Sashe 61
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
kasancewar da rana suka tarda shi bai samu zama da RAUDA ba sai da dare bayan sun ci abinci ta sake komawa wajensa, a lokacin ne ya dubeta cike da rauni ya ce"
cike da rauni uncle Umar ya ce" RAUDANA, my daughter, dan Allah ki yafe min, ki yafewa babanki, na dauko ki daga hannun wace ta yiwu da a wajenta kike da yanzun wata maganar ake yi ba irin tawa ba, har Allah ya amshi ranta ban bata dama ta baki tarbiyya da ilimi ba, ban san makarantar ki ta islamiyya ba ban san ta boko ba, sama sama idan na dan auna ne nakan kwatanta wasu kulawar da basu taka kara suka karya ba, maimakun na rike ki sai na karra maki rikon wani a kanki bayan ke dinma riko ce, sannan na hadaki zama da macen da sam bata da tausayi bale jin tsoron Allah a lamuranta, dan Allah ki yafe m..,....."
"Aba....." RAUDA ta fada a sanyaye, ba dan ta katse shi ba, kuma ba dan maganar da yake yi bata da mahinmanci ba, sai dan ba zata iya jin muryarsa a matsayinsa na uba a wajenta yana bata hakuri a kan yannayin zubin rayuwar da shi dinma ya yita ne yadda ta jirga shi, kwarai tana cikin yannayi, sai dai a yanzu kuma me ya rage mata na fitina? Allah ya gama wanke mutanen kirki daga cikin mutanensa na kirki ya hadata da su, sunna zaune tamkar y'ar da suka haifa da cikinsu, me kuma ya yi saura?
a sanyaye sosai ta ce" Dan Allah Aba ka daina bani hakuri, baka taba yi min laifi ba, koda ka min wanda ban sani ba na yafe maka duniya da kiyama ama ka daina bani hakuri, ni yanzun hankalina ya kwonta da Allah ya sa kana raye, ina fatan Allah ya karra tsare min kai a duk inda zaka shiga Aba"
hawayen da yake ta tarewa dole sai da suka zubar masa, ama kuma har cikin ransa sai ya ji sanyi sanyi na hakurin nan da ya bata, dan kuwa ko da ana azabtar da shi a hannun samarin nan da bashin giya ya haɗa su, adu'arsa daya ce a kulun, Allah ya sa ya samu ya ba marainiyar Allah hakuri kafin ya mutu, yana ta adu'ar Allah ya datar da shi da bata hakuri kafin ya koma ga mahaliccin sa, sai gashi Allah ya nuna masa , shi kam ba zai gaji da godewa wannan baiwan Allahn da ahalinsa ba, dama ya san shi farin sani, domin ya sha hanawa a dake shi idan wani abu ya hada shi rigima da wani a gidan giya, kun san gidan giya karamin yaro sai ya mare ka in ta hado ku, shi yasa yake karra tirrr da wannan rayuwa, ya je ya ga ukuba kala kala saboda yan kudaden da basu taka kara suka karya ba
da kula yana kallonta ya ce" Ama ban manta fadan da nake son yi ba, waye ya baki kudaden nan masu yawa?"
RAUDA ta sake sada kanta, dan kuwa ta san laifinta
a sanyaye ta ce" Aba, dama Abdallah ke min ire iren kyaututtukan nan, masu yawan gaske, da su nake kashe rikicin Mama wani lokacin dan ba kulun nake iya yiwa samarin dabara su bani kudin su ba tare da sun nuna min wata hanyar ba, walahi aba ban taba wulakantar da kaina ba, ban taba ba, ko nawa zaka gani a hannuna ba haramun bane, ban taba aikata wani aikin dan na samo kuɗi ba, Allah ya kare Ni sosai daga wannan halakar "
Aba ya sauke ajiyar zuciya yana yiwa Allah godiya a cikin ransa, a sanyaye kuma ya furta" Allah ya karra tsare ki, shi Abdallah din nan balaraben nan ko?, ya je wajena sau biyu"
RAUDA ta gyada kanta bata ce komai ba kanta a kasa
Aba ya ce" Sosai Bah din ku ya nuna min eh idan har ana iya bashi bashi da wata matsala da ta danganci mugun hali ko nasaba ko addini da za'a iya hanna masa, Ni kam na fada masa bani da damuwa in dai kina son shi Allah ya tabatar da alkhairi, shine akace to wai za'a saka nan da sati biyu, ana so kafin a maida Ni wajen neman lafiyar nan ace an daura ina nan, shin kina son shi? dan in har bakya son shi ba zan taba yarda na baki shi ba, domin ba zan so ki kuma shiga wata rayuwar kaka naka yi bayan wace kika yi a rayuwa RAUDA"
kanta na kasa ne, tana jin furucin Aba tamkar wanda yake yi mata yare da yaren da ba nata ba
sosai Hausar ke son yiwa zuciyarta nauyi, har ta dan dago tana kallonsa a raunane ta ce" Sati biyu kuma aba?"
