← Book details Azal Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 117

Sashe 7

Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ita dai Atu wata Salama ta samu a cikin zuciyyarta, Duda yanzu suka gama hawa sama da faduwa da kanwar mahaifiyarta a kan RAUDA, Tati ta nunawa mahaifiyarta bata son kusancin Atun da RAUDA, wai yanzu duniya ta lalace , yaushe rabon duniya da ƙawance, har ta karɓe tarin suturun da Atu ta warewa Rauda zata bata tace ba za'a bata ba, duniya ta lalace ta daina tausayin kawar nan Tata tana iya son mata miji, ire iren abubuwan nan dai mararsa dadi, har sai da Atun ta fara kuka sannan ta kyaleta, dan ba zata iya ganewa ba, sam ba zata yarda da irin zumuncin dake tsakaninsu ba, amana daya ce, gamon jinni ne daga Allah, tunda *AZAL* ta fada ratuwarta RAUDA ta rufa mata asiri bata tunanin a nan duniya wani abu zai rudi Rauda ta wukakantata ba, wai ba maganar miji bane ake yi? Su auri miji daya har zuciyyarta ba zata yi bakin ciki ba, tana son RAUDA domin Allah kamar yadda itama take sonta

Bayan sallar isha i aka shiga hada haɗar tafiya da amarya

A cikin motar da aka dauko amaryar mutun uku ne kawai a ciki, amarya, gefenta auntynta kanwata mahaifiyarta sai RAUDA a dayan gefen tana rike da hannun amaryar sunna magana kasa kasa tana ta rarashin Atun kan ta daina kukan hakanan dan sun sha kuka tare har kamar zata kamu da ciwon kai

Anguwar jan gwarzo ne gidan Bara'atu, da yar tafia kafin ake isawa, motarsu na shiga gidan aka datse taron mutanen dake waje dan mutanen sun yi yawa sosai gashi an shigo da amaryar

A Nutse Teti cike da isa irin ta uwar amarya ta ce" Direba, bana son kowa a hanyar dakin yarinyata, idan na shiga da ita dan Allah a dakatar da kowa, bana so kowa ya shigo, idan nace kowa ina nufin kowa da kowa!"

A lokacin da take wannan bayanin RAUDA kadai ke jinta, ita Atun hankalinta na wajen mutanen dake tare tana mamakin karar da aka masu, yawanci kuma saboda RAUDA aka masu wannan karar

A hankali RAUDA ta dauke dubanta daga kan Teti, tana iya cewa ta jima da Sannin matar bata son zumuncinta da Bara'atu, Akoy lokutan da kiri kiri ta nuna bata son zumuncin nan nasu saboda yanzu ba'a kawar arziki, a lokacin ta daukewa Bara'atu kafa da gidansu sai da mahaifiyarta ta sameta da kanta ta mata fada ne suka koma kamar da, a kulun idan ta ga irin haka takan jadadawa ranta Adu'ar da take yi wace ta tabbata Allah ba zai kunyata mu'amalarsu ba domin saboda Allah take tare da ita, a yau in bata yi farin cikin ci gaban Atu ba , ba zata zamo mai bakin ciki ba, Atu itace yar uwar da ta rasa, itace wace take fadawa damuwarta ta yi kuka ta share nata hawaye

A hankali ta samu ta silibe daga cikin kawayen makarantar su har ta samu ta fito bakin baban titi cikin nutsuwa ta shiga takawa a kafarta, ba dan bata da abin hawa motar komawa gidansu ba, a'a sai dan fatanta Allah ya sa idan ta isa Mama ta yi barci Shikenan ba sai ta tisata da cin zarafin da ta saba ba

Tun kafin ta fito daga Anguwar su Atu, wato gidan da aka kawota aure wasu motoci biyu suka shawo kwanar masu shegen daukan ido da kyan gaske

Bata yi zato ba sai gani ta yi sun tsaya daf da ita, hakan ya sa ta dakata dole da tafiyar da take yi , tana kallon motar

A lokacin da madubin baya ya bude idannuwanta suka sauka a fuskar ango murmushi ya bayyana a fuskarta ta ce" Kar dai kace min har an rako ka?"

Shima cikin barkwoncin da suka saba da junna bayan ya roki amini kuma aboki a wajensa kan sai ya zo rakiyarsa har yana fadan kar ya tsayar da shi zai je gaisar da HAJIA yau , sai kace auren farko yace da shi eh lalle ba auren farko bane ama soyayar farko ce dan Allah ya raka shi, sai gashi kuma ya tsayar da su a bakin hanya wai ga aminiyar amarya ko me? Shi yasa ya gama cika fuskarsa ya zuba masa ido shima yana jira ya gama wulakancin su tafi
Dan murmushi ya yi ya ce" To yaya zan yi da raina aminiyar aminiyatah, ban gane ba har kin taho baki tsaya kin kwaci budar kan ba?"

