Sashe 109
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A tausashe ya ce" Idan ka yi haka, kamar ka nuna ilimin ka sanin ne kawai, ba zaka yi aiki da shi ba....., ka ga rayuwa babu abinda bata zuwarwa bawa da shi, Ni in ce mi a kan tawa rayuwar? Ni na gina rayuwa da ita har mun haihu ama a kan shirme ta lalata komai, in ba dan mahaifinta ya yi tsaye ba da harta sunnan gidansa ta lalata, ka ga dan Adam ne keda haka, dan adam a kan kadan sai ya bata da yawa, inaga a yi hakuri da kadarar nan shine ya fi zama alkhairi "
"Na sani, kuma na yarda da haka, but Mah tace za'a zauna da ita a yadda take Man" ya fada kasa kasan yana lumshe idannuwansa
shima ido ya bude sosai ya ce" Ban fahimta ba, tana nufin zama na aure?"
YUSUF ya dan gyada kansa tamkar yana gabansa, kasa kasa ya ce" Na Bara maka sako a amail dinka, dangane da iyayen nata "
Mikewa ya yi da sauri ya karasa wajen da computarsa ke ajiye ya danna ya shiga dadanawa yana zuwa har ya kai wajen da yake son zuwan, YUSUF na jinsa kuma ya gane sakon ne yake son karantawa shi yasa ya yi lamo a saman kujerar yana sauraronsa har ya gama karantawa ya ringa jin salatinsa a nutse sannan ya ji ya shiga magana a tausashe kamar haka" Dole hukunci zai hau kansu, daga ita har shi la'ananen!, dole za'a sanar da hukuncinsu, sannan dole za'a sau yarinyar nan, ba matar SARKI bace!"
Shirun da Yusuf ya yi ya saka Shaheed fadin" Ba wasa nake yi ba, ba zan kyale ba fa, ba zan iya kyalewa ba, ba matar aurenka bace, rashin jin magana na rigima daban wanda Allah ke jarabtarmu da mata masu halin nan, wannan lamarin daban, da ace wasu yan tsirakun ne sai a daidaita zaman, ama abin da yawa , abin da yawan gaske da kuma girma, ita da kanta rayuwar garinka sai ya gagareta idan abin nan ya fita , bale ita din mutun ce mai janyowa kanta makiya da kanta, inaga abinda ya dace a yi shine a maida hankali a zartar da komai kafin ta sakankance!"
"Maganar Mah ake yi Shaheed, maganar Mah ake yi, ka san Wacece Mah a rayuwata, a duniyata, zan iya rantse maka ni dai ba zan taba tsallake maganarta ba tunda ba sabawa Allah ta yi ba,kuma na san kaima ba zaka sa a tsallake din ba......, ka san me yake damuna? Shaheed ka san menene ya fi damuna?"
Shaheed da jikinsa ya karra yin sanyi a hankali ya amsa shi da a'a
YUSUF ya ce" Abinda yake damuna Amnah sunnanta uwar gidana a cikin Matana, idan tana matsayin matata dole zamu samu iyali da ita in dai tana haihuwa kuma in nima ina haihuwa....., yaya zata tarbiyantar da yayana bayan ita dinma bata da tarbiyyar.....?, har yanzu bata yarda tana cikin aikata laifin da bai dace ba bale ta fara tuba, gidana ta sanyo min dan daudu har dakinta na barci, tana iya tubewa a gabansa bilahilazi!"
