Sashe 51
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiru ya yi yana zaunawa kusa da tarin kayan da suka sauka yau daga fadar SHAHEED ya kai hannunsa yana dan murza gaban goshinsa, ya ji Mah na fadin" RAUDA kuwa, ka san me yasa nake jinta har cikin raina? Yarinyar nan ta ga rayuwa, koda bata fito ta fadi dala dala ga irin abinda ta gani a rayuwa ba ina ji a jikina ta ga rayuwa, ka san wani lokacin mutun na koyan fada ne idan aka gama matse masa waje fa, son yakan koyo iya masifa ne dan ya kwaci kansa ba dan wani abu ba, ina gannin Rauda ta gama hardace rikicin duniya ta yadda ta koyi kwatar kanta, yau ko ba'a yi maka komai ba idan baka da uwa baka da uba a ringa tayaka da addu'a da rarashi son, ina son yarinyar har raina, ina so na ga rayuwarta ta samu cenji sosai .....ina fatan zaka taya Ni son ta"
Kwalayen agogon da yake dubawa yana mamakin SHAHEED ya dage kennan ko? Ya ajiye ya juyo wajen da Mah ke zaune ya dan zuba mata ido, sai kuma ya yi murmushi ya dauke dubansa ya ajiye ya taso ya dawo inda take zaune ya zauna a tausashe ya ce" Ko kare kike kiwo, zan Bashi abinci da wajen kwonciya, zan kula da shi sosai, bale mutun........, koda bayan su kinna son karo wasu ya'yan ki karro, in sha Allah ba zan rasa abin ciyar da su da tufatar da su ba , bale kin ga yannayin ginnin da za'a yi, kowace da wajenta, da dakunan ta da dukkan abin bukatarta, kina da damar sauke wanda kike so ya yi zaman da yake so a wajenki........."
Mah ta sauke ajiyar zuciya a tausashe ta furta" Allah ya tsare ka, ya yi maka albarka, Allah ya iya maka dukkan abinda ba zaka iya ba, ya baka mace ta gari .... YUSUF ba zaka taba wulakanta ba, domin ka faranta min , kuma ka faranta wa mahaifinka, laifukan da ka yiwa ubangijinka ka ci gaba da neman yafiyarsa, ka ringa kiyaye daukan alhakin mutun dan uwanka, in sha Allah idan ka kiyaye Wadinnan shikenan ba dai mutun ba sai dai Allah , dan a kulun ina maka fatan alkhairi da samun aljanna a wajen Ubangiji"
Idannuwansa ya lumshe yana jin abinda ke ratsa dukan gaban jikinsa, ya kai sau uku yana niyar zuwa ya ajiye rawanin nan kafin ya yarda ya rike, wannan baiwar Allahn kawai idan ya tuna sai ya rike ya ci gaba da rokon Allah alkhairinsa a kan zanen rubutun kundin kadararsa
"Malik?" Mah ta fada a tausashe
Idannuwansa ya bude yana kallonta hadi da sakar mata murmushi
Mah ta ce" Allah bana jin zan iya yafewa matar nan da ta dakar min y'a!"
Idannuwansa ya lumshe ya daga sosai daga dan gurfanawar da ya yi a kusan Mah ya zauna sosai sannan ya ce" Nima bana jin zan iya yafe mata"
Mah ta sake yi masa kwatankwacin kallon da ta yi masa a dazu da ya so ba RAUDA cofee din nan, da dan gagawa ta ce" Zaka saka a kamata ne ko? Zaka rufe ta ne ko?"
Kai ya girgiza yana kallon Mah
A tausashe ya ce" Bana tunanin matar nan wuni biyu ko uku a hannun iko zai sa ta saduda da rayuwa..........., ba zan kaita ofishin yan sanda ba, ama kuma ba zan kyaleta ba"
Mah ta dan zuba masa ido dan bata so yace zai dauki mataki da hannayensa, bale a yanzu ya dace ire irin abubuwan nan ya hakura da su , dan ana iya yi masa wata fasarar daban, ko magauta su samu hanyar cin masa ta haka"
Da kula sosai Mah ta ce" YUSUF, ka ga ina fada maka yanzu banda rigima ko? Shi yasa na dage kan dole a yi maka bayani a kan Shari'a, domin Shari'a abu ce mai girman gaske da abu kankani ke iya kai bawa ga halaka, ka yanke hukunci a kan mai laifi ko Ni ce, ka yiwa marar laifi adalci koda abokin gabarka ne, idan ka san wani abin zaka yi mata da bai dace ba gwara na barta da Allah ka ji?"