Aba ya zuba mata ido yana kallon yannayinta, da kula ya ce" Eh sati biyu yar gidan Aba, akoy wani abin ne? "
RAUDA ta sada kanta, a hankali tana fitar da numfashi daga bakinta dan sai ta ji murar dake sandarta ta toshe mata hanci nan take
"RAUDAH?" Aba ya fada a tausashe yana sake kallonta
dagowa ta yi da dan sauri tana kallonsa, sannan ya amsa
"akoy wani abu dake damun ki ne da ya danganci auren nan?, idan har akoy shi ki sanar min domin kina da dama tun kafin wuri ya kure maki, domin shi aure daraja gare shi, kuma maganar nan manyan mutane ke cikinta, koda ke din abar so ce a duniyar su ba zasu yarda ki saka su magana biyu ko zubar da kima a wajen mutane ba, *SHIN KINA SON ABDALLAH KO BAKYA SON SA?*"
RAUDA ta yi saurin sadda kanta, a hankali ta furta" Aba ina son shi"
"KINA SON SHI?" ya sake yi mata tambayar da ta fi kayar mata da gaba fiye da komai, dan bata san me yasa tambayar ke yi mata wani iri ba, ko dan iyayenta ne ke yi mata ita? Sai kawai ta sake sinne kanta ta gyada kan nata cike da jin wani rauni da kunya da kuma sake yiwa kanta tambayar menene yasa take jin wani sensation daban a kan lamarin nan?
"alhamdulilah, Allah ya nuna mana, ya tabatar da alkhairi, to wai shi Abdul din karami haka yake da son dadi? kin ga Abdul harda turanceni?" Aba ya fada da yannayin barkwoncin da ya sakata yin dan murmushi, ama sam bata iya yin dariyar da abin ya dace ya sakata ba, karshe salamarta ya yi dan ya kula ta daina gane yarensa ta mike ta fito daga ɓangaren bakin da aka sauke shi ta shiga tafiya a hankali tana jin tamkar iska na son kayar da ita, bayan ita din masha ALLAH a yanke take sosai, da wahala iska ta yi mata watsawar kara in ba gagarumar iskar dake iya jijigar mota ba
tanfatsetsiyar wayarta, wace tun bayan kwana uku da bacewar Tata Mah ta bata cewar yayansu ya sa aka kawo mata daga shagonsa mai sunna ONLY IPHONE dake cikin gari, wayar da ta ninka Tata a tsada da kyau, ta kampanin iphone din ce da layi harda katin da har yau ta kasa cinyewa duk irin kale kalenta a wajen su youtube ne da instagram da su tiktok bata gama cinyewa ba dan masu nauyi ne
numbar ABDALLAH dake nunawa cewar shine ke kiranta ya sakata lumshe idannuwanta hawayen da suke mata zafi a ciki suka fita ta sauke ajiyar zuciya ta goge fuskarta sannan ya daga a nutse ta yi salama
"Angel, ina gidanku fa, ama ban shigo baban filin wajen MALIK ba, ina daga nan wajen masu tsaro na barin dama, kin ga dare ya yi ba za'a barni shiga da mota har cen ba, Ni kuwa kirjina ke min nauyi bana jin dadin jikina yau"
a hankali ta hadiye yawun dake makogwaronta sannan ta karasa wajen masu tsaron babar kofar yana jinta ta sanar masu su bar shi ya shigo, dan ya riga ya zo ba zai yiwu ta maida shi ba, gashi yace bashi da lafiya dole zata kula da shi
tana nan tsayen har ya karaso aka bude masa ya shigo da motarsa sannan ta karasa ta dan dora hannayenta ta leka kanta taana kallonsa ta ce" why kake son yawon dare tsakanin hanyar nan da bata da kyau kuma baka da lafiya?"