Shaheed ya dafe kirji dan irin yadda wani abu ke masa zuga a ciki, shi fa da ace maganar nan ba Mah ciki, walahi walahi a gobe sai ya san abinda ya aikata aka fito da kowa aka yi masa dukan tsiya kafin a bashi hukuncin da ya dace, dan a yanzu shi bai cika bada hukunci ba duka ba, zane mutun ake yi da dukan da zai gigitashi sai a hauda da hukunci, shi yasa iya shege ya ragu sosai a Damagaran,
"Nd......nd....... Shaheed bana tunanin zan iya auren wata na hada da wancen dake barci na iya yin adalci......, ka ga an jima da kawar da maganar wai dole sai an yiwa sarki mace biyu, ko hudu, an dawo duniyar idan zai iya, Shaheed na riga na san in na yarda na karra mata wata rigima zata yi ta yi, kuma Ni rigimar ce bana so walahi du daga min hankali take yi" ya karashe a sanyaye
Shaheed ya yi shiru na yan sekwani, a hankali ya ce " wai wace ne haka?"
YUSUF ya ce " Baby mana wace zan ce in ba ita ba"
Shaheed ya sauke numfashi a dole yana dane dariyarsa, sai dai kiri da muzu dariyar nan ta ki dannuwa sai da ya yita kasa kasa yana fadin " Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, kai bawa, bawa? in ba dan gagawa ta bawa ba da ya cinma abu da yawa, ka duba ka ga irin dauki ba dadin da muke yi da kai, idan na ambata maka soyayama sai ka nunan yatsa, ashe Azal din ta idasa cin maka har kana fada baki sake? cewa fa ka yi ba zaka taba yafe mata ba? a kan me zaka yafe mata? kar ka yarda fa man"
YUSUF ya yi tsittttttttt yana sauraronsa, a hankali ya yi murmushi ya ce" Ai Allah yana son mai yafiya, ka ji tsoron Allah hadani zaka yi da iyalina? ka ga sai an jima dilla"
Gannin da gaske kashewa zai yi ya ce" zan ajiye maka sako a amail ka duba Please, kuma ka ga NAJEEBA tace zata zo ta yi Barka da tarewa, ama anya zaka bari a ga wama kace?"
Yusuf hankali kwonce ya ce" Baby, baby ne sunnan"
Shaheed ya sake saka dariya a dole, dan walahi bai tana gannin marar kunya irin YUSUF ba, uhum lalle, dama ya kyale shi wani cika da batsewa wani alwashin ba zai yafe masa ba ya bashi lokaci ne , gashinan abin ya zo ya koma wata y'ar murya kamar ba shi ba, a haka suka yi salama Shaheed ya shiga loda masa sakon da zai Bara masa din dan idan safiya ta yi ba lalle ya iya samun lokacin aika sakon ba, abu daya ya sani YUSUF sarki ne, ya kuma yarda da sarautarsa dan a hawansa zuwa yanzu ya jinjina masa fiye da kima, Yusuf ya yi rawar gani a garinsa yana cikin yi, Yusuf bai dogara da albashi gwamnati ba irin na wasu sarakan, a yanzu haka tun hawansa har zuwa yau bai san me gwamnati ke zuba masa ba matsayin albashi, shi yasa a lokacin da ake rigimar sarauta wa za'a Hauda yace sunna da sarki sama da wanda zai iya rike su ne? ai nasu da sarki sai wanda zai iya rike su, idan har rayuwar suke son gannin cenzawarta, kwarai Hajia baba ta yi gaskiya da tace da su me suke jira? duk wanda yake da ja ya kwatanta ya kawo wanda ya fi shi, YUSUF tun bai zama sarki ba yana taimakawa talakawan garinsa a boye bale da ya zama sarki, karami ne a cikin manya mai manyan kudade a dole rana tsaka manyan suka ce da MALEEK *BABA*
YUSUF kuwa murmushi ya yi yana karra jin sanyi a zuciyarsa
A rayuwa ko waye kai, ya zamo kana da abokin sirri, wanda idan dadi ya samu zaka tunkare shi da shi kai tsaye haka kuma wahala, tsakaninsa da shaheed sukan yi kiran tsakiyar dare dan kawai su yi jayayya a kan ball, haka kuma sukan yi dan su yi maganar sirrin su a tsakaninsu, gaskiya daya ce, amana daya ce, sunna shawartar junna da shawarwari masu kyau sunna kuma amintar junna da zuciya daya
