Sashe 29
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ya yi niya dan kansa ya ce" Zan iya Bara maki amanar mahaifiyata kafin gobe da safe?"
Idannuwanta dake lumshe ta bude da sauri tamkar wace ta yi maye ta tsaida dubanta waje daya ta kasa furta koda A ne
A tausashen da yannayin yau ya haifar masa na rashin da suka yi da halin da mahaifinsa ke ciki da halin da kakarsa ke ciki ya ce" Ba zan iya fita daga inda nake a yanzu ba, ita kuma bata da lafiya, zaki iya zaunawa a gefenta ki rike wayar nan a kusa da ke, idan jikinta ya kiya ki sanar min?"
Yanzun kam ji ta yi ta gaza yin shirun, a dole ta budi baki tana kallon Mah ta ce" Yaya zan yi mata?, bata da lafiya fa"
Shima ya dauke numfashi a hankali ya ce" Addu'a zaki yi mata, zaki iya?"
Rauda ta ja numfashi a hankali ta ce" Zan iya in sha Allah"
Shiru ya yi na dan lokaci, kafin ya iya budar bakinsa kasa kasa sosai ya furta" JAZAKILAH"
Kalmar da ta sa RISLAN sake zuba masa ido har ya katse kiran ya maido da hankalinsa kansa
Hannu ya bashi suka yi nusabaha cikin alhinin rashin da ya zamo na su duka suka yiwa junna jaje a takaice sannan ya juya ya nufi ciki ba tare da ya karra koda kalma daya ba, sai a lokacin RISLAN ya juya ya koma wajen da mahaifiyarsa ta yi tamkar zuciyarta zata buga dan bakin ciki
Yana zuwa bata tsaya wata wata ba ta saka hannunta ta make gefen keyarsa rai bace ta ce" Haka ka zabarwa kanka? Yana tsaye kana jira tamkar uban gidanka? Ka fi shi nasaba dan a jikina ba dati!, idan har haka kake so ba damuwa ka je ka bi shi kamar kare da mai gidansa, ba daraja ba mutunci, yadda yake takamar yana da jinnin sarauta a jikinsa kaima haka, kuma kai ka fi shi duk wata daraja dan baka wulakantar da kanka ba!"
Kasa cewa komai RISLAN ya yi, kansa a kasa har ta gama fadan da bai san dalilinsa, fadan da baya so sam ace mahaifiyarsa ce ke yinsa, domin fada ne na rashin gaskiya, a gaban idannuwanta a dazun motocin wa'inda koda babu su baba BELLO a doron kasa kafin ya hau sai sun hau suka ringa shigowa, a irin wannan lokacin ya dace ne ace tana cen wajen Hajia an gama kimtsa wajen dan karbar bakin da tabas da yawa sun kamo hanya, ga wata rigimar da ta bilo ta rikicin sai an gurfanar da iyalan mamacin a kan rashin hankalin da suka yi na kin fadin rashin lafiyarsa, rikici dai kala kala wanda a tunaninsa a matsayinta Na mace daya a tsakaninsu zuwa yanzu tana cen tana neman mafitar da ta dace da su baki daya, sai ga wani gihitacen zance a bakinta? Allah ya yiwa wannan buri nata tsawa dan ya tabata zata jazawa kanta fitinar da ta fi karfin ta da su ƴaƴanta baki daya
Gaba daya shi ya wakilci mahaifinsa , hankalinsa ya rarabu gida uku, yana yi yana lekawa wajen mahaifinsa wa'inda matansa ke zagaye da shi hankalinsu tashe baki dayansu, domin babu wace zata so ace wani abu ya same shi daga nan zuwa safe dan bakin labarima irin wannan shine ace ɗan matar da suke yiwa wani gani gani ya haye karagar mulkin nan, kai wata har ta mutu a cikinsu domin abu ne da zai iya dukan zukatansu baki daya, hakan ya sa ba su ba, ba ƴaƴansu ba, kowane rike da carbi sunna masa addu'a kuma sunna jira karin ruwan da likita ya jona masa ya kare ko ya dawo cikin hayacinsa
Shi dinma wannan addu'a ita ta fi komai tsaye masa a zuciya, ba zai taba misalta halin da zai shiga ba idan muguwar Kadara ta biyo da shi ta hanyar nan, shi ya san ba zai taba yarda da wannan tatsuniyar ba, shi yasa hankalinsa gaba daya a tashe yake, sau uku yana dora hannunsa wajen kan mamacin nan a ransa yana rokon Allah, Allah ya sa ya ga alamun doguwar summa ce ya yi, haka kuma idan ya je wajen mahaifinsa ya duka daf da fuskarsa a sanyaye yakan ce" Abu, dan Allah ka rufa min asiri ka tashi, Abu rasuwar dan uwanka na san dole zata gigitaka, ama ka tashi ka ji? Ka tashi ka masa addu'a sannan ka hau mulkinka, Abu Ni din gaba dayana yaushe ka haife Ni? Dan Allah ka tashi kar zuciyata ta buga ka ji Abu?"