idannuwanta yake kallo yadda suka nuna alamun jika ya ce" Me zai hannani zuwa inda kike banda mutuwa? me zai hannani zuwa na ganki banda mutuwa? na zo na ga amaryana ne, wai kin san an bani ke? za'a tabatar min da ke nan da sati biyu idan ba mutuwa ce ta daukeni kafin lokacin ba?"
idannuwanta da suka yi yaushi ya dora masa, a sanyaye ta furta" Abdallah, kar ka daga min hankali"
murmushi ya yi yana kallonta ya ce" Kuka kika yi?"
da sauri ta dan zarro ido tana kallonsa ta ce" Kuka kuma?"
Kai ya gyada yana kallonta, sai ta yi murmushi ta girgiza kanta kasa kasa ta furta" Ka je gida Please, ka kular min da kanka"
"Sai idan kin min alkawarin zamu yi waya!"
ya fada yana turo baki, hakan ya sa ta yi yar dariya ta ce" Zamu yi waya da kai dan saurayina....."
yana dariya ya girgiza kai ya ce" Allah akoy maganar da bamu gama ba, kuma ke bakya son surutu ta waya, Please ki shigo"
a dole ta bude gaban motar ta shiga ta zauna tana sauraronsa
yana kallonta ya ce" Dangane da maganar yarinyar da na taba yi maki a lokacin da nake maroko ne, Angel kin ga na fada maki inada matsalar haihuwa, kin san da wannan ko? shine nake tsoron zamanmu ba yara na iya saka ki a damuwa, kin amince mu daukota?"
cike da rauni uncle Umar ya ce" RAUDANA, my daughter, dan Allah ki yafe min, ki yafewa babanki, na dauko ki daga hannun wace ta yiwu da a wajenta kike da yanzun wata maganar ake yi ba irin tawa ba, har Allah ya amshi ranta ban bata dama ta baki tarbiyya da ilimi ba, ban san makarantar ki ta islamiyya ba ban san ta boko ba, sama sama idan na dan auna ne nakan kwatanta wasu kulawar da basu taka kara suka karya ba, maimakun na rike ki sai na karra maki rikon wani a kanki bayan ke dinma riko ce, sannan na hadaki zama da macen da sam bata da tausayi bale jin tsoron Allah a lamuranta, dan Allah ki yafe m..,....."
"Aba....." RAUDA ta fada a sanyaye, ba dan ta katse shi ba, kuma ba dan maganar da yake yi bata da mahinmanci ba, sai dan ba zata iya jin muryarsa a matsayinsa na uba a wajenta yana bata hakuri a kan yannayin zubin rayuwar da shi dinma ya yita ne yadda ta jirga shi, kwarai tana cikin yannayi, sai dai a yanzu kuma me ya rage mata na fitina? Allah ya gama wanke mutanen kirki daga cikin mutanensa na kirki ya hadata da su, sunna zaune tamkar y'ar da suka haifa da cikinsu, me kuma ya yi saura?
