Sashe 35
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mah kam ta yi Wunin nan gaba daya tare da mijinta
Ita har ga Allah ta zata kawai Herde ta yi tafiyarta ne, hakan ya sa bata wani leko ba, bata damu da nema masu abinci, bata san wainar da suke toya mata ta wuce tunanin bawa, domin kiri kiri sun kori ya'yan gidan sun baje, sunne harda su shiga kicin, ko a lokacin da amaryar Bah din ta fito dan tunda ta farfaɗo daga summar bata iya rintsawa ba, ta fito ne da nufin zuwa bangaren su Hajia baba dan ta sake yi masu sannu da zaman makokin sai ta samu taron nan na dangin Mah masha ALLAH, hakan sai ya daure mata kai sosai da sosai, ama kuma bata wani kula su ba ta wuce,dan ba zata kula wannan sabon haukan ba, abinda suka sani shine ba'a isa ba fa ace za'a kawo masu wannan matar da ta galabi zamansu da mijinsu wace a lokacin da ta zauna a tare da su ko me ta yi daidai ne a wajen miji, ko zaginta ka yi in dai ya ji sai ya saba maka, baya gannin kwaliyarsu baya yaba masu kamar yadda yake yaba mata, kai dan karshen wulakanci akoy ranar da girkinta ne ta tashi da zazabi Honorable ya shiga kicin sai da yara suka zo sunna murnar yau babansu zai yi girki suka ga haza, gashi sun tsufabma ba wani daina yin nan nan da ita ya yi ba, dan sun sani komai nata daban yake a duniyar sa yanzu kuma dan an yi nadin sarautar son kai da hauka an ba mashayi sarauta ace uwarsa zata tare masu, ba zai taba yiwuwa ba, ya mike inma yana mikewa ya amshi sarautarsa Sannan ya maida matarsa gidanta shi ya fi zame masa alkhairi..
Ratsa mutanen nan ta yi ta shige dakin Bah
A lokacin Mah na saman salaya tana ta addu'a ta gama sallarta kennan, bata kai ga gama shafa adu'ar ba kunnayenta suka jiyo mata tsaki kasa kasa da fita da bugowar kofar, ita dai bata dakatar ba sai da ta gama ta mike ta je ta shafe jikin Bah da addu'a sannan ta fita ta janyo kofar dan zuwa wajen Rauda wace ta yi kiran Salima sau biyu tana tabatar mata sunna tare shi yasama bata fito ba
Turus Mah ta yi cike da mamaki tana kallon sabon salo, wai kiran sallah da usur, danginta ashe sunna nan basu tafi ba?
Kusan kowa kimtsawa ya shiga yi sunna mata sannu da fitowa, hakan ya sake sakata jin kamar ta dakatar da su da wannan shashancin, dan kuwa ita a memorinta babu abinda ya shige mata cikin junna, to in Bama shirme ba in maye ya manta ai uwar d'a ba zai taba yiwuwa ta manta ba!
Kasa zama ta yi, a tsayen nan tana kallon Herde ta ce" Au ashe kuna nan?"
Herde dukda ranta ya kiya da yar uwar Tata ta yi banza da su a falo bata nuna ba, cike da darajata kamar itace yayarta ta ce" Mu je ina kuma mu barki ke kadai Andiya?, yanzu dai mu manyan muke cewa mu tafi, su yan matan nan fa cewa suka yi ba yanzu ba, ban san me suke nufi ba"
Mah ta kasa tantance Hausar Tata, yan matan ta ringa bi da kallo su uku, Musulima, Hindatu, sai Akilah, wa'inda in ba yau ba, zata iya rantsewa ko a titi suka ganta suma da wahala su shaidata dan basu wani santa ba, a lokacin da komai ya kunce tsakanin iyayensu da ita tun kafin a samu cikin YUSUF ne, to ina su ya'yan jiya jiyan nan?
