Sashe 63
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"ka tabbata, dan kawai yarinyata ta je wajen mijin da zai aureta a cikin gidan nan ne ranka ya ɓaci haka, ko kuwa bacin ran maganar Hajia ce ta shafeta, ko akoy wani abin a kasa wanda ya dace na sani tunda wuri ko zan iya magance shi?" Bah ya fada bayan ya tsaya yana kallon YUSUF
YUSUF ya dago yana kallon BAH, a hankali dan yannayin da ciwon kan ya kama masa harda ido ya ce" abinda ta yanke ai na san dole zan yi biyayya, babu wani abun a kasa"
Bah ya sake zuba masa ido, sai kuma ya girgiza kai a tausashe ya ce" Ko menene , ya dace ka kula, ka san me yake kaika wannan makurar,, ban saba ganninka haka ba, baka iya fushi ba Son"
murmushi ya kakaro yana sake duban Bah a hankali ya furta" In sha Allah "
daga nan Bah ya juya ya fice dan sam ya ki bashi damar su yi firar nan, sai dai abinda ke cen cikin zuciyarsa na neman lalata farin cikin da yake ciki na firar da suka yi da matarsa, domin tunda ya shige ya zauna yana zayane mata abinda yake faruwa ya so bata hakuri da bakin cewar ba daga shi bane hukuncin zabawa YUSUF macen aure ta fari, kuma ta kwontar da hankalinta in sha Allah ya san Hajia zata zaba masa wace ta dace, sai ta hanna shi yin wannan ta nuna masa to meye a ciki dan Hajia ta zabar masa mace, ko shi bata tunanin idan zai bijire domin fadan da suke yi ba yana nufin baya son Hajia ba, YUSUF na son Hajia fiye da tunanin bawa, dan sabanin da suke samu kuwa ba shine zai dakusar da soyayar da yake yi mata ba
irin wannan halaya nata da suka karra siye zuciyarsa suka saka ya zamo baya iya daina sonta da kaunarta ne, a yanzunma ta gwada masa, shi ya san ita din mai karra ce, mai hakuri ce, mai biyayya ce, sai ga wani gagarumin abu dake iya rikita masu lissafi na neman kutso masu, ya Allah.....ka ƙaryata abinda nake zargi, domin idan har hakane ban san yaya zan iya kawar da kai ina kallo MALIK ya shiga wani halin ba, haka kuma ba zan so na yiwa y'ar mutane dole ba, ita din amana ce a wajena, abar a tausaya mata ce, itama y'a ce, tana da nata zabin kuma tana da ra'ayi, ya rab ko menene ka daidaita min cikin salama.......
da wannan ya je dakin Mah ya zauna saman kujera yana jiran dawowarta
BAH na nufar dakin YUSUF, MAH ta nufi na su Rauda da sauri dan yannayin da ta fice tana kuka sai da ya mugun daga mata hankali
A Lokacin da Mah ke kokarin shigewa bedroom dinsu ne ta ji Muryar Salima na fadin" Me yasa duk abinda ya shafi yayanmu ke mugun daga maki hankali, wani lokacin sai in ga abin bai kai ki yi irin kukan nan ba, sai na ga kin yi kuka kamar zaki sike, shin a nan menene abin kuka haka RAUDA?, haba RAUDA ta yiwu fa kin same shi ne a lokacin da yake cikin bacin rai shi yasa abin ya sauka kanki, ba wai dan ya tsane ki ba, RAUDA yaya za'a yi ya tsane ki kuma fisabililahi?"
ga mamakin Mah, duk irin abinda ke faruwa tana jira ta ji wata maganar ne daban, sai ta ji Muryar RAUDA a sanyaye sosai tana fadin" Salima, kin tabata bai tsane Ni ba?"
itama Salimar sai ta gaza gane komai, kawai ta yi sororo tana kallon Raudar har ta ajiye wayarta ta mike ta nufi bayi ɗan gannin Salima ta ki bata amsa ranta sai ya ringa sosuwa, haka kawai ta ringa jin bacin rai kala kala a cikin zuciyarta da tarin jin haushin Abdallah, ko saurin me yake mata da zai sa a mata aure yanzu yanzu, ita fa auren ne kansa take gannin bata wani shirya ba, to ta barwa Abdul wa yake nufi? lallema sam baya tunani shi kam!