Idan ya mike ya fito har duhu duhu yake gani, ga wasu masu tsaron da Hajia ta karro da taimakon commisionan yan sanda da sarakan da suka isa tuni an zagaye masarautar haka kuma kiri kiri idan ya motsa sukan motsa ne da shi, abin har ya fara neman zautar da dukkan tunaninsa dan ba zai iya misalta wannan tashin hankalin a kansa ba, ina ba dai shi ba
Yakan kirayi RAUDA ne a dukkan motsinsa, tun tana amsa shi idannuwanta biyu, har barci ya dauketa a bayan Mah a kwonce bayan ta shinfida masu bargo sun kwonta a falon tana yi tana taba goshin Mah din da yi mata sannu har barci ya yi gaba da ita itama bai hakura ba, a cikin barcin take dagawa idannuwa a rufe ruf dan ta gaji sosai ta amsa shi sannan ta mayar da idannuwan ta rufe har aka fara kiraye kirayen sallar asubahi ta farka sakamakon farkawar da Mah ta yi suka yi ido hudu
Da sauri ta shiga lalaubar hijabinta a dan birkice ta ce" Hajia kin farka? Yaya jikin?"
Mah da ta jingina da jikin kujera ta sauke ajiyar zuciya tana kirkiro murmushi a tausashe ta ce" Ki daina ce min Hajia, ba zaki kirayeni da Mama ba? Ko bakya so na zama mamanki?"
Kafeta Rauda ta yi da ido ta kasa cewa komai, tana kallonta ta ciciba ta tashi ta nufi ciki dan yin wanka domin ta dauri niya sunna gama sallah zasu kama hanya zata ga ubanda zai hannata fita yau a masu tsaron nan dan ba zata iya ba , zuciyarta na iya bugawa
RAUDA ta dauke ajiyar zuciya ta juya zata mike wayar nan ta kuma daukan kara
Sai da ta dafe goshi dan abin ya ishe ta ita kam sannan ta daga , tun kafin ya yi magana ta ce" Ta fa tashi , ta shiga wanka fa ka bar kiran hakanan mana ai da sauki ko?"
YUSUF dake zaune a dakin mahaifinsa kansa na sarawa , domin su har sun fito daga masalaci, baki sun gama cika ko'ina, mutane ta ko'ina, abinda ya fi daga masa hankali magangannun dake yawo cewar shi YUSUF shine magajin garin kai tsaye , ba kwane kwane, a irin wannan lokacin da ake ciki ba'a san halin da mahaifinsa ke ciki ba kuwa ba za'a nadawa mahaifinsa sarauta ba, ba zai taba yiwuwa ba, bale uwa uba sarakai sun iso ba za'a taba dora masu tsarin da ba daidai yake da sarautar garin ba, hakan ya idasa rikita shi har ya rasa halin da yake ciki, sai gashi ana masa magana a sama sama ana fadin ya daina kiran mahaifiyarsa?
Wani irin Gwauron numfashi ya sauke, bai iya cewa komai ba, duk irin abinda yake bakinsa bai iya furta wa ba, ya sake kai dubansa kan mahaifinsa wanda yake gannin tamkar da gangan ya ki amsa shi, sai dai ba maganar gangan jikin mahaifinsa ya rikice tunda suka kawo shi suka kwontar, kirjinsa bugawa yake yi gashi dama yana da ciwon zuciya dan tun a lokacin da aka so hanna shi auren mahaifiyar Yusuf aka tabatar da ciwon zuciyarsa wanda idan abu ya dake shi yake zubar da shi, sai gashi jiya wani abin ya dake shi kai tsaye wanda YUSUF yake gannin bai masa adalci ba idan har ya ki amsa shi ya mike ya amshi sarautar shi cen ya karata da ita
Mikewa ya yi har kamar zai kifa ya fito falon gidan, nan ya samu matan mahaifinsa biyu, sunna ganninsa ya ga sun sada kawunansu, kuma har ya wuce basu dago ba, hakan ya sake daga masa hankali, kennan da abinda yake faruwa?
