Sashe 19
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A zaunen da yake mayafin Rauda ne a hannunsa yana dan gogawa a wajen hancinsa wanda shi da kansa bai san asalin turaren dake jiki yake shaka ba, shi dai ya rike yama manta na MEYE abin dai a hannunsa kamar nasa haka ya masa rikon gaske
Suturar dake jikinsa yake kallo har zuwa sarkar dake wuyansa yar siririya mai ruwan ash, ko karfe ce ko azurfa ce? Wa ya sani
Damatsunansa da suka shake a cikin rigar nan ya zubawa ido har zuwa ƙafarsa dake cikin takalmi kafa ciki ama ba mai nauyi ba
Agogon hannunsa ya zubawa ido da dayan hannunsa dake cikin na mahaifiyarsa a hankali yana kallonta tana ta labari yana murmushi
Murmushin ya samu kansa da saki yana dauke dubansa daga kansa
Abu daya ya sani shine da wahala YUSUF ya wulakanta a duniya, da wahala ya wulakanta saboda baya haɗa su da kowa, bai taba yarda ya haɗa soyayarsu da ta kowa, rabonsa da siyan shinkafar gidansa har ya manta, idan ya bada kudin cefane niya ya yi dan badangarci, ya jima da dauke masa hidimar kannensa, ya jima da fito da mahaifinsa cikin manyan kwarin kasa, domin a kasar Nijar baki daya a yanzu mutanen dake mu'amala da shi, shi da kansa ya san dan tsaya masan da yaronsa ya yi ne ba dan shi karfinsa ya kai cen ba, domin a yadda duniya ta zama idan kai ba kowa bane baka da fada a ji a gaban kowa hakan ne, shi BELLO yana da damar shiga inda ya ga dama a lokacin da ya ga dama idanma bashi da sanaya da mutumen da zarar ya fadawa YUSUF za'a neme shi ne yana zaune a saman gadonsa, lokuta da yawa shine ke yiwa sarki hanyar halartar wani taron , a yanzu dai a Nijar duk wani baba yana daukan mota ne a park din YUSUF, hakama a wasu kasashen makota, YUSUF ya mallaki park park da dama a garuruwa, kuma duk wata babbar mota yana yi mata nata daban ne, ya jima da shiga cikin duniyar bada kwongila a tsarin gwamnati, mutun ne mai nema ido rufe kuma a kulun habaka kasuwancinsa yake yi , ya ki ya matsa daga Damagaran da garin mahaifinsa ne saboda iyayensa,
A hankali mahaifinsa ya ringa jin wani abu mai kama da kunya da jin nauyi
Shin dan sun haife shi ne suke wulakanta shi haka?
Kwarai matarsa tana da gaskiya ya dace ya fara yiwa kansa wa'azi ya duba abinda yake ciki da yaronsa
Daren dai, shi bai samu rintsawa ba, domin YUSUF mahaifiyarsa na yin barci ya KWONTAR da kansa a saman gadon hannunsa cikin nata, dayan kuwa rike da mayafin Nan barci ya dauke shi, shi kuwa ya yi gadinsu har aka fara kiraye kirayen sallar asubahi
Farkawa YUSUF ya yi yana yin hama kadan hadi da son bude rinanun idannuwansa ya sauke dubansa cikin idannuwan mahaifiyarsa da kuma mahaifinsa dake daf da ita yana taba goshinta da wuyanta
Murmushi ta sakar masa, haka shima ya mike ya nufi bayi yana dan sake mikar da jikinsa dan jin du ya ririke
Kulawa ya yi da kansa ya dauro alwallah ya fito yana jin jikinsa du a ririke saboda rashin wanka da brush
Yana soke mayafin Nan a aljihunsa mahaifinsa ya karaso ya mika hannayensa yana cire masa sarkar nan dake wuyansa
Yana cireta ya saka a aljihunsa kasa kasa ya ce" Mu je masalaci"
Kallon fuskarsa yake yi da mamaki harda tunanin toh fa, sabon salo MEYE wannan din kuma? Ko dai shi din ma bashi da lafiyar?
