Sashe 55
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mah ta yi murmushi , sosai ta so sai ta gama jansa a kasa kafin ya zo gidan nan, sai dai wani tunani da ta yi ya kashe mata gaban jiki har ya saka ta ba Rauda damar ta sanar masa ya zo bayan sallar Isha, dan ba zata so abinda ya sameta ya samu koda makiyinta ba, domin ba zata taba mantawa ba, mafarin abinda ya sa suka fara haduwa da mahaifin YUSUF a anguwa su yi fira dan an hanna masa damar zuwa zance gidansu, ance wai ba yanzu ba sai ta gama digiri dinta, duk yadda ta so su bata dama suka kiya,
Ajiyar zuciya ta sauke bayan RAUDA ta fita a hankali ta furta" BI IZINILLAH, DA ADDU'A, DA KIYAYE DOKOKIN ALLAH, ABINDA YA FARU DA NI BA ZAI FARU A CIKIN AHALINA BA, CIKI KUWA HARDA KE RAUDANA, ZAN SANARWA YUSUF IDAN YA SHIGO, ZAMU BASHI DAMA YA ZO SAU DAYA YA GAISHE MU SU DAN ZANTA KAFIN MU BASHI DAMA TA BIYU WACE ZATA BAMU DAMAR SANNIN WAYE SHI, SAI AURE......ALLAH YA TABATAR MANA DA ALKHAIRI"
RAUDA na komawa ta dauki wayar Salima ta kirayi numbar Abdallah
Ta yi ta ringing bai daga ba dan haka ta Bara masa sako, dan tana kyautata zaton yana barci ko yana wani abin da ya sa wayarsa bata kusa da shi
Karatun novel ta shiga yi , wanda ya kusan cinye mata lokacin dan sam bata jin barci, kuma nata jin ciwon kan, haka kuma ba barinta shiga kicin Mah zata yi ba, tunda su Abdul suka dawo da Salima ta bashi littafinsa na karatun addinin Musulunci suka fice sai ta nutsu a karatun littafi har sai da kiraye kirayen sallah suka sakata ajiyewa ta mike tana mamakin gudun lokacin ta nufi bayi
Bayan sun gama cin abinci Mah ta kiraye su gaba dayansu ta sanar masu tana so su shige kicin uku, sauran biyun kuwa su shiga gyaran falo baba da karami saboda MALIK zai yi baki , kuma RAUDA na da bako
Tunda Mah ta fadi RAUDA zata yi bako Musulima ta samu salama a zuciyarta, har ya zamto ta saki ranta da jikinta kamar sauran suka shiga hada hada, dan ta riga ta sani da ace akoy wani abin da take hasashe da wane mutun in ji mutuwa, bako ko na jinni ne ai sai an tantance in dai wando yake sakawa ba sket ba , saima ta samu kanta da yaba girkin da suke yi harda yannayin halittar Raudar a ranta, dan wani sahihin salihin kyau da Allah ya zuba mata mai sakawa a yaba mata koda ba'a so, domin tun daga kalar fatar jikinta har kirarta ta keru iya keruwa yan falo kuwa sunna cen sunna mopping da cenza su labulaye da bade gidan da turarukan wuta da na ruwa, ya zamo tun kusan magariba idan ka tunkaro falon sai dai kanshi ya yi maka maraba
Abinci kuwa manya manyan kuloli na alfarma ne ke jere saman table , kallonsu kadai zai iya baka sha'awar cin su
Ana kiraye kirayen sallar magaribar Mah ta umarce su kan su je su yi wanka su yi sallah su huta
Har sun juya zasu kama hanya Mah ta yi kiran RAUDA ta sanar mata saman gadon ta akoy abaya ta shirya da ita saboda bakonta
Cike da jin kunya ta wuce dakin na Mah ta dauko Abayar sannan ta debo turaran wuta saboda sabo da ta yi da anfani da shi ko a gidan uncle dinta, ta dawo ta shige dakin SALIMA ta zauna sunna fira da Salimar saboda yan matan da suka rigaye su kama bayin, ta karshe na fitowa Salima tace RAUDA ta shiga, itama tace a'a ta je ta fito sai ta shiga