Murmushi ya yi , ya shiga saukowa Mah akwatunnan dake zube tari tari a saman gadonsa dauke da suturun wajen SHAHEED ya sanar mata sakon wajen SHAHEED ne aka kawo, nan fa Mah ta shiga murnar kayan da mamaki harda sakawa a yi mata kiransa dan ta yi godiya, da wannan ya bada mata zancen suka shige wani daban
A lokacin da su Mah suka fice a dakin nan RAUDA ta jima tana kallon kofin cofee din nan ba tare da ta san takamaiman abinda take tunani ba
Shigowar Musulima da Salima dauke da kayan karin kumalon da Mah ta saka a yi kowa ya karya , Musulima ta taya Salima daukowa dan kawai ta ga wai menene dalilin da ya sa har YUSUF ya dauko yarinyar nan , suka shigo da salama a bakunnansu, Salima na murmushi tana kallon RAUDA wace ta dago dara daram idannuwanta masu shige da jikakun idannuwa bayan basu da wata jikar hawaye haka yanayinsu yake , gasu a mugun mace , dama matatun idannuwa ne da ita,, kuma ciwon nan ya karra masu dan nauyi sai take kallo kamar na wace ta maku, wani kallo kasa kasa
Murmushin ta yi itama tana dauke dubanta daga kallon da Musulima ke yi mata wanda ya zarce misali
Da fara'a Salima ta furta" Alhamdulilah, jiki ya yi kyau, yaya jikin ko yar uwa?"
RAUDA ta yi murmushi tana amsar plate din da take miko mata ta furta" Alhamdulilah yar uwa, kuma sai kika barni kika gudu kika sa na hanna mamana barci ko?"
Salima na yar dariya ta zauna bakin gadon ta mika hannu dan daukan cofee din nan, sai ta ga Rauda ta rigayeta dauka, bayan ta dauka din sai kuma ta dan yi jim kamar zata maido mata , kuma sai ta fasa
Salima dai bata san komai ba dan haka ta yi maganarta tana fadin" Ai gwara da kika kwana a gefenta, da ba zata iya barci ba kwana zata yi tana kai kawo dakin cen da nan, ya baki sha cofee din ba? Har ya huce ko"
Murmushi RAUDA ta yi ta ciro cokalin dake ciki ta mika mata sannan ta shiga dan sha kadan kadan ta dago idannuwanta, da idannuwanta ta yiwa Musulima alamun yaya dai?
Sai a lokacin Musulima ta ankara da abinda yake faruwa, ta dauke fuskarta da sauri tana hade fuskar Tata ta nufi wajen ajiyewa ta ajiye ta juya ba tare da tace da ita yaya jikin ba kamar yadda ta cewa SALIMA, har sai da Salimar ta ankara ama bata ce komai ba, tana ba RAUDA dariyar Abdul , dan yana cen ana auna shi, kuma.da zarar ya karya za'a fita da shi boutique a zabo masa suturun da zai fara amfani da su
Kai RAUDAH ta sada, zuciyarta na tsintsinkewa, tana jin wata irin daraja da girman ahalin nan baki daya a zuciyarta
A hankali ta dago dubanta tana kallon Salima dake zaune itama ta bararaje tana ta yi mata labari
A sanyaye sosai ta furta " Na san a jiya kin cika da tunani da tambayoyi tun bayan tambayar da kika min a lokacin da muka kama hanyar gidanmu, na kasa baki amsa ko?.....kin san me yasa na kasa baki amsa?"