Shi kuwa ya yi gaba yana boye yannayin da yaron nasa ya shiga a ransa suka ba Nurse din damar shiga ta taimakawa Mama ta yi wanka da alwallah da sallah , wace ta nuna yanzu kam zata iya jikinta ya warke ba sai an kamata ba, ama Duda haka likitar ta ki tafiya tana kula da ita har ta gama aka gama gyara dakin nata aka saka turare mai sanyin kanshi aka barta
A waje kuwa sunna gama sallar ya fito ya je wajen da Ishak ke tsaye da manyan ledoji dauke da kayan abinci da su fruits
Nuna masa ya yi ya bashi dan mahaifinsa na nan kuma baya so su dagawa mahaifiyarsa hankali a kan wannan
Jiki ba karfi Ishak ya bashi ledojin ya koma cikin motar da fatan samun lafiya wa mahaifiyar YUSUF din tare da fadin yanzu direbansa zai kawo masa motarsa da tufafinsa a ciki sannan ya tafi da ky din gidan a hannunsa
Yana juyowa ya ga Hon BELLO tsaye kofar asibitin yana kallonsa, zuwa lokacin haske ya fara yi sosai a garin
Fuska ya hade dan ya riga ya san yanzu zasu hau sama su fado, domin ya ga Ishak din da yake gudun ya gani
Yana isowa kunnayensa suka jiyo masa Muryar mahaifinsa yana fadin" Me yasa ya juya?"
Dakatawa ya yi yana kallon mahaifin nasa, ya sake kallonsa da kyau sai kuma ya dan dauke dubansa ya ce" Yana da uzuri ne"
Murmushi Hon ya yi ya mika hannayensa ya ce" Kawo na rage maka kayan"
Wannan karon kasa boyewa mamakinsa ya yi, har ya dan ja baya kadan yana kallonsa kafin ya ce" Me yake faruwa ne?"
Hon Bello ya zuba masa ido ya ce" A ina fa?"
YUSUF ya sauke ajiyar zuciya ya ce" Na ga yanzu Bama gabanta , kuma ka ci gaba da wani abin daban Abu"
Murmushi ya yi yana riko ledar dake dauke da jus ya ce" Bani Ni haba ya ina so in taya ka kana wani kiyawa"
Baki ya saki yana kallonsa, sai kuma a hankali ya ce" Ina son dibarwa wannan yarinyar da ta kwana a nan"
Yana fada ne yana nuna daidai dakin da RAUDA take, daidai lokacin ne kuma Raudar ke cikin fadan a cire mata abinda yake hannunta gida zata je, Aminu sai faman kwatanta mata yake yi ama ta nuna masa ta ji sauki gida take so
Samun kansa ya yi da nufar dakin ya murda ya shiga kai tsaye yana sauke dubansa a kan Aminu dake tsaye, da Nurse din dake tsayen itama rike da dan kwanon nan nasu na likitoci, sai RAUDA dake tsaye rike da abin gado sai luuuuuu take yiwa ido saboda abin magani ama fadi take yi gida zata je a salameta
"Me yake faruwa?" Ya iya furtawa bayan ya kare mata kallo ya juya yana kallon Nurse din da Aminu
Nurse din ta ce" Sir, zuwa na yi dan na cenza mata karin ruwan nan, na tarda ita ta farka shine tace ba za'a saka mata ba gida zata je yanzu yanzu"
YUSUF ya kalleta da dan mamaki a fuskarsa ya ce" Ke da baki da lafiya zaki tafi gida?"
Idannuwanta ta dauke daga fuskarsa tana saukewa kan Aminu, a raunane ta ce" Ina son gida Aminu, ta yiwa uncle a gida ya kwana yana nemana, Ni gida zan je!"
"Ki yi hakuri y'ata a cire maki sai a kaiki gidan, zauna a cire maki" Abu ya fada a tausashe yana karewa Rauda kallo da son karantar yannayinta
Ajiyar zuciya Rauda ta ringa saukewa ta zauna saman gadon, hakan ya sa sket dinta tatarewa sosai har kamar cinyarta dake fara sol zata bayyanar da kanta, duk kuwa yadda ta yi dan ta rufe jikinta hakan ya gagara sai kanta da ta sada kasa cike da jin kunya da takaicin zaratan mazan dake dakin a irin wannan lokacin jikinta na son bayana
Har dan dukawa Nurse din ta yi wajen amsa umarnin Hon ta karasa ta cirewa Rauda sannan ta saka abin goge jinnin nan ta goge mata ta danne mata da auduga
Da kula sosai Abu ya dubi Aminu, zuwa lokacin Yusuf ya fice ya nufi dakin mahaifiyarsa , ya ce" A me kuka zo ne?"