Yana fitowa babbar harabar masarautar mai filin gaske wace ta fara cika da mutane masu bin nan nasa suka kuma biyo shi, a birkice ya nufi bangaren Hajia, shi ba ya dakatar da su ba, shi ba ya dakatar da mai sanar da jana'izar Sarki karfe goma na safe, da kuma nadin sarauta *MAGAJIN MAGAJI?, KAN UBANCEN BABU WANDA YA ISA YA DORA MASA WANNAN RIKICIN, INA BA ZAI YIWU BA, BA ZAI TABA YIWUWA BA!*
A rikice ya shiga, ko salama bai iya yi da karfin da za'a ji shi ba sai ganninsa aka yi
Da sauri tsofafi da iyaye da tarin matan dake wajen suka ringa gaishe shi da girmamawar da ta dake bata masa rai sunna barin falon har ya zama daga Hajia sai NANA a falon sannan ya kalli mai biye da shi ya mashi alamun ya koma waje
Yana tafia ya karaso kan kujerar da Hajia ke zaune, cikin shigar hijab mai ruwan blue har kasa dan ya yi mata zubul da yawa har kafarta mai dauke da abin karayar a ciki ta rufe ruf hannunta rike da carbi tana ja hankalinta a kansa ya zuba mata ido a hankali ya kamo hannunta mai rike da carbin nan yana kallonta a tausashen da rabonta da ta ga ya yi mata magana a haka har ta manta ya ce" Dan Allah ki katse wannan rigimar ba zan iya ba, dan Allah ki rabani da wannan fitinar ba tafiyata bace, ki dora wanda kike so ama ba Ni ba, ku yi hakurin ya tashi , ciwon zuciyarsa ne ya tashi ba tsufa ya yi ba, ba kuma ciwon da zai hanna shi mulki bane, Hajia ba zan iya ba, bana so!"
Idannuwanta dake lumshe ta bude da sauri tamkar wace ta yi maye ta tsaida dubanta waje daya ta kasa furta koda A ne
A tausashen da yannayin yau ya haifar masa na rashin da suka yi da halin da mahaifinsa ke ciki da halin da kakarsa ke ciki ya ce" Ba zan iya fita daga inda nake a yanzu ba, ita kuma bata da lafiya, zaki iya zaunawa a gefenta ki rike wayar nan a kusa da ke, idan jikinta ya kiya ki sanar min?"
Yanzun kam ji ta yi ta gaza yin shirun, a dole ta budi baki tana kallon Mah ta ce" Yaya zan yi mata?, bata da lafiya fa"
Shima ya dauke numfashi a hankali ya ce" Addu'a zaki yi mata, zaki iya?"
Rauda ta ja numfashi a hankali ta ce" Zan iya in sha Allah"
Shiru ya yi na dan lokaci, kafin ya iya budar bakinsa kasa kasa sosai ya furta" JAZAKILAH"
Kalmar da ta sa RISLAN sake zuba masa ido har ya katse kiran ya maido da hankalinsa kansa
Hannu ya bashi suka yi nusabaha cikin alhinin rashin da ya zamo na su duka suka yiwa junna jaje a takaice sannan ya juya ya nufi ciki ba tare da ya karra koda kalma daya ba, sai a lokacin RISLAN ya juya ya koma wajen da mahaifiyarsa ta yi tamkar zuciyarta zata buga dan bakin ciki
Yana zuwa bata tsaya wata wata ba ta saka hannunta ta make gefen keyarsa rai bace ta ce" Haka ka zabarwa kanka? Yana tsaye kana jira tamkar uban gidanka? Ka fi shi nasaba dan a jikina ba dati!, idan har haka kake so ba damuwa ka je ka bi shi kamar kare da mai gidansa, ba daraja ba mutunci, yadda yake takamar yana da jinnin sarauta a jikinsa kaima haka, kuma kai ka fi shi duk wata daraja dan baka wulakantar da kanka ba!"