Salima ta tsareta da ido tana girgiza kanta a hankali
A nutse RAUDA ta ce" Dan na cika da zulumin abinda zaki tarar na rayuwata wanda ban cika budar baki na sanar ba sai idan Allah ya sa ka gani ko wani ya fada maka...., Salima abinda kike gani a jiya kadan ne daga abinda marikiyata tun ina yarinya take iya yi, dan Allah kar ki yi wani tunani a kaina, idan kin ga na yi abinda bai dace ba, na rikice ne dan na rasa tunanina a lokacin da na ga irin abinda ta yiwa Abdul bayan ta sato shi daga wajen da yake da gata ta kawo sun wulakanta, duk irin abinda nake yi dama dan ya tsira ne, dan na san Ni Babu abinda suka iya da Ni, ko ba komai zuwa yanzu na kai wajen da nake iya ja in ja da su baki daya....ama kina kallo suka dauko shi suka wulakanta min shi...."
Sai kawai hawaye suka bale mata, a hankali ta dauki tissu tana gogewa tana jin Muryar Salima da ta rike hannayenta tana kallonta tana fadin" Dan Allah ki yi hakuri, ki yi hakuri da abinda ta makiy tabas ta kasance mutun mai son kanta da kin jin tsoron Allah, kalaman ta kuwa sun yi tsaurin da ban san a wani bigiri zan ajiye su ba, tsabar jahilci ne ya sa ko kuwa rashin imani? Abinda na sani shine a yanzu daga ke har Abdul kun fi karfin ganninta bale har ta kai hannu jikin ku, ita kuwa ta yi jiran sakayar Ubangiji a kwana kusa !"
Ajiyar zuciya RAUDA ke saukewa a nutse ta furta" bi'izinillah kam, babu ita babu kuma cutar min da Abdul, dan kuwa idan na maida shi wajen inna sai na sa hukuma ta shiga tsakaninta da shi!"
"Gidan inna?, Wacece inna?" Salima ta fada tana kallon RAUDA
RAUDA ta ce" Kakarsa ce"
Salima ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Aya, bawan Allah, mahaifinsa baya kasar ko? Ashe kakarsa da rai? Masha ALLAH "
RAUDA ta gyada kanta a hankali tana dan murza yan yatsunta ta ce" Da ranta, mahaifiyarsa ma tana da rai, mahaifinsa kuwa shine uncle dina wanda ya rike Ni"
Da sauri Salima ta kalli RAUDA, sosai ta so yin magana ama ta kasa ta hanna kanta, ama a zuciyarta mamaki fal ya cika mata zuciya, wai dama Abdul ba d'an RAUDA bane?, ikon Allah ama sun shaku da junna kamar yaronta, kofa yake yadda take nunawa ne kowa zai yi tunanin ɗan nata ne, ama RAUDA akoy karfin hali da zuciyar tausayi, ta yiwu abinda ta gani saboda yaron ba kadan bane a rayuwa, sai ta ji ta sake shiga ranta da tausayinta sosai
Kwalayen agogon da yake dubawa yana mamakin SHAHEED ya dage kennan ko? Ya ajiye ya juyo wajen da Mah ke zaune ya dan zuba mata ido, sai kuma ya yi murmushi ya dauke dubansa ya ajiye ya taso ya dawo inda take zaune ya zauna a tausashe ya ce" Ko kare kike kiwo, zan Bashi abinci da wajen kwonciya, zan kula da shi sosai, bale mutun........, koda bayan su kinna son karo wasu ya'yan ki karro, in sha Allah ba zan rasa abin ciyar da su da tufatar da su ba , bale kin ga yannayin ginnin da za'a yi, kowace da wajenta, da dakunan ta da dukkan abin bukatarta, kina da damar sauke wanda kike so ya yi zaman da yake so a wajenki........."
Mah ta sauke ajiyar zuciya a tausashe ta furta" Allah ya tsare ka, ya yi maka albarka, Allah ya iya maka dukkan abinda ba zaka iya ba, ya baka mace ta gari .... YUSUF ba zaka taba wulakanta ba, domin ka faranta min , kuma ka faranta wa mahaifinka, laifukan da ka yiwa ubangijinka ka ci gaba da neman yafiyarsa, ka ringa kiyaye daukan alhakin mutun dan uwanka, in sha Allah idan ka kiyaye Wadinnan shikenan ba dai mutun ba sai dai Allah , dan a kulun ina maka fatan alkhairi da samun aljanna a wajen Ubangiji"
Idannuwansa ya lumshe yana jin abinda ke ratsa dukan gaban jikinsa, ya kai sau uku yana niyar zuwa ya ajiye rawanin nan kafin ya yarda ya rike, wannan baiwar Allahn kawai idan ya tuna sai ya rike ya ci gaba da rokon Allah alkhairinsa a kan zanen rubutun kundin kadararsa
"Malik?" Mah ta fada a tausashe
Idannuwansa ya bude yana kallonta hadi da sakar mata murmushi
Mah ta ce" Allah bana jin zan iya yafewa matar nan da ta dakar min y'a!"