Aminu ya ce" Sir, ai da daidaitar tawa ce aka yi accident din, tana nan police station sun ce idan an gama fitar da sakamakon wanda bashi da gaskiya nima sai sun buga min takarda na biya diyyar yawo da ita ba awo, zamu tsayar da adaidaita ne"
Hon ya dan gyada kansa ya laluba aljihunsa ya ciro abin saka kudinsa ya ciro kudi masu dan kauri ya bashi da kula ya ce" Ku shiga ku je, sannan ka sanar min gidan su yarinyar zan zo da dare dan na basu hakuri na sanar masu hatsari ne kuka yi , Ni da YUSUF in sha Allah"
Sosai Aminu yake godiya, yana so ya nuna masa ba sai sun zo ba dan kar su ga wulakanci gurin Mama, sai dai ya kasa fadin hakan, Rauda kuwa a lokacin ta shiga wanke bakinta koda da bakin ruwa ne, dan ji take du a takure, Bama kamar jikinta ji take yi kamar kazantar duniya ta tare a kanta
Yana ficewa ta fito tana tambayar Aminu wayarta da mayafinta da pos dinta
Ya bata wayar da pos din, ama bai san inda mayafin yake ba, dan haka suka fice tana jinta wani iri duda a garin yan mata na fita ba mayafi, ba wani abin bane a garin
A cikin asibiti kuwa Abu na karasawa dakin ya samu YUSUF zaune yana ciyar da mahaifiyarsa wace take zaune itama ram da ita tana masa fira yana murmushi
Yana shigowa YUSUF din ya zuba masa ido, idannuwansa cike da yannayin son yin tambaya, ama ya gaza yin, shi kuwa Hon karantarsa ya yi tsaf sannan ya nemi waje ya zauna ya bude wani abincin da kula ya yi bismillah kafin ya kai bakinsa ya ce" To wai haka ake yiwa budurwa? Sai ka tafiyarka dan tana rigimar gidansu za'a kaita? Lalabasu fa ake yi ko su dagawa mutun hankali walahi"
Dan dakatawa ya yi da son kaiwa mamansa abincin a bakinta ya dan kallo mahaifinsa, kasa kasa ya ce" Ba budurwata bace"
"To ama kama sonta ko?" Ya katse shi da son lalle sai ya ja shi surutu
Suturar dake jikinsa yake kallo har zuwa sarkar dake wuyansa yar siririya mai ruwan ash, ko karfe ce ko azurfa ce? Wa ya sani
Damatsunansa da suka shake a cikin rigar nan ya zubawa ido har zuwa ƙafarsa dake cikin takalmi kafa ciki ama ba mai nauyi ba
Agogon hannunsa ya zubawa ido da dayan hannunsa dake cikin na mahaifiyarsa a hankali yana kallonta tana ta labari yana murmushi
Murmushin ya samu kansa da saki yana dauke dubansa daga kansa
Abu daya ya sani shine da wahala YUSUF ya wulakanta a duniya, da wahala ya wulakanta saboda baya haɗa su da kowa, bai taba yarda ya haɗa soyayarsu da ta kowa, rabonsa da siyan shinkafar gidansa har ya manta, idan ya bada kudin cefane niya ya yi dan badangarci, ya jima da dauke masa hidimar kannensa, ya jima da fito da mahaifinsa cikin manyan kwarin kasa, domin a kasar Nijar baki daya a yanzu mutanen dake mu'amala da shi, shi da kansa ya san dan tsaya masan da yaronsa ya yi ne ba dan shi karfinsa ya kai cen ba, domin a yadda duniya ta zama idan kai ba kowa bane baka da fada a ji a gaban kowa hakan ne, shi BELLO yana da damar shiga inda ya ga dama a lokacin da ya ga dama idanma bashi da sanaya da mutumen da zarar ya fadawa YUSUF za'a neme shi ne yana zaune a saman gadonsa, lokuta da yawa shine ke yiwa sarki hanyar halartar wani taron , a yanzu dai a Nijar duk wani baba yana daukan mota ne a park din YUSUF, hakama a wasu kasashen makota, YUSUF ya mallaki park park da dama a garuruwa, kuma duk wata babbar mota yana yi mata nata daban ne, ya jima da shiga cikin duniyar bada kwongila a tsarin gwamnati, mutun ne mai nema ido rufe kuma a kulun habaka kasuwancinsa yake yi , ya ki ya matsa daga Damagaran da garin mahaifinsa ne saboda iyayensa,
A hankali mahaifinsa ya ringa jin wani abu mai kama da kunya da jin nauyi
Shin dan sun haife shi ne suke wulakanta shi haka?