Bata iya cewa komai ba, yan matan kuwa da shiri suka zo kwanan suka zo, domin sun zo da tufafi, kuma wani abu da ta kula a tsakaninsu su ukun kowace bata shiga sabgar yar uwarta, ita abinda ya fi dan tsaye mata a rai to ina zata ajiye su ne?, itama bakuwa take a gidan nan fa, dakinta yana amsa sunnan nata dan baban su YUSUF yace Babu ubanda zai saka komai a ciki dan da mai dakin
Da kula sosai ta ce" To, abinda dai nake gani kar su takura, kin san nan din ba gidana bane, daki daya ne da Ni sai na YUSUF, wanda na tabata ko yau a ciki zai kwana tunda ba'a gama zaman bangaren marigayi ba, "
Herde ta ce" To ai ba wani abu bane dan sun zauna a dakin Mamansu, ko Musulima ta zauna, sauran su koma gida kawai dan bana so a barki ke kadai "
Idannuwa kawai Mah ta lumshe dan hanna kanta shiga matsanancin yannayin da zata fito ta fadi abinda yake ranta, ta yi gumm tana binsu da kallo dan ta yiwa kanta alkawarin sai ta iya gudun ruwan kowa a cikinsu
Matar yayansu ce da ta tabe baki jin maganar Herde ta ce" Aa, su zauna su duka ai ba wani damuwa bane, kin ga yanzu dole sai an tayata abubuwa kar su mata yawa, ga Honorable ga jigilar mai martaba, mu kuma da ace an bamu dama sai mu zauna mu taimaka mata, to wajen ne yanzun a nan bamu da wadatacen fili, sai an koma wajen Mai martabar in sha Allah "
Magana suke yi a tsakaninsu irin na yan uwa , ama kowa neman hanyar da zai shige jikinta ne yake yi, bayan sun manta jikin nan nata sun riga sun masa dukan da komai ya ruguje dangane da su sai abinda ba za'a rasa ba wanda musulunci ya tabbatar a tsakani
Bata kuma tanka masu ba har suka mike sai sake jaddada mata ta kula suke suka tafi , nan ta dawo ta cewa yan matan tana zuwa
Dakin Salima ta je ta yi salama
RAUDA na jin muryarta ta dago kanta da take tufkewa dan daga wanka ta fito kuma ruwa ya dan bata mata kan shine ta warware ya bushe ta shiga maida tufkewar
Sassauta fuskarta ta yi sosai tana kallon Mah ta furta" Mamah, sannu"
Mah ta saki nata fuskar fiye da ta RAUDA ta karaso ta zauna daf da gadon da Rauda ke zaune ta ce" Kin yi wanka ne?"
RAUDA ta gyada kanta ta idasa tufke kanta ta dauki mayafin suturarta ta saka tana sake kallon Mah
Mah ta ce" yaya abincin fa? Kin ci kuwa?"
Ita du banbarakwai take jin tambayoyin nan idan ana mata su ana nuna an damu da itan nan, kuma har yanzu ta kasa sakewa sosai wajen amsawa, ama kuma tana amsa Mah fiye da kowa, a tausashe da girmamawa ta ce" Mun ci tare da Salima ai Mamah"
Mah ta yi murmushi daidai Salima ta fito daga bayi tana gaisheta ta amsa da kula sosai ta ce" Allah ya saka da alkhairi daughter, kin kular min da yarinyata, oya tashi mu je ki kwonta dan ki huta sosai"
Tana fada ta mike ne, Har Rauda ta mike itama Salima da kula ta ce" Mah, ki barta a nan mana, na ga ke kike kula da Bah, kar a barta ita kadai a dakinki, ama in ta fi son cen din to"
Mah ta dubi Salima da murmushi a fuskarta, ta sake bin dakin Salimar da kallo, kwarai yana iya isar su koda su biyar ne bale su biyu kadai, ta sauke dubanta a kan RAUDA a tausashe ta ce" Zaki zauna a nan din kuwa?"
Da kula sosai Rauda ta gyadawa Mah kai, Salima kuwa ta fice da carbinta ta nufi bangaren mahaifiyarta dan ta sake gannin jikinta sannan ta mata sai da safe
Mah ta amshi wayarta ta saka mata numbarta ta ce" Ga numbana, idan kina da bukatar wani abu ki yi kirana ko wani time ne kin ji?"