A nutse ya koma saman gadon nan, cikin dabara ya dorata saman kirjinsa a hankali yana shafa kanta har barci ya fara fizgarsa , a kasan zuciyarsa yana yarda da akace abin nan fa na dadi ne, bai taba tunanin shi YUSUF zai iya wayar gari, gashi ga RAUDA a daki daya wani abu ya hanna shi far mata ba, sai gashi yannayin da zuciyarsa ke ciki a yau ya ki wani yunkurin dan ba zai so ya sauke mata wani fushi ko tashin hankalin a kanta ba, zai fi so ko menene ya zo masu a nutse yadda abin zai zama baban tarihi a rayuwarsu....da wannan barcin ya dauke shi shima mai sanyi da nutsuwar dake jikinsa har kiran sallah ya tashe shi, ko nace ya tashe su gaba daya
Irin yadda yanzunma take boye fuska ya saka shi nishadi , irin yadda take hade jikinta tana murzar yan yatsu ya saka shi yi mata kallon y'ar shilar amarya har a cikin ransa, sai kuma ya ringa jin tamkar zai yi bincike a duniyarta, domin tunda yake bai taba motsi da nufin bincikar Wacece RAUDA ba, sai iya abinda ta fada da bakinta a ranar da suka je gidan su shi da Bah da Mah, da wanda ta fada bayan ta gama koke koken uncle din ta, wato dai sama sama gefe gefe ya san RAUDA, ya hanna kansa bincikar Wacece ita dan baban tsoronsa kar garin bincike binciken ya bincikawa kansa ciwon da zai zame masa ila a rayuwa
Da wannan ya fice a dakin ya nufi masalaci, itama ta dauki hijabinta dake kasa da kwanukan nan da gudu gudu ta gudu nata bangaren ko wayarta bata iya tsayawa dauka ba, tsoronta daya kar ya kuma samun ta a dakin ya hannata zuwa nata dakin, wannan abu da ya aikata mata jiya zuwa yau kuwa ya gama like mata a zuciya, zuciyarta banda kiran d'an Mah ba abinda take yi a boye
Kamar yadda suka saba daga masalaci shi da Bah suke nufowa bangaren Hajia baba hakan ce ta faru yauma
Sai dai a hanya Bah din ya sanar masa abinda ya faru a jiya shi da Mah da kuma abinda suke da niyar yankewa shi da Hajia
"Na sani, kuma na yarda da haka, but Mah tace za'a zauna da ita a yadda take Man" ya fada kasa kasan yana lumshe idannuwansa
shima ido ya bude sosai ya ce" Ban fahimta ba, tana nufin zama na aure?"
YUSUF ya dan gyada kansa tamkar yana gabansa, kasa kasa ya ce" Na Bara maka sako a amail dinka, dangane da iyayen nata "
Mikewa ya yi da sauri ya karasa wajen da computarsa ke ajiye ya danna ya shiga dadanawa yana zuwa har ya kai wajen da yake son zuwan, YUSUF na jinsa kuma ya gane sakon ne yake son karantawa shi yasa ya yi lamo a saman kujerar yana sauraronsa har ya gama karantawa ya ringa jin salatinsa a nutse sannan ya ji ya shiga magana a tausashe kamar haka" Dole hukunci zai hau kansu, daga ita har shi la'ananen!, dole za'a sanar da hukuncinsu, sannan dole za'a sau yarinyar nan, ba matar SARKI bace!"
Shirun da Yusuf ya yi ya saka Shaheed fadin" Ba wasa nake yi ba, ba zan kyale ba fa, ba zan iya kyalewa ba, ba matar aurenka bace, rashin jin magana na rigima daban wanda Allah ke jarabtarmu da mata masu halin nan, wannan lamarin daban, da ace wasu yan tsirakun ne sai a daidaita zaman, ama abin da yawa , abin da yawan gaske da kuma girma, ita da kanta rayuwar garinka sai ya gagareta idan abin nan ya fita , bale ita din mutun ce mai janyowa kanta makiya da kanta, inaga abinda ya dace a yi shine a maida hankali a zartar da komai kafin ta sakankance!"