Kwarai matarsa tana da gaskiya ya dace ya fara yiwa kansa wa'azi ya duba abinda yake ciki da yaronsa
Daren dai, shi bai samu rintsawa ba, domin YUSUF mahaifiyarsa na yin barci ya KWONTAR da kansa a saman gadon hannunsa cikin nata, dayan kuwa rike da mayafin Nan barci ya dauke shi, shi kuwa ya yi gadinsu har aka fara kiraye kirayen sallar asubahi
Farkawa YUSUF ya yi yana yin hama kadan hadi da son bude rinanun idannuwansa ya sauke dubansa cikin idannuwan mahaifiyarsa da kuma mahaifinsa dake daf da ita yana taba goshinta da wuyanta
Murmushi ta sakar masa, haka shima ya mike ya nufi bayi yana dan sake mikar da jikinsa dan jin du ya ririke
Kulawa ya yi da kansa ya dauro alwallah ya fito yana jin jikinsa du a ririke saboda rashin wanka da brush
Yana soke mayafin Nan a aljihunsa mahaifinsa ya karaso ya mika hannayensa yana cire masa sarkar nan dake wuyansa
Yana cireta ya saka a aljihunsa kasa kasa ya ce" Mu je masalaci"
Kallon fuskarsa yake yi da mamaki harda tunanin toh fa, sabon salo MEYE wannan din kuma? Ko dai shi din ma bashi da lafiyar?
Shi kuwa ya yi gaba yana boye yannayin da yaron nasa ya shiga a ransa suka ba Nurse din damar shiga ta taimakawa Mama ta yi wanka da alwallah da sallah , wace ta nuna yanzu kam zata iya jikinta ya warke ba sai an kamata ba, ama Duda haka likitar ta ki tafiya tana kula da ita har ta gama aka gama gyara dakin nata aka saka turare mai sanyin kanshi aka barta
A waje kuwa sunna gama sallar ya fito ya je wajen da Ishak ke tsaye da manyan ledoji dauke da kayan abinci da su fruits
Nuna masa ya yi ya bashi dan mahaifinsa na nan kuma baya so su dagawa mahaifiyarsa hankali a kan wannan
Jiki ba karfi Ishak ya bashi ledojin ya koma cikin motar da fatan samun lafiya wa mahaifiyar YUSUF din tare da fadin yanzu direbansa zai kawo masa motarsa da tufafinsa a ciki sannan ya tafi da ky din gidan a hannunsa
Yana juyowa ya ga Hon BELLO tsaye kofar asibitin yana kallonsa, zuwa lokacin haske ya fara yi sosai a garin
Fuska ya hade dan ya riga ya san yanzu zasu hau sama su fado, domin ya ga Ishak din da yake gudun ya gani
Yana isowa kunnayensa suka jiyo masa Muryar mahaifinsa yana fadin" Me yasa ya juya?"
Dakatawa ya yi yana kallon mahaifin nasa, ya sake kallonsa da kyau sai kuma ya dan dauke dubansa ya ce" Yana da uzuri ne"
Murmushi Hon ya yi ya mika hannayensa ya ce" Kawo na rage maka kayan"
Wannan karon kasa boyewa mamakinsa ya yi, har ya dan ja baya kadan yana kallonsa kafin ya ce" Me yake faruwa ne?"
Hon Bello ya zuba masa ido ya ce" A ina fa?"