Rauda ta kuma gyada kai tana gannin abin wani iri
Mah ta sake dubanta da kula sosai ta ce " dangane da neman babanki, ki kwontar da hankalinki kuma ki yi ta addu'a, in sha Allah da ba ga an samu dan sarari zan sake yiwa YUSUF maganar, na tabata zai maida hankali kin ji? Ama yanzun ki yi hakuri ki yi ta saka shi a addu'a, zan yi iya yina dan kar abin nan ya zama wani iri, kin ga babanku ya kai maganar ana ta bincike dan comissiona ya sanar min ko jiyan nan marikiyarki a wajensu ta yi rabin wuni dan shi bai yarda da ita ba, wai ko har sai da aka zane kanwar nan taki? Ni dai abinda na sani shine bi izinillah za'a same shi , sai mu yi ta saka shi a addu'a ya zamto a same sshi a cikin hayacinsa"
A sanyaye RAUDA ta ce" In sha Allah Mama na gode"
Mah ta yi murmushi sannan ta tafi ta barta zaune bakin gado
Bayan fitar Mah ta jima sosai a yannayin nan tana ta saka da warwara, daga bisani ta gyara kwinciyarta baki bakin gadon ta yi addu'a ta shiga neman barci, dan a hankali ta ringa jin sauki a zuciyarta da samun tabbacin in sha Allah za'a ga uncle dinta , a lokacin karfe goman dare tuni ta gabato dan saura yan mintuna ta cika Salimar kuma bata dawo ba,
Cen barci ya kusa daukar ta Salima ta dawo, tana jinta tana addu'a kuma tana ji ta rufa mata lalausan bargo itama ta kwonta nesa da ita ta rufan bayan ta kashe fitila, daga nan barci ya fara awom gaba da ita
Sai kusan sha biyu ya nufo bangaren Bah, tare da mutanen da suka rako shi, suke tafiya tamkar ta kurame domin tunda ya shiga gabansu suka yi shiru suke tafe kowane na mamakin taku baban taku irin na rikaken sarki a tare da sarkinsu
Sunna zuwa wajen get din ya dakata ya juyo a nutse da idannuwansa masu tsauri da girma da kaifi ya ringa bin su da kallo yana jin yadda suke masa salama da yare mai tafe da kirari sunna duka masa da yi masa sai da safe
Ita har ga Allah ta zata kawai Herde ta yi tafiyarta ne, hakan ya sa bata wani leko ba, bata damu da nema masu abinci, bata san wainar da suke toya mata ta wuce tunanin bawa, domin kiri kiri sun kori ya'yan gidan sun baje, sunne harda su shiga kicin, ko a lokacin da amaryar Bah din ta fito dan tunda ta farfaɗo daga summar bata iya rintsawa ba, ta fito ne da nufin zuwa bangaren su Hajia baba dan ta sake yi masu sannu da zaman makokin sai ta samu taron nan na dangin Mah masha ALLAH, hakan sai ya daure mata kai sosai da sosai, ama kuma bata wani kula su ba ta wuce,dan ba zata kula wannan sabon haukan ba, abinda suka sani shine ba'a isa ba fa ace za'a kawo masu wannan matar da ta galabi zamansu da mijinsu wace a lokacin da ta zauna a tare da su ko me ta yi daidai ne a wajen miji, ko zaginta ka yi in dai ya ji sai ya saba maka, baya gannin kwaliyarsu baya yaba masu kamar yadda yake yaba mata, kai dan karshen wulakanci akoy ranar da girkinta ne ta tashi da zazabi Honorable ya shiga kicin sai da yara suka zo sunna murnar yau babansu zai yi girki suka ga haza, gashi sun tsufabma ba wani daina yin nan nan da ita ya yi ba, dan sun sani komai nata daban yake a duniyar sa yanzu kuma dan an yi nadin sarautar son kai da hauka an ba mashayi sarauta ace uwarsa zata tare masu, ba zai taba yiwuwa ba, ya mike inma yana mikewa ya amshi sarautarsa Sannan ya maida matarsa gidanta shi ya fi zame masa alkhairi..