Kasa cewa komai RISLAN ya yi, kansa a kasa har ta gama fadan da bai san dalilinsa, fadan da baya so sam ace mahaifiyarsa ce ke yinsa, domin fada ne na rashin gaskiya, a gaban idannuwanta a dazun motocin wa'inda koda babu su baba BELLO a doron kasa kafin ya hau sai sun hau suka ringa shigowa, a irin wannan lokacin ya dace ne ace tana cen wajen Hajia an gama kimtsa wajen dan karbar bakin da tabas da yawa sun kamo hanya, ga wata rigimar da ta bilo ta rikicin sai an gurfanar da iyalan mamacin a kan rashin hankalin da suka yi na kin fadin rashin lafiyarsa, rikici dai kala kala wanda a tunaninsa a matsayinta Na mace daya a tsakaninsu zuwa yanzu tana cen tana neman mafitar da ta dace da su baki daya, sai ga wani gihitacen zance a bakinta? Allah ya yiwa wannan buri nata tsawa dan ya tabata zata jazawa kanta fitinar da ta fi karfin ta da su ƴaƴanta baki daya
Gaba daya shi ya wakilci mahaifinsa , hankalinsa ya rarabu gida uku, yana yi yana lekawa wajen mahaifinsa wa'inda matansa ke zagaye da shi hankalinsu tashe baki dayansu, domin babu wace zata so ace wani abu ya same shi daga nan zuwa safe dan bakin labarima irin wannan shine ace ɗan matar da suke yiwa wani gani gani ya haye karagar mulkin nan, kai wata har ta mutu a cikinsu domin abu ne da zai iya dukan zukatansu baki daya, hakan ya sa ba su ba, ba ƴaƴansu ba, kowane rike da carbi sunna masa addu'a kuma sunna jira karin ruwan da likita ya jona masa ya kare ko ya dawo cikin hayacinsa
Shi dinma wannan addu'a ita ta fi komai tsaye masa a zuciya, ba zai taba misalta halin da zai shiga ba idan muguwar Kadara ta biyo da shi ta hanyar nan, shi ya san ba zai taba yarda da wannan tatsuniyar ba, shi yasa hankalinsa gaba daya a tashe yake, sau uku yana dora hannunsa wajen kan mamacin nan a ransa yana rokon Allah, Allah ya sa ya ga alamun doguwar summa ce ya yi, haka kuma idan ya je wajen mahaifinsa ya duka daf da fuskarsa a sanyaye yakan ce" Abu, dan Allah ka rufa min asiri ka tashi, Abu rasuwar dan uwanka na san dole zata gigitaka, ama ka tashi ka ji? Ka tashi ka masa addu'a sannan ka hau mulkinka, Abu Ni din gaba dayana yaushe ka haife Ni? Dan Allah ka tashi kar zuciyata ta buga ka ji Abu?"
Idan ya mike ya fito har duhu duhu yake gani, ga wasu masu tsaron da Hajia ta karro da taimakon commisionan yan sanda da sarakan da suka isa tuni an zagaye masarautar haka kuma kiri kiri idan ya motsa sukan motsa ne da shi, abin har ya fara neman zautar da dukkan tunaninsa dan ba zai iya misalta wannan tashin hankalin a kansa ba, ina ba dai shi ba
Yakan kirayi RAUDA ne a dukkan motsinsa, tun tana amsa shi idannuwanta biyu, har barci ya dauketa a bayan Mah a kwonce bayan ta shinfida masu bargo sun kwonta a falon tana yi tana taba goshin Mah din da yi mata sannu har barci ya yi gaba da ita itama bai hakura ba, a cikin barcin take dagawa idannuwa a rufe ruf dan ta gaji sosai ta amsa shi sannan ta mayar da idannuwan ta rufe har aka fara kiraye kirayen sallar asubahi ta farka sakamakon farkawar da Mah ta yi suka yi ido hudu
Da sauri ta shiga lalaubar hijabinta a dan birkice ta ce" Hajia kin farka? Yaya jikin?"
Mah da ta jingina da jikin kujera ta sauke ajiyar zuciya tana kirkiro murmushi a tausashe ta ce" Ki daina ce min Hajia, ba zaki kirayeni da Mama ba? Ko bakya so na zama mamanki?"