a sanyaye sosai ta ce" Dan Allah Aba ka daina bani hakuri, baka taba yi min laifi ba, koda ka min wanda ban sani ba na yafe maka duniya da kiyama ama ka daina bani hakuri, ni yanzun hankalina ya kwonta da Allah ya sa kana raye, ina fatan Allah ya karra tsare min kai a duk inda zaka shiga Aba"
hawayen da yake ta tarewa dole sai da suka zubar masa, ama kuma har cikin ransa sai ya ji sanyi sanyi na hakurin nan da ya bata, dan kuwa ko da ana azabtar da shi a hannun samarin nan da bashin giya ya haɗa su, adu'arsa daya ce a kulun, Allah ya sa ya samu ya ba marainiyar Allah hakuri kafin ya mutu, yana ta adu'ar Allah ya datar da shi da bata hakuri kafin ya koma ga mahaliccin sa, sai gashi Allah ya nuna masa , shi kam ba zai gaji da godewa wannan baiwan Allahn da ahalinsa ba, dama ya san shi farin sani, domin ya sha hanawa a dake shi idan wani abu ya hada shi rigima da wani a gidan giya, kun san gidan giya karamin yaro sai ya mare ka in ta hado ku, shi yasa yake karra tirrr da wannan rayuwa, ya je ya ga ukuba kala kala saboda yan kudaden da basu taka kara suka karya ba
da kula yana kallonta ya ce" Ama ban manta fadan da nake son yi ba, waye ya baki kudaden nan masu yawa?"
RAUDA ta sake sada kanta, dan kuwa ta san laifinta
a sanyaye ta ce" Aba, dama Abdallah ke min ire iren kyaututtukan nan, masu yawan gaske, da su nake kashe rikicin Mama wani lokacin dan ba kulun nake iya yiwa samarin dabara su bani kudin su ba tare da sun nuna min wata hanyar ba, walahi aba ban taba wulakantar da kaina ba, ban taba ba, ko nawa zaka gani a hannuna ba haramun bane, ban taba aikata wani aikin dan na samo kuɗi ba, Allah ya kare Ni sosai daga wannan halakar "
Aba ya sauke ajiyar zuciya yana yiwa Allah godiya a cikin ransa, a sanyaye kuma ya furta" Allah ya karra tsare ki, shi Abdallah din nan balaraben nan ko?, ya je wajena sau biyu"
RAUDA ta gyada kanta bata ce komai ba kanta a kasa
Aba ya ce" Sosai Bah din ku ya nuna min eh idan har ana iya bashi bashi da wata matsala da ta danganci mugun hali ko nasaba ko addini da za'a iya hanna masa, Ni kam na fada masa bani da damuwa in dai kina son shi Allah ya tabatar da alkhairi, shine akace to wai za'a saka nan da sati biyu, ana so kafin a maida Ni wajen neman lafiyar nan ace an daura ina nan, shin kina son shi? dan in har bakya son shi ba zan taba yarda na baki shi ba, domin ba zan so ki kuma shiga wata rayuwar kaka naka yi bayan wace kika yi a rayuwa RAUDA"
kanta na kasa ne, tana jin furucin Aba tamkar wanda yake yi mata yare da yaren da ba nata ba
sosai Hausar ke son yiwa zuciyarta nauyi, har ta dan dago tana kallonsa a raunane ta ce" Sati biyu kuma aba?"
Aba ya zuba mata ido yana kallon yannayinta, da kula ya ce" Eh sati biyu yar gidan Aba, akoy wani abin ne? "
RAUDA ta sada kanta, a hankali tana fitar da numfashi daga bakinta dan sai ta ji murar dake sandarta ta toshe mata hanci nan take
"RAUDAH?" Aba ya fada a tausashe yana sake kallonta
dagowa ta yi da dan sauri tana kallonsa, sannan ya amsa
"akoy wani abu dake damun ki ne da ya danganci auren nan?, idan har akoy shi ki sanar min domin kina da dama tun kafin wuri ya kure maki, domin shi aure daraja gare shi, kuma maganar nan manyan mutane ke cikinta, koda ke din abar so ce a duniyar su ba zasu yarda ki saka su magana biyu ko zubar da kima a wajen mutane ba, *SHIN KINA SON ABDALLAH KO BAKYA SON SA?*"
RAUDA ta yi saurin sadda kanta, a hankali ta furta" Aba ina son shi"
"KINA SON SHI?" ya sake yi mata tambayar da ta fi kayar mata da gaba fiye da komai, dan bata san me yasa tambayar ke yi mata wani iri ba, ko dan iyayenta ne ke yi mata ita? Sai kawai ta sake sinne kanta ta gyada kan nata cike da jin wani rauni da kunya da kuma sake yiwa kanta tambayar menene yasa take jin wani sensation daban a kan lamarin nan?