Yau babu harare hararen nan nasu a tsakaninsu da ita, dama su suke yin abinsu ita sai dai ta kalle su ta yi murmushi bata taɓa kula haukansu ba, dan kuwa basa gabanta gaskiya kuma ko me suke takama da shi su suka gano ba ita ba
Abayar ta dora a saman kujera mai raga raga ta saka mata turaran wutar nan sannan ta dauko wandon ta irin na cikin nan ta dora da bra kafin ta shige wankan bayan SALIMA ta fito
Bata wani jima sosai a ciki ba ta fito ta shiga gabatar da sallarta, tana gamawa ta dora ta Isha domin an yi tuni
Cikin nutsuwa ta shiga shirya wa bayan ta sauko kayan gyaran fuskar SALIMA
Tana tsakar caje girarta SALIMA ta shigo, itama ta dandatsa lesh mai shegen kyau ta saka hijab a sama tana ta hidima da bakin da suka zo bayan an gama sallar Isha,
Wayar dake hannunta ta miko mata tana fadin" Kin san kuwa da ABDALLAH ya jima a falo karami? Har sun gaisa da Mah sun jima sunna fira , kiri kiri Mah tace a barshi ya yi jira wai, Ni dai na sanar maki dan Allah ki yi ki gama a zaune kike yanzu fisabililahi?"
Da mamaki RAUDA ta kalli agogon bangon dakin , sai ta ga ashe karfe tara ke neman yi, ikon Allah lokaci yana gudu yanzu, ama bayan ta gama sallah sai da ta yi su turaran wuta a jikinta da sauransu sannan ta zauna ta shiga tsara fuskarta kamar yadda ta saba, wato boyayiyar kwaliyar dake mahaukacin fito da fuskarta da baban sirrin dake saka maza haukacewa a kanta, domin ko kalar saka kwalin da take yi yana matukar tasiri wajen ladaftar da kallon cikin ido ta ce" kina nufin cikin aka shigo da shi?"
SALIMA ta zauna tana kallon yadda ta yiwa girarta sai mamaki ya kamata ta ce" dole zai shigo ciki kar ki manta mutumen da ake saka ran zamowa mijinki ne, wai dama kin iya mak'up?"
RAUDA da ta mike tana kallon call din na sake shigowa nasa ta karasa wajen tufafinta ta sauko su tana fadin" Mak'up sai an iya aunty Salima?, ka iya daidaita fuskarka ya wadatar ban fa shafa hoda ba"
Da sauri SALIMA ta mike jin ana kiranta za fice tana fadin" zamu zauna ne my kawa, Please ki yi ki fito na kai masa abinci ya ki ci"
Murmushi RAUDA ta yi ta shiga kimtsawa
Bayan ta saka Abayar ne ta warware gashin kanta ta caje shi bayanta, bata saka masa ribom na ta dauki dan kwalin Abayar ta bude shi ta dan ninka gabansa kadan ta daidaita shi sosai ta caka dauri irin na zahra Buhari ta ya fito sosai ya hau saman suturarta dan sai ta fito dasss da ita tamkar ka sace ta ka gudu
Turaran ruwa, irin mai kaurin nan, mai sansanyan kanshi ma Madina za bude ta shafa a jikinta sosai dan shi ba'a shafawa tufafi dan yana iya yin dan maski maski, shi ta shafa a matsayin mai domin bata cika son shafa mai ba,sannan ta dauko wayar wajen SALIMA ta nufi wajen kujerun da yan matan nan suke ta saka takalminta plate ta juya ta fice a dakin na tare da tace masu komai ba, ta bar idannuwansu da rakata da kallo har sai da suka kula da sun bita da kallo ne su dukansu sannan kowace ta dauke kanta
A nutse take takawa, kwarai kunnayenta na jiyo mata firar maza sama sama haka, kasancewar su maza in dai suka taru a waje to fa sai surutun nan ya cika waje komai wayewar su
Ita dai bata yi gigin bi ta baban falon ba tana murmushin Salima da ta taho dauke da butar shayi
Alamu ta yi mata da ta mahaukacin haduwa, sannan ta mata alamun zasu hade wai motocin MALIK sun karaso na zata iya tsayawa ba ya ritsata a tsaye
Ita kam sai ta rasa to ina zata nufa? Ta koma ne har ya shige ko kawai ta yi tafiyarta?