Ratsa mutanen nan ta yi ta shige dakin Bah
A lokacin Mah na saman salaya tana ta addu'a ta gama sallarta kennan, bata kai ga gama shafa adu'ar ba kunnayenta suka jiyo mata tsaki kasa kasa da fita da bugowar kofar, ita dai bata dakatar ba sai da ta gama ta mike ta je ta shafe jikin Bah da addu'a sannan ta fita ta janyo kofar dan zuwa wajen Rauda wace ta yi kiran Salima sau biyu tana tabatar mata sunna tare shi yasama bata fito ba
Turus Mah ta yi cike da mamaki tana kallon sabon salo, wai kiran sallah da usur, danginta ashe sunna nan basu tafi ba?
Kusan kowa kimtsawa ya shiga yi sunna mata sannu da fitowa, hakan ya sake sakata jin kamar ta dakatar da su da wannan shashancin, dan kuwa ita a memorinta babu abinda ya shige mata cikin junna, to in Bama shirme ba in maye ya manta ai uwar d'a ba zai taba yiwuwa ta manta ba!
Kasa zama ta yi, a tsayen nan tana kallon Herde ta ce" Au ashe kuna nan?"
Herde dukda ranta ya kiya da yar uwar Tata ta yi banza da su a falo bata nuna ba, cike da darajata kamar itace yayarta ta ce" Mu je ina kuma mu barki ke kadai Andiya?, yanzu dai mu manyan muke cewa mu tafi, su yan matan nan fa cewa suka yi ba yanzu ba, ban san me suke nufi ba"
Mah ta kasa tantance Hausar Tata, yan matan ta ringa bi da kallo su uku, Musulima, Hindatu, sai Akilah, wa'inda in ba yau ba, zata iya rantsewa ko a titi suka ganta suma da wahala su shaidata dan basu wani santa ba, a lokacin da komai ya kunce tsakanin iyayensu da ita tun kafin a samu cikin YUSUF ne, to ina su ya'yan jiya jiyan nan?
Bata iya cewa komai ba, yan matan kuwa da shiri suka zo kwanan suka zo, domin sun zo da tufafi, kuma wani abu da ta kula a tsakaninsu su ukun kowace bata shiga sabgar yar uwarta, ita abinda ya fi dan tsaye mata a rai to ina zata ajiye su ne?, itama bakuwa take a gidan nan fa, dakinta yana amsa sunnan nata dan baban su YUSUF yace Babu ubanda zai saka komai a ciki dan da mai dakin
Da kula sosai ta ce" To, abinda dai nake gani kar su takura, kin san nan din ba gidana bane, daki daya ne da Ni sai na YUSUF, wanda na tabata ko yau a ciki zai kwana tunda ba'a gama zaman bangaren marigayi ba, "
Herde ta ce" To ai ba wani abu bane dan sun zauna a dakin Mamansu, ko Musulima ta zauna, sauran su koma gida kawai dan bana so a barki ke kadai "
Idannuwa kawai Mah ta lumshe dan hanna kanta shiga matsanancin yannayin da zata fito ta fadi abinda yake ranta, ta yi gumm tana binsu da kallo dan ta yiwa kanta alkawarin sai ta iya gudun ruwan kowa a cikinsu
Matar yayansu ce da ta tabe baki jin maganar Herde ta ce" Aa, su zauna su duka ai ba wani damuwa bane, kin ga yanzu dole sai an tayata abubuwa kar su mata yawa, ga Honorable ga jigilar mai martaba, mu kuma da ace an bamu dama sai mu zauna mu taimaka mata, to wajen ne yanzun a nan bamu da wadatacen fili, sai an koma wajen Mai martabar in sha Allah "
Magana suke yi a tsakaninsu irin na yan uwa , ama kowa neman hanyar da zai shige jikinta ne yake yi, bayan sun manta jikin nan nata sun riga sun masa dukan da komai ya ruguje dangane da su sai abinda ba za'a rasa ba wanda musulunci ya tabbatar a tsakani
Bata kuma tanka masu ba har suka mike sai sake jaddada mata ta kula suke suka tafi , nan ta dawo ta cewa yan matan tana zuwa
Dakin Salima ta je ta yi salama
RAUDA na jin muryarta ta dago kanta da take tufkewa dan daga wanka ta fito kuma ruwa ya dan bata mata kan shine ta warware ya bushe ta shiga maida tufkewar
Sassauta fuskarta ta yi sosai tana kallon Mah ta furta" Mamah, sannu"
Mah ta saki nata fuskar fiye da ta RAUDA ta karaso ta zauna daf da gadon da Rauda ke zaune ta ce" Kin yi wanka ne?"