Idannuwansa ya lumshe ya daga sosai daga dan gurfanawar da ya yi a kusan Mah ya zauna sosai sannan ya ce" Nima bana jin zan iya yafe mata"
Mah ta sake yi masa kwatankwacin kallon da ta yi masa a dazu da ya so ba RAUDA cofee din nan, da dan gagawa ta ce" Zaka saka a kamata ne ko? Zaka rufe ta ne ko?"
Kai ya girgiza yana kallon Mah
A tausashe ya ce" Bana tunanin matar nan wuni biyu ko uku a hannun iko zai sa ta saduda da rayuwa..........., ba zan kaita ofishin yan sanda ba, ama kuma ba zan kyaleta ba"
Mah ta dan zuba masa ido dan bata so yace zai dauki mataki da hannayensa, bale a yanzu ya dace ire irin abubuwan nan ya hakura da su , dan ana iya yi masa wata fasarar daban, ko magauta su samu hanyar cin masa ta haka"
Da kula sosai Mah ta ce" YUSUF, ka ga ina fada maka yanzu banda rigima ko? Shi yasa na dage kan dole a yi maka bayani a kan Shari'a, domin Shari'a abu ce mai girman gaske da abu kankani ke iya kai bawa ga halaka, ka yanke hukunci a kan mai laifi ko Ni ce, ka yiwa marar laifi adalci koda abokin gabarka ne, idan ka san wani abin zaka yi mata da bai dace ba gwara na barta da Allah ka ji?"
Murmushi ya yi , ya shiga saukowa Mah akwatunnan dake zube tari tari a saman gadonsa dauke da suturun wajen SHAHEED ya sanar mata sakon wajen SHAHEED ne aka kawo, nan fa Mah ta shiga murnar kayan da mamaki harda sakawa a yi mata kiransa dan ta yi godiya, da wannan ya bada mata zancen suka shige wani daban
A lokacin da su Mah suka fice a dakin nan RAUDA ta jima tana kallon kofin cofee din nan ba tare da ta san takamaiman abinda take tunani ba
Shigowar Musulima da Salima dauke da kayan karin kumalon da Mah ta saka a yi kowa ya karya , Musulima ta taya Salima daukowa dan kawai ta ga wai menene dalilin da ya sa har YUSUF ya dauko yarinyar nan , suka shigo da salama a bakunnansu, Salima na murmushi tana kallon RAUDA wace ta dago dara daram idannuwanta masu shige da jikakun idannuwa bayan basu da wata jikar hawaye haka yanayinsu yake , gasu a mugun mace , dama matatun idannuwa ne da ita,, kuma ciwon nan ya karra masu dan nauyi sai take kallo kamar na wace ta maku, wani kallo kasa kasa
Murmushin ta yi itama tana dauke dubanta daga kallon da Musulima ke yi mata wanda ya zarce misali
Da fara'a Salima ta furta" Alhamdulilah, jiki ya yi kyau, yaya jikin ko yar uwa?"
RAUDA ta yi murmushi tana amsar plate din da take miko mata ta furta" Alhamdulilah yar uwa, kuma sai kika barni kika gudu kika sa na hanna mamana barci ko?"
Salima na yar dariya ta zauna bakin gadon ta mika hannu dan daukan cofee din nan, sai ta ga Rauda ta rigayeta dauka, bayan ta dauka din sai kuma ta dan yi jim kamar zata maido mata , kuma sai ta fasa
Salima dai bata san komai ba dan haka ta yi maganarta tana fadin" Ai gwara da kika kwana a gefenta, da ba zata iya barci ba kwana zata yi tana kai kawo dakin cen da nan, ya baki sha cofee din ba? Har ya huce ko"
Murmushi RAUDA ta yi ta ciro cokalin dake ciki ta mika mata sannan ta shiga dan sha kadan kadan ta dago idannuwanta, da idannuwanta ta yiwa Musulima alamun yaya dai?