Tunawar da ta yi na lalle ya biyo ta wajen karamin falo na ya saka ta karasawa karamin falon , domin shi baban falon akoy hanyar shigarsa, shi yasa ta tafiyarta hankali kwonce tana kallon ABDALLAH, wanda hakan ya sa ta ji kamar hankalinta na neman tashi dan irin ramar da ta ga ya yi
A lokacin da take ta kokarin daidaita kanta tana gannin yadda ya wani zuba mata ido yana sauke mata murmushi mai ratsa zuciyar nan hannayensa bude dan kawai ya tsokaneta domin yakan yi mata haka sai ya bude hannayensa yace ta zo, ita kuma sai ta toge tace ta ki din sannan ta bi shi da harara, hakan na matukar saka shi nishadi
Hannayensa a bude, yana murmushi ya ce" zo jikina masoyiyatah...."
A lokacin da take shirin sakar masa harara gabanta ya kwonci kwonci ya fadi, sakamakon shigowar da MALIKI YUSUF BINE BELLO ya yi, kuma idannuwansa tsai a kansu, kallo irin ya kalli Abdallah wanda ganninsa ya saka shi fadada fuskarsa da murmushi ya mike tsaye dan girmamawa a gare shi, domin dama sun san junna yana siyan manyan motoci a wajensa sai dai basu da wata mu'amala ta kusa da kusa , ko siyan motar wata mota ce da ya so sosai shi kuwa ya ki saidawa sai Honorable ya saka baki ya saida masa ita.........
A hankali YUSUF ya dan so lumshe idannuwansa, sai dai wani irin zafi da sukar da suka masa ya hanna shi abinda ya yi niya har ya sake bude su tarrrr a saman fuskarta da ta nuna alamun damuwar da bata san ko ta meye ba har ta dan dago da sauri zata yi magana ta ga ya kauce fuskarsa daga barinta ya maida wajen ABDALLAH da sam bai san abinda yake faruwa ba domin hannu ne ya miko masa dan su yi musabaha
Idannuwansa ya lumshe a hankali bayan ya kalli fuskarsa, a nutse ya .........
Happy juma'at
Azl 31
*Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina*
Bismillahi rahamanin rahim
Ajiyar zuciya ta sauke bayan RAUDA ta fita a hankali ta furta" BI IZINILLAH, DA ADDU'A, DA KIYAYE DOKOKIN ALLAH, ABINDA YA FARU DA NI BA ZAI FARU A CIKIN AHALINA BA, CIKI KUWA HARDA KE RAUDANA, ZAN SANARWA YUSUF IDAN YA SHIGO, ZAMU BASHI DAMA YA ZO SAU DAYA YA GAISHE MU SU DAN ZANTA KAFIN MU BASHI DAMA TA BIYU WACE ZATA BAMU DAMAR SANNIN WAYE SHI, SAI AURE......ALLAH YA TABATAR MANA DA ALKHAIRI"
RAUDA na komawa ta dauki wayar Salima ta kirayi numbar Abdallah
Ta yi ta ringing bai daga ba dan haka ta Bara masa sako, dan tana kyautata zaton yana barci ko yana wani abin da ya sa wayarsa bata kusa da shi
Karatun novel ta shiga yi , wanda ya kusan cinye mata lokacin dan sam bata jin barci, kuma nata jin ciwon kan, haka kuma ba barinta shiga kicin Mah zata yi ba, tunda su Abdul suka dawo da Salima ta bashi littafinsa na karatun addinin Musulunci suka fice sai ta nutsu a karatun littafi har sai da kiraye kirayen sallah suka sakata ajiyewa ta mike tana mamakin gudun lokacin ta nufi bayi
Bayan sun gama cin abinci Mah ta kiraye su gaba dayansu ta sanar masu tana so su shige kicin uku, sauran biyun kuwa su shiga gyaran falo baba da karami saboda MALIK zai yi baki , kuma RAUDA na da bako