YUSUF ya sauke ajiyar zuciya ya ce" Na ga yanzu Bama gabanta , kuma ka ci gaba da wani abin daban Abu"
Murmushi ya yi yana riko ledar dake dauke da jus ya ce" Bani Ni haba ya ina so in taya ka kana wani kiyawa"
Baki ya saki yana kallonsa, sai kuma a hankali ya ce" Ina son dibarwa wannan yarinyar da ta kwana a nan"
Yana fada ne yana nuna daidai dakin da RAUDA take, daidai lokacin ne kuma Raudar ke cikin fadan a cire mata abinda yake hannunta gida zata je, Aminu sai faman kwatanta mata yake yi ama ta nuna masa ta ji sauki gida take so
Samun kansa ya yi da nufar dakin ya murda ya shiga kai tsaye yana sauke dubansa a kan Aminu dake tsaye, da Nurse din dake tsayen itama rike da dan kwanon nan nasu na likitoci, sai RAUDA dake tsaye rike da abin gado sai luuuuuu take yiwa ido saboda abin magani ama fadi take yi gida zata je a salameta
"Me yake faruwa?" Ya iya furtawa bayan ya kare mata kallo ya juya yana kallon Nurse din da Aminu
Nurse din ta ce" Sir, zuwa na yi dan na cenza mata karin ruwan nan, na tarda ita ta farka shine tace ba za'a saka mata ba gida zata je yanzu yanzu"
YUSUF ya kalleta da dan mamaki a fuskarsa ya ce" Ke da baki da lafiya zaki tafi gida?"
Idannuwanta ta dauke daga fuskarsa tana saukewa kan Aminu, a raunane ta ce" Ina son gida Aminu, ta yiwa uncle a gida ya kwana yana nemana, Ni gida zan je!"
"Ki yi hakuri y'ata a cire maki sai a kaiki gidan, zauna a cire maki" Abu ya fada a tausashe yana karewa Rauda kallo da son karantar yannayinta
Ajiyar zuciya Rauda ta ringa saukewa ta zauna saman gadon, hakan ya sa sket dinta tatarewa sosai har kamar cinyarta dake fara sol zata bayyanar da kanta, duk kuwa yadda ta yi dan ta rufe jikinta hakan ya gagara sai kanta da ta sada kasa cike da jin kunya da takaicin zaratan mazan dake dakin a irin wannan lokacin jikinta na son bayana
Har dan dukawa Nurse din ta yi wajen amsa umarnin Hon ta karasa ta cirewa Rauda sannan ta saka abin goge jinnin nan ta goge mata ta danne mata da auduga
Da kula sosai Abu ya dubi Aminu, zuwa lokacin Yusuf ya fice ya nufi dakin mahaifiyarsa , ya ce" A me kuka zo ne?"
Aminu ya ce" Sir, ai da daidaitar tawa ce aka yi accident din, tana nan police station sun ce idan an gama fitar da sakamakon wanda bashi da gaskiya nima sai sun buga min takarda na biya diyyar yawo da ita ba awo, zamu tsayar da adaidaita ne"
Hon ya dan gyada kansa ya laluba aljihunsa ya ciro abin saka kudinsa ya ciro kudi masu dan kauri ya bashi da kula ya ce" Ku shiga ku je, sannan ka sanar min gidan su yarinyar zan zo da dare dan na basu hakuri na sanar masu hatsari ne kuka yi , Ni da YUSUF in sha Allah"
Sosai Aminu yake godiya, yana so ya nuna masa ba sai sun zo ba dan kar su ga wulakanci gurin Mama, sai dai ya kasa fadin hakan, Rauda kuwa a lokacin ta shiga wanke bakinta koda da bakin ruwa ne, dan ji take du a takure, Bama kamar jikinta ji take yi kamar kazantar duniya ta tare a kanta
Yana ficewa ta fito tana tambayar Aminu wayarta da mayafinta da pos dinta
Ya bata wayar da pos din, ama bai san inda mayafin yake ba, dan haka suka fice tana jinta wani iri duda a garin yan mata na fita ba mayafi, ba wani abin bane a garin
A cikin asibiti kuwa Abu na karasawa dakin ya samu YUSUF zaune yana ciyar da mahaifiyarsa wace take zaune itama ram da ita tana masa fira yana murmushi
Yana shigowa YUSUF din ya zuba masa ido, idannuwansa cike da yannayin son yin tambaya, ama ya gaza yin, shi kuwa Hon karantarsa ya yi tsaf sannan ya nemi waje ya zauna ya bude wani abincin da kula ya yi bismillah kafin ya kai bakinsa ya ce" To wai haka ake yiwa budurwa? Sai ka tafiyarka dan tana rigimar gidansu za'a kaita? Lalabasu fa ake yi ko su dagawa mutun hankali walahi"
Dan dakatawa ya yi da son kaiwa mamansa abincin a bakinta ya dan kallo mahaifinsa, kasa kasa ya ce" Ba budurwata bace"
"To ama kama sonta ko?" Ya katse shi da son lalle sai ya ja shi surutu