"alhamdulilah, Allah ya nuna mana, ya tabatar da alkhairi, to wai shi Abdul din karami haka yake da son dadi? kin ga Abdul harda turanceni?" Aba ya fada da yannayin barkwoncin da ya sakata yin dan murmushi, ama sam bata iya yin dariyar da abin ya dace ya sakata ba, karshe salamarta ya yi dan ya kula ta daina gane yarensa ta mike ta fito daga ɓangaren bakin da aka sauke shi ta shiga tafiya a hankali tana jin tamkar iska na son kayar da ita, bayan ita din masha ALLAH a yanke take sosai, da wahala iska ta yi mata watsawar kara in ba gagarumar iskar dake iya jijigar mota ba
tanfatsetsiyar wayarta, wace tun bayan kwana uku da bacewar Tata Mah ta bata cewar yayansu ya sa aka kawo mata daga shagonsa mai sunna ONLY IPHONE dake cikin gari, wayar da ta ninka Tata a tsada da kyau, ta kampanin iphone din ce da layi harda katin da har yau ta kasa cinyewa duk irin kale kalenta a wajen su youtube ne da instagram da su tiktok bata gama cinyewa ba dan masu nauyi ne
numbar ABDALLAH dake nunawa cewar shine ke kiranta ya sakata lumshe idannuwanta hawayen da suke mata zafi a ciki suka fita ta sauke ajiyar zuciya ta goge fuskarta sannan ya daga a nutse ta yi salama
"Angel, ina gidanku fa, ama ban shigo baban filin wajen MALIK ba, ina daga nan wajen masu tsaro na barin dama, kin ga dare ya yi ba za'a barni shiga da mota har cen ba, Ni kuwa kirjina ke min nauyi bana jin dadin jikina yau"
a hankali ta hadiye yawun dake makogwaronta sannan ta karasa wajen masu tsaron babar kofar yana jinta ta sanar masu su bar shi ya shigo, dan ya riga ya zo ba zai yiwu ta maida shi ba, gashi yace bashi da lafiya dole zata kula da shi
tana nan tsayen har ya karaso aka bude masa ya shigo da motarsa sannan ta karasa ta dan dora hannayenta ta leka kanta taana kallonsa ta ce" why kake son yawon dare tsakanin hanyar nan da bata da kyau kuma baka da lafiya?"
idannuwanta yake kallo yadda suka nuna alamun jika ya ce" Me zai hannani zuwa inda kike banda mutuwa? me zai hannani zuwa na ganki banda mutuwa? na zo na ga amaryana ne, wai kin san an bani ke? za'a tabatar min da ke nan da sati biyu idan ba mutuwa ce ta daukeni kafin lokacin ba?"
idannuwanta da suka yi yaushi ya dora masa, a sanyaye ta furta" Abdallah, kar ka daga min hankali"
murmushi ya yi yana kallonta ya ce" Kuka kika yi?"
da sauri ta dan zarro ido tana kallonsa ta ce" Kuka kuma?"
Kai ya gyada yana kallonta, sai ta yi murmushi ta girgiza kanta kasa kasa ta furta" Ka je gida Please, ka kular min da kanka"
"Sai idan kin min alkawarin zamu yi waya!"
ya fada yana turo baki, hakan ya sa ta yi yar dariya ta ce" Zamu yi waya da kai dan saurayina....."
yana dariya ya girgiza kai ya ce" Allah akoy maganar da bamu gama ba, kuma ke bakya son surutu ta waya, Please ki shigo"
a dole ta bude gaban motar ta shiga ta zauna tana sauraronsa
yana kallonta ya ce" Dangane da maganar yarinyar da na taba yi maki a lokacin da nake maroko ne, Angel kin ga na fada maki inada matsalar haihuwa, kin san da wannan ko? shine nake tsoron zamanmu ba yara na iya saka ki a damuwa, kin amince mu daukota?"