Tunda Mah ta fadi RAUDA zata yi bako Musulima ta samu salama a zuciyarta, har ya zamto ta saki ranta da jikinta kamar sauran suka shiga hada hada, dan ta riga ta sani da ace akoy wani abin da take hasashe da wane mutun in ji mutuwa, bako ko na jinni ne ai sai an tantance in dai wando yake sakawa ba sket ba , saima ta samu kanta da yaba girkin da suke yi harda yannayin halittar Raudar a ranta, dan wani sahihin salihin kyau da Allah ya zuba mata mai sakawa a yaba mata koda ba'a so, domin tun daga kalar fatar jikinta har kirarta ta keru iya keruwa yan falo kuwa sunna cen sunna mopping da cenza su labulaye da bade gidan da turarukan wuta da na ruwa, ya zamo tun kusan magariba idan ka tunkaro falon sai dai kanshi ya yi maka maraba
Abinci kuwa manya manyan kuloli na alfarma ne ke jere saman table , kallonsu kadai zai iya baka sha'awar cin su
Ana kiraye kirayen sallar magaribar Mah ta umarce su kan su je su yi wanka su yi sallah su huta
Har sun juya zasu kama hanya Mah ta yi kiran RAUDA ta sanar mata saman gadon ta akoy abaya ta shirya da ita saboda bakonta
Cike da jin kunya ta wuce dakin na Mah ta dauko Abayar sannan ta debo turaran wuta saboda sabo da ta yi da anfani da shi ko a gidan uncle dinta, ta dawo ta shige dakin SALIMA ta zauna sunna fira da Salimar saboda yan matan da suka rigaye su kama bayin, ta karshe na fitowa Salima tace RAUDA ta shiga, itama tace a'a ta je ta fito sai ta shiga
Yau babu harare hararen nan nasu a tsakaninsu da ita, dama su suke yin abinsu ita sai dai ta kalle su ta yi murmushi bata taɓa kula haukansu ba, dan kuwa basa gabanta gaskiya kuma ko me suke takama da shi su suka gano ba ita ba
Abayar ta dora a saman kujera mai raga raga ta saka mata turaran wutar nan sannan ta dauko wandon ta irin na cikin nan ta dora da bra kafin ta shige wankan bayan SALIMA ta fito
Bata wani jima sosai a ciki ba ta fito ta shiga gabatar da sallarta, tana gamawa ta dora ta Isha domin an yi tuni
Cikin nutsuwa ta shiga shirya wa bayan ta sauko kayan gyaran fuskar SALIMA
Tana tsakar caje girarta SALIMA ta shigo, itama ta dandatsa lesh mai shegen kyau ta saka hijab a sama tana ta hidima da bakin da suka zo bayan an gama sallar Isha,
Wayar dake hannunta ta miko mata tana fadin" Kin san kuwa da ABDALLAH ya jima a falo karami? Har sun gaisa da Mah sun jima sunna fira , kiri kiri Mah tace a barshi ya yi jira wai, Ni dai na sanar maki dan Allah ki yi ki gama a zaune kike yanzu fisabililahi?"
Da mamaki RAUDA ta kalli agogon bangon dakin , sai ta ga ashe karfe tara ke neman yi, ikon Allah lokaci yana gudu yanzu, ama bayan ta gama sallah sai da ta yi su turaran wuta a jikinta da sauransu sannan ta zauna ta shiga tsara fuskarta kamar yadda ta saba, wato boyayiyar kwaliyar dake mahaukacin fito da fuskarta da baban sirrin dake saka maza haukacewa a kanta, domin ko kalar saka kwalin da take yi yana matukar tasiri wajen ladaftar da kallon cikin ido ta ce" kina nufin cikin aka shigo da shi?"
SALIMA ta zauna tana kallon yadda ta yiwa girarta sai mamaki ya kamata ta ce" dole zai shigo ciki kar ki manta mutumen da ake saka ran zamowa mijinki ne, wai dama kin iya mak'up?"