(uhum, 🤔🤔🤔🤔1)
A hankali Mah ta juya ta ki shiga dakin ta nufi dakinta jikinta a mugun sanyaye
Tana shiga ta ga Bah zaune, da sauri ta karasa inda yake ta zauna daf da shi tana kamo hannayensa ta ce" Na shiga uku, ka san tare muka san su ko? Tun yaushe suka san junna? na shiga uku Bah, kar dai , kar dai, to ama kuma in har akoy wani abin tsakaninsu ai da an sani ko? ai ba zasu kyale har a saka aurenta ba ko? wayo Allahna, fushin nan na YUSUF ba banza ba, Ni kam ba banza ba!"
Bah ya sauke ajiyar zuciya a nutse ya ce" na yi iya yina ya nuna min ba komai , ban san wani iri bane YUSUF, Please ki tambayi y'arki cikin hikima, idan akoy wani abin su fada mana tunda wuri dan bana son a zo a hada min tunani, a yanzu ba lalle ne na iya bari wani abin ya rikita masa lissafi ba, sai in ya fi karfina!"
Mah ta dafe kai cike da zulumi, karshe dai daren nan wani iri suka kwana dan kowa da tarin tunani ya kwonta har kiraye kirayen sallar asubahi ta saka kowa ya kama gabansa dan gaisar da Ubangiji
kamar yadda ta saba zuwa gaishe da Mah tun da duhu duhu kadan hakan ne yauma ta je ta duka gaban Mah ta gaisheta
har zata mike Mah ta saka ta koma ta zauna, sai da Mah ta gama abinda take yi ta fuskanceta, da yannayin kula sosai ta ce" Baby, yauma zan sake yi maki tambayar da na maki sau uku a baya, dan ina son amsa ta karshe, domin hakin hakan a wuyuana yake, ki fada min, kina son ABDALLAH sosai zaki iya yin rayuwar aure da shi?"
RAUDA ta lumshe idannuwanta da suka yi mata nauyi, a hankali ta gyada kanta muryarta a raunane sosai ta furta" Eh Mah "
Mah ta tsura mata ido, haka kawai take ji a ranta abinda take fada ba gaskiyar abinda take son fada bane, sosai take son tambayarta da gaske ba komai tsakaninta da wanin bayan Abdallah, ama ta gaza, dan haka ta sauke ajiyar zuciya a sanyaye ta ce" Allah ya tabatar mana da alkhairi, daga yau mai gyara zata zo a fara gyara min y'ata in sha Allah, je ki huta kafin a jima zan kiraye ki mu shiga kicin mu fara girkin Larabawa"
Mikewa ta yi tsaye tana jin idannuwanta sun ciko da kwallah ta juya ta fice, Mah kuwa ta rakata da kallo tamkar tace ke zo nan, karya kike ki fada min gaskiya, sai dai ta gaza dan bata san yaya zata hau yarinyar da fada ba, bata iyawa, tana kaunarta tana jin tausayinta sosai a rayuwa
kasancewar coridor ne kafin a fito falo karami sannan a nufi wani corridor din a tafi dakin Salima ya sa take tafe a hankali har ta zo daf da fita daga corridor din ta ja da karfi , kirjinta na mahaukacin dokawa , a hankali ta sada kanta daga kallon tsararan rawanin dake zagaye da ni'imtaciyar fuskarsa , jikinsa dauke da manyan tufafi na dakarun sarakai, sarakai masu aji, sarakai masu ya'yan banki, suturarsu kadai abin girgiza zuciya ce bale idan Allah ya halice su da iza, da kwarjini, kallon su na hadasa danshi a ido da bugawar zuciya koda baka so ba, girmama su ya zame maka dole saboda Allah ne ya basu ba wani ba
kan da ta sada yake kallo, kafin ya bi yan yatsunta dake dauke da jan lalle da kallo
a hankali ya furta" Raudah......?"