Sai a lokacin Musulima ta ankara da abinda yake faruwa, ta dauke fuskarta da sauri tana hade fuskar Tata ta nufi wajen ajiyewa ta ajiye ta juya ba tare da tace da ita yaya jikin ba kamar yadda ta cewa SALIMA, har sai da Salimar ta ankara ama bata ce komai ba, tana ba RAUDA dariyar Abdul , dan yana cen ana auna shi, kuma.da zarar ya karya za'a fita da shi boutique a zabo masa suturun da zai fara amfani da su
Kai RAUDAH ta sada, zuciyarta na tsintsinkewa, tana jin wata irin daraja da girman ahalin nan baki daya a zuciyarta
A hankali ta dago dubanta tana kallon Salima dake zaune itama ta bararaje tana ta yi mata labari
A sanyaye sosai ta furta " Na san a jiya kin cika da tunani da tambayoyi tun bayan tambayar da kika min a lokacin da muka kama hanyar gidanmu, na kasa baki amsa ko?.....kin san me yasa na kasa baki amsa?"
Salima ta tsareta da ido tana girgiza kanta a hankali
A nutse RAUDA ta ce" Dan na cika da zulumin abinda zaki tarar na rayuwata wanda ban cika budar baki na sanar ba sai idan Allah ya sa ka gani ko wani ya fada maka...., Salima abinda kike gani a jiya kadan ne daga abinda marikiyata tun ina yarinya take iya yi, dan Allah kar ki yi wani tunani a kaina, idan kin ga na yi abinda bai dace ba, na rikice ne dan na rasa tunanina a lokacin da na ga irin abinda ta yiwa Abdul bayan ta sato shi daga wajen da yake da gata ta kawo sun wulakanta, duk irin abinda nake yi dama dan ya tsira ne, dan na san Ni Babu abinda suka iya da Ni, ko ba komai zuwa yanzu na kai wajen da nake iya ja in ja da su baki daya....ama kina kallo suka dauko shi suka wulakanta min shi...."
Sai kawai hawaye suka bale mata, a hankali ta dauki tissu tana gogewa tana jin Muryar Salima da ta rike hannayenta tana kallonta tana fadin" Dan Allah ki yi hakuri, ki yi hakuri da abinda ta makiy tabas ta kasance mutun mai son kanta da kin jin tsoron Allah, kalaman ta kuwa sun yi tsaurin da ban san a wani bigiri zan ajiye su ba, tsabar jahilci ne ya sa ko kuwa rashin imani? Abinda na sani shine a yanzu daga ke har Abdul kun fi karfin ganninta bale har ta kai hannu jikin ku, ita kuwa ta yi jiran sakayar Ubangiji a kwana kusa !"
Ajiyar zuciya RAUDA ke saukewa a nutse ta furta" bi'izinillah kam, babu ita babu kuma cutar min da Abdul, dan kuwa idan na maida shi wajen inna sai na sa hukuma ta shiga tsakaninta da shi!"
"Gidan inna?, Wacece inna?" Salima ta fada tana kallon RAUDA
RAUDA ta ce" Kakarsa ce"
Salima ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Aya, bawan Allah, mahaifinsa baya kasar ko? Ashe kakarsa da rai? Masha ALLAH "
RAUDA ta gyada kanta a hankali tana dan murza yan yatsunta ta ce" Da ranta, mahaifiyarsa ma tana da rai, mahaifinsa kuwa shine uncle dina wanda ya rike Ni"
Da sauri Salima ta kalli RAUDA, sosai ta so yin magana ama ta kasa ta hanna kanta, ama a zuciyarta mamaki fal ya cika mata zuciya, wai dama Abdul ba d'an RAUDA bane?, ikon Allah ama sun shaku da junna kamar yaronta, kofa yake yadda take nunawa ne kowa zai yi tunanin ɗan nata ne, ama RAUDA akoy karfin hali da zuciyar tausayi, ta yiwu abinda ta gani saboda yaron ba kadan bane a rayuwa, sai ta ji ta sake shiga ranta da tausayinta sosai