai bin kowa take yi da kallo kasa kasa , Hajiar ta ce" Ka yi hakuri da take abinda ka ce , kuma Ni ban san cewa har yanzu bata cen din ba"
Sai a lokacin ya bude idannuwansa yana kallon rigimamiyar kakarsa, ita dai a yi rikici baya ce mata komai, a yi ta surutu kuwa haka ta fi so
A tausashe sosai ya ce" Ku yi hakuri, ku yi hakuri, ku yi hakuri, ama Ni ba wanda ya dace da rikon dukiya irin wannan bace, san kuwa Ni tsoroma kudaden nan da gidajen nan suka bani, Dan Allah a yi hakuri ama babu wanda ya cencenci ajiyar dukiyar nan sama da HONORABLE ko MALIK, a yi hakuri kar a hadani da rikicin nan dan tsaf barci zai kaurace min " Ya karashe maganar da raha, wace Hajia kadai ta yi yar dariya
Bah shima ya sauke ajiyar zuciya yana dubansu ya ce" Ka san dukiya irin wannan, ajiyar ta ba abu ne mai sauki ba, a wannan zamanin da duniya ta ki gaskiya ko bankin ka kai sai ya zamo ka san me ake ciki me ke shiga yake fita, saboda yanzu duniya ta ki gaskiya sai hamdallah, dukiyar nan in dai ba wata damuwa a sakata a hannun YUSUF , shine zai sakata inda ya dace"
YUSUF kam du sauraronsu yake, bayanan su na saka shi nazartar lamarin har sai da suka gama magana ana ta fadin eh shi zai adana, kanta a kasa ita, shi kuwa yana bin su da kallo sannan ya dan sauke ajiyar zuciya a nutse ya ce" Babu wanda zai ajiye mata dukiyarta sai ita da kanta!"
Gaba dayansu sai da suka dubi fuskarsa, shi kuwa a lokacin da ya ajiye maganar ya dubeta ne, hakan ya sa suka yi ido hudu shi da ita
Kansa ya dauke daga dubanta ya maida kan Hajia, Mah, da su Bah ya ce" Da ace sun haihu, dole za'a yi rabin gado a killace na abinda suka samu har zuwa yadda Allah ya yi, ama a yanzu dukiyar nan tata ce, kuma kudi ne da gidaje, ba zai yiwu a killace su a ajiye har zuwa yaushe? kudi juya su ake yi, saboda komai yawansu idan ba'a juyawa sunna iya zama kadan, gidaje za'a saka mutanen da suka sani su bi daya bayan daya, wa'inda suka zamo ba zasu anfanu yadda ya dace ba za'a saida a gina wasu ko a sayi wasu ginanu, wa'inda zasu anfanu za'a ba manyan ma'aikata haya, ta yadda kudi zasu ringa shigowa a duk lokacin da ya dace kuma in zasu bar gida zasu gyara dukan abinda suka lalata"
Ya dan dakata a nutse ya dora da fadin" Dukiya da ta zama ta kudi za'a yi dogon tunani na abinda za'a dora na kasuwanci, a taba kadan ba da yawa ba a gwada, ta kula da abinta da kanta, ba ina nufin ta je ta tsare ba, daga gida komai ya shiga ya fita tana gani tana kuma bi har a ga abinda ya bada, idan har ya je yadda ake so sai a sake daukan wata hanyar ta yadda kudade zasu ringa shigowa ne yadda ya kamata"
Ya sake dakatarwa da maganar da yake yi, sannan ya dora da fadin" Zai zamo da account daban wanda kudaden kashewarta na abinda ta yi niya ne a ciki, domin rayuwa ce, tana iya son yin wata gwaninta Tata da mutanenta, kuma idan ya zamo tana jin nauyin tambayar mamanta sai kawai ta yi abinta kai tsaye, ama na haramta mata ciyar da kanta ko tufatar da kanta ko yiwa kanta wata hidimar da aljihunta in dai ina ray..."
ya dan dakatar a hankali ya furta" Raye....."
Ya sake dubansu, dan irin yadda fuskokinsu suka yi, ciki harda ita da ta kasa daina kallonsa, dan ko ta dauke idannuwanta sai ta maida kan fuskarsa a nutse ya furta" Babu abinda zata yi da kanta, ama dukkan abinda za'a yi tana wajen da kuma izinin ta, Abubuwan ajiyewa za'a bude wajen ajiya, na rikewa a gida za'a ba Mamanta ta rike mata, Allah ya bamu ikon kiyaye hakin wani"
Kusan gaba daya da amen aka amsa, Hajia kuwa ta wani gyara zama tana murmushi ta ce" gagara kake uban marayu, gagara kake uban talakawa, ja gaba kake uban masu uba, mararsa ubanma kai ne babansu, ka yi naka ka yi nasu ka yi na masu karfi , na mararsa karfinma kai ke yi, Jikan Hajia khadija kake, jika a wajen gagara marigayi d'an Bello da Ameerah ikon Allah...... Dole...."
Kallon da ya dakata yana mata dan niyarsa tafiya saboda yanada abubuwan yi sosai, ama ikon Allah na Hajia ya saka shi yin turus yana kallonta ya sakata dan tsagaitaWa , ama bata yi shiru ba sai da ta kalli Bah ta ce" Yanzu yaya ka ga abinda na fada maka a lokacin da nace maka tabas yadda ka fada MAKIK , MALIK ne?"
Kai ya girgiza kawai a tausashe ya ce" Shikenan? in tafi?"