Gabanta ya sake faduwa, ta dago dubanta a raunane ta saka cikin nasa
idannuwansa ya janye kadan daga cikin nata , kasa ya furta" Ya yi kyau"
jikinta ta ji ya fara rawa, tsigar jikinta na tashi, gumi na son wanke mata fuska, da sauri ta sada kanta dan ba zata iya duban idannuwansa ba
Sai dai bata tsira ba, domin dukar da kanta da ta yi ba shine ya rabata da shi ba, har sai da ta ji amon muryarsa wannan karron daf da ita ya sake furta" RAUDAH?"
"innalilahi Wa inna ilaihi raj'une..." ta fada a hankali saman lebenta kirjinta na bugawa da karfi
Sosai ya karanci abinda ta furta, ama bai sace masa gwuiwa ba, to shi meye kuma ya rage tace masa? wannan ai tabataciyar kalma ta maimaita dan tace daga Allah muke gareshi zamu koma, ta fa taba ce masa shedani har ta nemi tsari da shi fa ko? , a hankali ya hadiye yawun dake son busar masa da makogwaro kasa kasa ya furta" Nace ya yi kyau RAUDAH"
idannuwanta dake cike da kwallah ta dago ta saka cikin nasa, da karfi ta ja numfashi ta sauke sannan ta kausasa dubanta, da karfin ikon Allah ta sakar masa zazafan harara sannan ta ja baya ta yi tsaye hadi da dukar da kanta zuciyarta na tafarfasa, bata san me yasa ba, gani take yi babu wanda ya taba wulakantata irinsa, ita a yanzun gani take yi kamar baya jin tsoron Allah, ashe shi aurema zai yi nan da sati biyu? tirrrrr tirrrrr tirrrrr da wannan hali, tirrrrr da fitinanen hali, kuma tana tausayawa matar dan kuwa ta iya ganganci, aikin banza Allah ya sa a Daura masa hudu a tashi daya kowama ya huta, itafa dama tunda ta ga idannuwansa ta gane za'a yi biye biye a nan, shi yasa ta zabi auren Balarabe dan yanzu ko bahaushe ka shige tsaf zai maka kishiya, ita kuma ba zata taba zama da kishiya ba, bata so, bafa ta so, bata so!, aikin banza wai aure zai yi , hum!
YUSUF ya dago yana kallon BAH, a hankali dan yannayin da ciwon kan ya kama masa harda ido ya ce" abinda ta yanke ai na san dole zan yi biyayya, babu wani abun a kasa"
Bah ya sake zuba masa ido, sai kuma ya girgiza kai a tausashe ya ce" Ko menene , ya dace ka kula, ka san me yake kaika wannan makurar,, ban saba ganninka haka ba, baka iya fushi ba Son"
murmushi ya kakaro yana sake duban Bah a hankali ya furta" In sha Allah "
daga nan Bah ya juya ya fice dan sam ya ki bashi damar su yi firar nan, sai dai abinda ke cen cikin zuciyarsa na neman lalata farin cikin da yake ciki na firar da suka yi da matarsa, domin tunda ya shige ya zauna yana zayane mata abinda yake faruwa ya so bata hakuri da bakin cewar ba daga shi bane hukuncin zabawa YUSUF macen aure ta fari, kuma ta kwontar da hankalinta in sha Allah ya san Hajia zata zaba masa wace ta dace, sai ta hanna shi yin wannan ta nuna masa to meye a ciki dan Hajia ta zabar masa mace, ko shi bata tunanin idan zai bijire domin fadan da suke yi ba yana nufin baya son Hajia ba, YUSUF na son Hajia fiye da tunanin bawa, dan sabanin da suke samu kuwa ba shine zai dakusar da soyayar da yake yi mata ba
irin wannan halaya nata da suka karra siye zuciyarsa suka saka ya zamo baya iya daina sonta da kaunarta ne, a yanzunma ta gwada masa, shi ya san ita din mai karra ce, mai hakuri ce, mai biyayya ce, sai ga wani gagarumin abu dake iya rikita masu lissafi na neman kutso masu, ya Allah.....ka ƙaryata abinda nake zargi, domin idan har hakane ban san yaya zan iya kawar da kai ina kallo MALIK ya shiga wani halin ba, haka kuma ba zan so na yiwa y'ar mutane dole ba, ita din amana ce a wajena, abar a tausaya mata ce, itama y'a ce, tana da nata zabin kuma tana da ra'ayi, ya rab ko menene ka daidaita min cikin salama.......