Murmushi ta saki yanzunma, cikin tsarariyar sanyayar muryarta ta dan girgiza kai ta ce" Wannan ai ka san koda ban kwata yau ba bashi ne, bana so na yi dare ne na rasa abin hawa daga nan zuwa gidanmu"

Daya daga cikin abokan su dake gaba ne ya leko shima cikin shigar tasa gizner sai kanshi suke ya ce" A'a haba aminiyar aminiyar aminina kin san dai ba zamu bar tsaleliyar budurwa irinki neman abin hawa ba, me anfaninmu? Shigo Mu je idan muka ajiye shi da kaina zan kai abata nima gida ko?" Tunda suka fara kyarkyarar kamar yadda ya ambaci abinda suke yi a gaban karamar yarinyar da muryarta ya saka shi fasarata haka baima gane ta dazu da rana bace ransa ke kuna har sai da ya ji wani balagagen rashin da'a wai ta shigo su je ya saka shi kallon na gaban da duban hakan ba zata gyara ka ba sannan ya dan kalli angon kasa kasa ya furta" Bana son bata lokacin mu je mana"......ya karashe yana sauke idannuwansa a kan fuskarta a lokacin da itama ta kalli tasa fuskar dan sarai yannayin magana a kamilancen da jimula ta rashin mutunci ta mata kama da ta wanda yace a kore su dazu baya son surutu, ai kam tana sauke idannuwanta suka sauka a fuskarsa , kasancewarta mai baiwa irin ta ji ya saka abinda ya fada tsaf a cikin kunnayenta, har ya zamo a yanzu ta kasa hadiye yannayi na harara da watsarwa da idannuwanta suka dauko sannan ta kalli angon bayan yi murmushi kasa kasa sosai ta ce" Zan dawo ne, kar ka kakabe aljihun dan nawa bashi ne"

Daga haka ta juya ta mikar da tafiyarta dan gaba daya nunawa ta yi bata ji Yaren dayan abokin angon ba

"YUSEF Please kar ka fita mana" Elhaji ke fada yana kokarin Hanna shi fita a motar dan takaici su ya saka shi saka su tsayawa da nufin zai fice

Idannuwansa ya dan lumshe kasa kasa ya ce" Zan zo fa, ka ga zan je har wajen su Elhaji ne bana so na cika dare"

A dole Elhaji ya bar shi yana kallo har ya bude dayar motar ya shige baya, motar dake dauke da yan mata biyu , sai abokinsa da kuma direbansa suka dauki hanyar Fada

Ajiyar zuciya Elhajin ya sauke yana fatan ganin ranar da amininsa zai daina wasu halayan da suka zamo basu da anfani a duniyarsa, a matsayinsa da darajarsa sam basu kamaceshi ba, sai dai abinda za'a fasara ahalin nasu da shi menene , shin *AZAL* ya sauka a gidan nasu, ko karfin jinnin dake yawo a jikinsu ne ya jaza haka? Rayuwar dai gatanan kowa da tasa a boye, shine uban garin nasa ba boyaye bane tunda ba ubanda yake tsoro!

Asalamu alaikum jama'a....mun zo maku da nagartacen ingantaccen maganin Ulcer, magani ne na Hausa jikake wanda Dubai suka gwada suka ji dadinsa, nagartatun tsaftatatun itaciyoyin da suka bamu sasake masu anfani ne ake anfani da su, a nan jamhuriyar Nijar a garin Damagaran a farashi mai rahusa dubu biyu yan naija , yan nijer kuwa 1500francs mai bukata ga numbar +227 96897192 , HAJIA RAHAMA
🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶
*AZAL!*
🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶

*SAJIDA NIJAR*

*PAID BOOK*

_Bismillahir rahamanir-rahim._

*5*

*wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍*

*TALLAH, TALLAH, TALKAH*
_*TOH TO TO!*_
🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_
_Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_
Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake
_Amarya_Uwar gida_
_Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_
_Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_
INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼
🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI*
*🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU*
_KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_
_SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_
💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻*
💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI…
_MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_
*ADRESSE 94536935 94.53.69.35*
*Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER*
KARKU BARI A BAKU LABARI🥳

Litattafan marubuciyar
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Bak'a ce
Bani da zabi
Daga tafia daukar soja
Neman na kaina
Kutkale
Mage
Bani da zabi
Idan ka raina inda kake
Umughuluk itifal
Duk nisan jifa
Wata kokowar
Ni zan ladabi
Dakika biyar
Da ciwo a zuciyata
Aure yakin mata
Alkalamin Kadarata
Dutse
Daga tafiya daukar soja
Makauniyace
ND now *AZAL*

A lokacin da Rauda ta karasa gidansu dare ya tsala sosai, ama kofar gidan a bude take ham, hakan ya sa ta gane cewar Uncle dinta ya dawo gida yau

Ajiyar zuciya ta sauke a lokacin da ta ganshi zaune saman kujera yana kallon kofar shigowar

Karasawa ta yi inda yake zaunen tana dubansa da kula ta ce" Barka da warhaka Abu"
Chapter 7 · 0% Book details