Kafin Hajia ta yi magana Mah dake murmushin Hajia ta dago da kula ta ce" AA, kar ka tafi, ina son sannin ina matarka? yaya aka yi wata hudu kennan da aure bata hau abinda ya dace ace ta hau na darajar dake kanta ba?"
A tausashe ta fada, sai dai kana kallo zaka gane abinda ta tambaya amsarsa take so,
RAUDA, kanta ke kasa, a hankali ta samu kanta da jin sarawar kai , a hankali ta lumshe idannuwanta ta ki dagowa , dukda ta so mikewa ta bada waje, ama kuma ta kasa hakan dan haka kawai ta ji dole sai ta ji amsar nan!
Hajia ce ta dauki magana tana mikewa ta ce" Ya Salam, wai dama bata bangarenki yarinyar nan? da bakina na ce da ita bangarenki akace ta je ba na Hajia ba, Ina zuwa"
Ficewa ta yi, Mah kuwa ta dauke dubanta daga fuskar Bah, tana kallon gefe daya, a ranta tana ayana' Ba fa zai yiwu ba, sai dai na ringa tsintar wasu abubuwa dake iya zubar da kimar dana a banza a wofi? a zuwanta gidan nan, ma'aikata uku ta kora dan jin dadi da isa, a cikinsu harda wace tun kafin a haifi YUSUF din take gidan, wai aikin me zata yi ta tsufa ta yi tafiyarta, sai ita ta saka aka maidata bangarenta, dama ba wani aiki ne take yi ba, tana dai dan abubuwan da ana zasu gagareta ba dan da aka nemi ta zauna ta huta ba zata rasa dukkan abinda ya dace na rayuwa ba, ta nuna dan Allah a barta ta yi aikinta dan idan ta zauna zaunewa zata yi .
An dauki mintina kusan sha biyar Hajia ta shigo ranta bace tana tafe a hankali a hankali duba da jikin tsufa , ama muryarta radau tana fada ta dubi Bah dake zaune saman kujera ta kai zaune itama saman kujerar daidai Hajia ta shigo , bayanta kuwa Amaryar da ake nufin tasa ce ta shigo itama , wace shi gaba daya yake mantawa da ita, dan ya yi waje daya ya ajiyeta tuni, Hajia ta ce" BELLO, ya dace ka tsawatarwa iyalinka kan abubuwan da ake son sako min, wa'inda bana tunanin in zan iya hakurinsu, ita a wa zata kai AMNAH bangarenta ta zauna, ? inace nan MALIK yace ta zauna shine zata zaune tsayin watannin nan a bangarenta tana kallo bata zo ta sanar min ba? me kennan? hanyar da za'a saka yarinya ta raina min jika ake nema dan kuwa an saka ta baudewa umarninsa me ake nufi in ba haka ba? a'a fa, Ni dama na so a duba lamarin nan aka dakatar da Ni, bafa zan dauka ba!"
Ta karashe rai a bace, shi kuwa ya ringa kallon Hajia da ta zauna tana sada kanta a nutse ta furta" Allah ya huci zuciyarki Hajia, ban san hakan zai haifar da matsala ba, kuma ban san baki san tana cen ba"
Hajia baba ta ki bata amsa dan ita abin ya bata mata rai, kuma da ta je yanzu yarinyar nan barci take ta yi, a dakinta a saman gadonta, ita dai rabonsu da junna da iyayenta da suka yi maganar wai a kai kayanta bangarensa ta nuna a kawo bangarenta a ajiye wasu, wasu ta ajiye a na Mah din har ya yi magana, ta nuna bata so a kuma dawo mata kan maganar dan ba zata lamunta ba, idan aka matsa kuwa su je da ita kawai zasu waiwayo su, dan ita diris take jira a san yadda aka yi, dan ba zata taba so ace wannan ce matarsa ta farko ba, uwar yayansa, itama tarbiyya bata isheta ba bale ta ba wani!
Bah ya saka baki sosai wajen ba hajia hakurin shima, dan a yanzu abinda zai iya yi kennan, dan a kashe maganar, ama shima zai ganta ta fada masa manufarta
hakurin da Bah ke badawa kuwa sai ya kular da Mah, gani take yi ita da ta fada masa kennan bai yarda ba? gashi kuma da Hajia ta fada yana tarewa kar a yi magana ko? ba laifi su ci gaba da yi, ita dai akoy lokacin da ba zata dauki abubuwan nan ba!
Uncle Umar kuwa gannin abin zai kacame sai ya yi kamar yana amsa waya ya fice a falon, yana son ya kirayi RAUDA ta basu waje itama, ama kuma ya ga kanta a kasa bata dago ba ko kadan, kuma ya sha mamakin gannin bata fita ba, ko me yasa?
Da kyar Hajia baba ta yi hakurin, Hajia ta mike ta tafi, zuciyarta cike da farin cikin ko ba komai a irin turbar da ta karra dora yarinyar ko a yanzu da wahala su ji dadinta, kuma zata ci gaba dan walahi bakin rai bakin fama ita da ANDIYA, ba zata taba jin dadin sarakuwa ba!
Bayan hajia ta nunawa Amnah wajen da ta zata zauna, ta zauna din sai bin kowa take yi da kallo kasa kasa , Hajiar ta ce" Ka yi hakuri da take abinda ka ce , kuma Ni ban san cewa har yanzu bata cen din ba"
Sai a lokacin ya bude idannuwansa yana kallon rigimamiyar kakarsa, ita dai a yi rikici baya ce mata komai, a yi ta surutu kuwa haka ta fi so