da wannan ya je dakin Mah ya zauna saman kujera yana jiran dawowarta
BAH na nufar dakin YUSUF, MAH ta nufi na su Rauda da sauri dan yannayin da ta fice tana kuka sai da ya mugun daga mata hankali
A Lokacin da Mah ke kokarin shigewa bedroom dinsu ne ta ji Muryar Salima na fadin" Me yasa duk abinda ya shafi yayanmu ke mugun daga maki hankali, wani lokacin sai in ga abin bai kai ki yi irin kukan nan ba, sai na ga kin yi kuka kamar zaki sike, shin a nan menene abin kuka haka RAUDA?, haba RAUDA ta yiwu fa kin same shi ne a lokacin da yake cikin bacin rai shi yasa abin ya sauka kanki, ba wai dan ya tsane ki ba, RAUDA yaya za'a yi ya tsane ki kuma fisabililahi?"
ga mamakin Mah, duk irin abinda ke faruwa tana jira ta ji wata maganar ne daban, sai ta ji Muryar RAUDA a sanyaye sosai tana fadin" Salima, kin tabata bai tsane Ni ba?"
itama Salimar sai ta gaza gane komai, kawai ta yi sororo tana kallon Raudar har ta ajiye wayarta ta mike ta nufi bayi ɗan gannin Salima ta ki bata amsa ranta sai ya ringa sosuwa, haka kawai ta ringa jin bacin rai kala kala a cikin zuciyarta da tarin jin haushin Abdallah, ko saurin me yake mata da zai sa a mata aure yanzu yanzu, ita fa auren ne kansa take gannin bata wani shirya ba, to ta barwa Abdul wa yake nufi? lallema sam baya tunani shi kam!
(uhum, 🤔🤔🤔🤔1)
A hankali Mah ta juya ta ki shiga dakin ta nufi dakinta jikinta a mugun sanyaye
Tana shiga ta ga Bah zaune, da sauri ta karasa inda yake ta zauna daf da shi tana kamo hannayensa ta ce" Na shiga uku, ka san tare muka san su ko? Tun yaushe suka san junna? na shiga uku Bah, kar dai , kar dai, to ama kuma in har akoy wani abin tsakaninsu ai da an sani ko? ai ba zasu kyale har a saka aurenta ba ko? wayo Allahna, fushin nan na YUSUF ba banza ba, Ni kam ba banza ba!"
Bah ya sauke ajiyar zuciya a nutse ya ce" na yi iya yina ya nuna min ba komai , ban san wani iri bane YUSUF, Please ki tambayi y'arki cikin hikima, idan akoy wani abin su fada mana tunda wuri dan bana son a zo a hada min tunani, a yanzu ba lalle ne na iya bari wani abin ya rikita masa lissafi ba, sai in ya fi karfina!"
Mah ta dafe kai cike da zulumi, karshe dai daren nan wani iri suka kwana dan kowa da tarin tunani ya kwonta har kiraye kirayen sallar asubahi ta saka kowa ya kama gabansa dan gaisar da Ubangiji
kamar yadda ta saba zuwa gaishe da Mah tun da duhu duhu kadan hakan ne yauma ta je ta duka gaban Mah ta gaisheta
har zata mike Mah ta saka ta koma ta zauna, sai da Mah ta gama abinda take yi ta fuskanceta, da yannayin kula sosai ta ce" Baby, yauma zan sake yi maki tambayar da na maki sau uku a baya, dan ina son amsa ta karshe, domin hakin hakan a wuyuana yake, ki fada min, kina son ABDALLAH sosai zaki iya yin rayuwar aure da shi?"