RAUDA ta gyada kanta ta idasa tufke kanta ta dauki mayafin suturarta ta saka tana sake kallon Mah
Mah ta ce" yaya abincin fa? Kin ci kuwa?"
Ita du banbarakwai take jin tambayoyin nan idan ana mata su ana nuna an damu da itan nan, kuma har yanzu ta kasa sakewa sosai wajen amsawa, ama kuma tana amsa Mah fiye da kowa, a tausashe da girmamawa ta ce" Mun ci tare da Salima ai Mamah"
Mah ta yi murmushi daidai Salima ta fito daga bayi tana gaisheta ta amsa da kula sosai ta ce" Allah ya saka da alkhairi daughter, kin kular min da yarinyata, oya tashi mu je ki kwonta dan ki huta sosai"
Tana fada ta mike ne, Har Rauda ta mike itama Salima da kula ta ce" Mah, ki barta a nan mana, na ga ke kike kula da Bah, kar a barta ita kadai a dakinki, ama in ta fi son cen din to"
Mah ta dubi Salima da murmushi a fuskarta, ta sake bin dakin Salimar da kallo, kwarai yana iya isar su koda su biyar ne bale su biyu kadai, ta sauke dubanta a kan RAUDA a tausashe ta ce" Zaki zauna a nan din kuwa?"
Da kula sosai Rauda ta gyadawa Mah kai, Salima kuwa ta fice da carbinta ta nufi bangaren mahaifiyarta dan ta sake gannin jikinta sannan ta mata sai da safe
Mah ta amshi wayarta ta saka mata numbarta ta ce" Ga numbana, idan kina da bukatar wani abu ki yi kirana ko wani time ne kin ji?"
Rauda ta kuma gyada kai tana gannin abin wani iri
Mah ta sake dubanta da kula sosai ta ce " dangane da neman babanki, ki kwontar da hankalinki kuma ki yi ta addu'a, in sha Allah da ba ga an samu dan sarari zan sake yiwa YUSUF maganar, na tabata zai maida hankali kin ji? Ama yanzun ki yi hakuri ki yi ta saka shi a addu'a, zan yi iya yina dan kar abin nan ya zama wani iri, kin ga babanku ya kai maganar ana ta bincike dan comissiona ya sanar min ko jiyan nan marikiyarki a wajensu ta yi rabin wuni dan shi bai yarda da ita ba, wai ko har sai da aka zane kanwar nan taki? Ni dai abinda na sani shine bi izinillah za'a same shi , sai mu yi ta saka shi a addu'a ya zamto a same sshi a cikin hayacinsa"
A sanyaye RAUDA ta ce" In sha Allah Mama na gode"
Mah ta yi murmushi sannan ta tafi ta barta zaune bakin gado
Bayan fitar Mah ta jima sosai a yannayin nan tana ta saka da warwara, daga bisani ta gyara kwinciyarta baki bakin gadon ta yi addu'a ta shiga neman barci, dan a hankali ta ringa jin sauki a zuciyarta da samun tabbacin in sha Allah za'a ga uncle dinta , a lokacin karfe goman dare tuni ta gabato dan saura yan mintuna ta cika Salimar kuma bata dawo ba,
Cen barci ya kusa daukar ta Salima ta dawo, tana jinta tana addu'a kuma tana ji ta rufa mata lalausan bargo itama ta kwonta nesa da ita ta rufan bayan ta kashe fitila, daga nan barci ya fara awom gaba da ita
Sai kusan sha biyu ya nufo bangaren Bah, tare da mutanen da suka rako shi, suke tafiya tamkar ta kurame domin tunda ya shiga gabansu suka yi shiru suke tafe kowane na mamakin taku baban taku irin na rikaken sarki a tare da sarkinsu
Sunna zuwa wajen get din ya dakata ya juyo a nutse da idannuwansa masu tsauri da girma da kaifi ya ringa bin su da kallo yana jin yadda suke masa salama da yare mai tafe da kirari sunna duka masa da yi masa sai da safe