Kafeta Rauda ta yi da ido ta kasa cewa komai, tana kallonta ta ciciba ta tashi ta nufi ciki dan yin wanka domin ta dauri niya sunna gama sallah zasu kama hanya zata ga ubanda zai hannata fita yau a masu tsaron nan dan ba zata iya ba , zuciyarta na iya bugawa
RAUDA ta dauke ajiyar zuciya ta juya zata mike wayar nan ta kuma daukan kara
Sai da ta dafe goshi dan abin ya ishe ta ita kam sannan ta daga , tun kafin ya yi magana ta ce" Ta fa tashi , ta shiga wanka fa ka bar kiran hakanan mana ai da sauki ko?"
YUSUF dake zaune a dakin mahaifinsa kansa na sarawa , domin su har sun fito daga masalaci, baki sun gama cika ko'ina, mutane ta ko'ina, abinda ya fi daga masa hankali magangannun dake yawo cewar shi YUSUF shine magajin garin kai tsaye , ba kwane kwane, a irin wannan lokacin da ake ciki ba'a san halin da mahaifinsa ke ciki ba kuwa ba za'a nadawa mahaifinsa sarauta ba, ba zai taba yiwuwa ba, bale uwa uba sarakai sun iso ba za'a taba dora masu tsarin da ba daidai yake da sarautar garin ba, hakan ya idasa rikita shi har ya rasa halin da yake ciki, sai gashi ana masa magana a sama sama ana fadin ya daina kiran mahaifiyarsa?
Wani irin Gwauron numfashi ya sauke, bai iya cewa komai ba, duk irin abinda yake bakinsa bai iya furta wa ba, ya sake kai dubansa kan mahaifinsa wanda yake gannin tamkar da gangan ya ki amsa shi, sai dai ba maganar gangan jikin mahaifinsa ya rikice tunda suka kawo shi suka kwontar, kirjinsa bugawa yake yi gashi dama yana da ciwon zuciya dan tun a lokacin da aka so hanna shi auren mahaifiyar Yusuf aka tabatar da ciwon zuciyarsa wanda idan abu ya dake shi yake zubar da shi, sai gashi jiya wani abin ya dake shi kai tsaye wanda YUSUF yake gannin bai masa adalci ba idan har ya ki amsa shi ya mike ya amshi sarautar shi cen ya karata da ita
Mikewa ya yi har kamar zai kifa ya fito falon gidan, nan ya samu matan mahaifinsa biyu, sunna ganninsa ya ga sun sada kawunansu, kuma har ya wuce basu dago ba, hakan ya sake daga masa hankali, kennan da abinda yake faruwa?
Yana fitowa babbar harabar masarautar mai filin gaske wace ta fara cika da mutane masu bin nan nasa suka kuma biyo shi, a birkice ya nufi bangaren Hajia, shi ba ya dakatar da su ba, shi ba ya dakatar da mai sanar da jana'izar Sarki karfe goma na safe, da kuma nadin sarauta *MAGAJIN MAGAJI?, KAN UBANCEN BABU WANDA YA ISA YA DORA MASA WANNAN RIKICIN, INA BA ZAI YIWU BA, BA ZAI TABA YIWUWA BA!*
A rikice ya shiga, ko salama bai iya yi da karfin da za'a ji shi ba sai ganninsa aka yi
Da sauri tsofafi da iyaye da tarin matan dake wajen suka ringa gaishe shi da girmamawar da ta dake bata masa rai sunna barin falon har ya zama daga Hajia sai NANA a falon sannan ya kalli mai biye da shi ya mashi alamun ya koma waje
Yana tafia ya karaso kan kujerar da Hajia ke zaune, cikin shigar hijab mai ruwan blue har kasa dan ya yi mata zubul da yawa har kafarta mai dauke da abin karayar a ciki ta rufe ruf hannunta rike da carbi tana ja hankalinta a kansa ya zuba mata ido a hankali ya kamo hannunta mai rike da carbin nan yana kallonta a tausashen da rabonta da ta ga ya yi mata magana a haka har ta manta ya ce" Dan Allah ki katse wannan rigimar ba zan iya ba, dan Allah ki rabani da wannan fitinar ba tafiyata bace, ki dora wanda kike so ama ba Ni ba, ku yi hakurin ya tashi , ciwon zuciyarsa ne ya tashi ba tsufa ya yi ba, ba kuma ciwon da zai hanna shi mulki bane, Hajia ba zan iya ba, bana so!"