RAUDA da ta mike tana kallon call din na sake shigowa nasa ta karasa wajen tufafinta ta sauko su tana fadin" Mak'up sai an iya aunty Salima?, ka iya daidaita fuskarka ya wadatar ban fa shafa hoda ba"
Da sauri SALIMA ta mike jin ana kiranta za fice tana fadin" zamu zauna ne my kawa, Please ki yi ki fito na kai masa abinci ya ki ci"
Murmushi RAUDA ta yi ta shiga kimtsawa
Bayan ta saka Abayar ne ta warware gashin kanta ta caje shi bayanta, bata saka masa ribom na ta dauki dan kwalin Abayar ta bude shi ta dan ninka gabansa kadan ta daidaita shi sosai ta caka dauri irin na zahra Buhari ta ya fito sosai ya hau saman suturarta dan sai ta fito dasss da ita tamkar ka sace ta ka gudu
Turaran ruwa, irin mai kaurin nan, mai sansanyan kanshi ma Madina za bude ta shafa a jikinta sosai dan shi ba'a shafawa tufafi dan yana iya yin dan maski maski, shi ta shafa a matsayin mai domin bata cika son shafa mai ba,sannan ta dauko wayar wajen SALIMA ta nufi wajen kujerun da yan matan nan suke ta saka takalminta plate ta juya ta fice a dakin na tare da tace masu komai ba, ta bar idannuwansu da rakata da kallo har sai da suka kula da sun bita da kallo ne su dukansu sannan kowace ta dauke kanta
A nutse take takawa, kwarai kunnayenta na jiyo mata firar maza sama sama haka, kasancewar su maza in dai suka taru a waje to fa sai surutun nan ya cika waje komai wayewar su
Ita dai bata yi gigin bi ta baban falon ba tana murmushin Salima da ta taho dauke da butar shayi
Alamu ta yi mata da ta mahaukacin haduwa, sannan ta mata alamun zasu hade wai motocin MALIK sun karaso na zata iya tsayawa ba ya ritsata a tsaye
Ita kam sai ta rasa to ina zata nufa? Ta koma ne har ya shige ko kawai ta yi tafiyarta?
Tunawar da ta yi na lalle ya biyo ta wajen karamin falo na ya saka ta karasawa karamin falon , domin shi baban falon akoy hanyar shigarsa, shi yasa ta tafiyarta hankali kwonce tana kallon ABDALLAH, wanda hakan ya sa ta ji kamar hankalinta na neman tashi dan irin ramar da ta ga ya yi
A lokacin da take ta kokarin daidaita kanta tana gannin yadda ya wani zuba mata ido yana sauke mata murmushi mai ratsa zuciyar nan hannayensa bude dan kawai ya tsokaneta domin yakan yi mata haka sai ya bude hannayensa yace ta zo, ita kuma sai ta toge tace ta ki din sannan ta bi shi da harara, hakan na matukar saka shi nishadi
Hannayensa a bude, yana murmushi ya ce" zo jikina masoyiyatah...."
A lokacin da take shirin sakar masa harara gabanta ya kwonci kwonci ya fadi, sakamakon shigowar da MALIKI YUSUF BINE BELLO ya yi, kuma idannuwansa tsai a kansu, kallo irin ya kalli Abdallah wanda ganninsa ya saka shi fadada fuskarsa da murmushi ya mike tsaye dan girmamawa a gare shi, domin dama sun san junna yana siyan manyan motoci a wajensa sai dai basu da wata mu'amala ta kusa da kusa , ko siyan motar wata mota ce da ya so sosai shi kuwa ya ki saidawa sai Honorable ya saka baki ya saida masa ita.........
A hankali YUSUF ya dan so lumshe idannuwansa, sai dai wani irin zafi da sukar da suka masa ya hanna shi abinda ya yi niya har ya sake bude su tarrrr a saman fuskarta da ta nuna alamun damuwar da bata san ko ta meye ba har ta dan dago da sauri zata yi magana ta ga ya kauce fuskarsa daga barinta ya maida wajen ABDALLAH da sam bai san abinda yake faruwa ba domin hannu ne ya miko masa dan su yi musabaha
Idannuwansa ya lumshe a hankali bayan ya kalli fuskarsa, a nutse ya .........
Happy juma'at
Azl 31
*Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina*
Bismillahi rahamanin rahim