RAUDA ta lumshe idannuwanta da suka yi mata nauyi, a hankali ta gyada kanta muryarta a raunane sosai ta furta" Eh Mah "
Mah ta tsura mata ido, haka kawai take ji a ranta abinda take fada ba gaskiyar abinda take son fada bane, sosai take son tambayarta da gaske ba komai tsakaninta da wanin bayan Abdallah, ama ta gaza, dan haka ta sauke ajiyar zuciya a sanyaye ta ce" Allah ya tabatar mana da alkhairi, daga yau mai gyara zata zo a fara gyara min y'ata in sha Allah, je ki huta kafin a jima zan kiraye ki mu shiga kicin mu fara girkin Larabawa"
Mikewa ta yi tsaye tana jin idannuwanta sun ciko da kwallah ta juya ta fice, Mah kuwa ta rakata da kallo tamkar tace ke zo nan, karya kike ki fada min gaskiya, sai dai ta gaza dan bata san yaya zata hau yarinyar da fada ba, bata iyawa, tana kaunarta tana jin tausayinta sosai a rayuwa
kasancewar coridor ne kafin a fito falo karami sannan a nufi wani corridor din a tafi dakin Salima ya sa take tafe a hankali har ta zo daf da fita daga corridor din ta ja da karfi , kirjinta na mahaukacin dokawa , a hankali ta sada kanta daga kallon tsararan rawanin dake zagaye da ni'imtaciyar fuskarsa , jikinsa dauke da manyan tufafi na dakarun sarakai, sarakai masu aji, sarakai masu ya'yan banki, suturarsu kadai abin girgiza zuciya ce bale idan Allah ya halice su da iza, da kwarjini, kallon su na hadasa danshi a ido da bugawar zuciya koda baka so ba, girmama su ya zame maka dole saboda Allah ne ya basu ba wani ba
kan da ta sada yake kallo, kafin ya bi yan yatsunta dake dauke da jan lalle da kallo
a hankali ya furta" Raudah......?"
Gabanta ya sake faduwa, ta dago dubanta a raunane ta saka cikin nasa
idannuwansa ya janye kadan daga cikin nata , kasa ya furta" Ya yi kyau"
jikinta ta ji ya fara rawa, tsigar jikinta na tashi, gumi na son wanke mata fuska, da sauri ta sada kanta dan ba zata iya duban idannuwansa ba
Sai dai bata tsira ba, domin dukar da kanta da ta yi ba shine ya rabata da shi ba, har sai da ta ji amon muryarsa wannan karron daf da ita ya sake furta" RAUDAH?"
"innalilahi Wa inna ilaihi raj'une..." ta fada a hankali saman lebenta kirjinta na bugawa da karfi
Sosai ya karanci abinda ta furta, ama bai sace masa gwuiwa ba, to shi meye kuma ya rage tace masa? wannan ai tabataciyar kalma ta maimaita dan tace daga Allah muke gareshi zamu koma, ta fa taba ce masa shedani har ta nemi tsari da shi fa ko? , a hankali ya hadiye yawun dake son busar masa da makogwaro kasa kasa ya furta" Nace ya yi kyau RAUDAH"
idannuwanta dake cike da kwallah ta dago ta saka cikin nasa, da karfi ta ja numfashi ta sauke sannan ta kausasa dubanta, da karfin ikon Allah ta sakar masa zazafan harara sannan ta ja baya ta yi tsaye hadi da dukar da kanta zuciyarta na tafarfasa, bata san me yasa ba, gani take yi babu wanda ya taba wulakantata irinsa, ita a yanzun gani take yi kamar baya jin tsoron Allah, ashe shi aurema zai yi nan da sati biyu? tirrrrr tirrrrr tirrrrr da wannan hali, tirrrrr da fitinanen hali, kuma tana tausayawa matar dan kuwa ta iya ganganci, aikin banza Allah ya sa a Daura masa hudu a tashi daya kowama ya huta, itafa dama tunda ta ga idannuwansa ta gane za'a yi biye biye a nan, shi yasa ta zabi auren Balarabe dan yanzu ko bahaushe ka shige tsaf zai maka kishiya, ita kuma ba zata taba zama da kishiya ba, bata so, bafa ta so, bata so!, aikin banza wai aure zai yi , hum!