"Maganar Mah ake yi Shaheed, maganar Mah ake yi, ka san Wacece Mah a rayuwata, a duniyata, zan iya rantse maka ni dai ba zan taba tsallake maganarta ba tunda ba sabawa Allah ta yi ba,kuma na san kaima ba zaka sa a tsallake din ba......, ka san me yake damuna? Shaheed ka san menene ya fi damuna?"
Shaheed da jikinsa ya karra yin sanyi a hankali ya amsa shi da a'a
YUSUF ya ce" Abinda yake damuna Amnah sunnanta uwar gidana a cikin Matana, idan tana matsayin matata dole zamu samu iyali da ita in dai tana haihuwa kuma in nima ina haihuwa....., yaya zata tarbiyantar da yayana bayan ita dinma bata da tarbiyyar.....?, har yanzu bata yarda tana cikin aikata laifin da bai dace ba bale ta fara tuba, gidana ta sanyo min dan daudu har dakinta na barci, tana iya tubewa a gabansa bilahilazi!"
Shaheed ya dafe kirji dan irin yadda wani abu ke masa zuga a ciki, shi fa da ace maganar nan ba Mah ciki, walahi walahi a gobe sai ya san abinda ya aikata aka fito da kowa aka yi masa dukan tsiya kafin a bashi hukuncin da ya dace, dan a yanzu shi bai cika bada hukunci ba duka ba, zane mutun ake yi da dukan da zai gigitashi sai a hauda da hukunci, shi yasa iya shege ya ragu sosai a Damagaran,
"Nd......nd....... Shaheed bana tunanin zan iya auren wata na hada da wancen dake barci na iya yin adalci......, ka ga an jima da kawar da maganar wai dole sai an yiwa sarki mace biyu, ko hudu, an dawo duniyar idan zai iya, Shaheed na riga na san in na yarda na karra mata wata rigima zata yi ta yi, kuma Ni rigimar ce bana so walahi du daga min hankali take yi" ya karashe a sanyaye
Shaheed ya yi shiru na yan sekwani, a hankali ya ce " wai wace ne haka?"
YUSUF ya ce " Baby mana wace zan ce in ba ita ba"
Shaheed ya sauke numfashi a dole yana dane dariyarsa, sai dai kiri da muzu dariyar nan ta ki dannuwa sai da ya yita kasa kasa yana fadin " Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, kai bawa, bawa? in ba dan gagawa ta bawa ba da ya cinma abu da yawa, ka duba ka ga irin dauki ba dadin da muke yi da kai, idan na ambata maka soyayama sai ka nunan yatsa, ashe Azal din ta idasa cin maka har kana fada baki sake? cewa fa ka yi ba zaka taba yafe mata ba? a kan me zaka yafe mata? kar ka yarda fa man"
YUSUF ya yi tsittttttttt yana sauraronsa, a hankali ya yi murmushi ya ce" Ai Allah yana son mai yafiya, ka ji tsoron Allah hadani zaka yi da iyalina? ka ga sai an jima dilla"
Gannin da gaske kashewa zai yi ya ce" zan ajiye maka sako a amail ka duba Please, kuma ka ga NAJEEBA tace zata zo ta yi Barka da tarewa, ama anya zaka bari a ga wama kace?"
Yusuf hankali kwonce ya ce" Baby, baby ne sunnan"
Shaheed ya sake saka dariya a dole, dan walahi bai tana gannin marar kunya irin YUSUF ba, uhum lalle, dama ya kyale shi wani cika da batsewa wani alwashin ba zai yafe masa ba ya bashi lokaci ne , gashinan abin ya zo ya koma wata y'ar murya kamar ba shi ba, a haka suka yi salama Shaheed ya shiga loda masa sakon da zai Bara masa din dan idan safiya ta yi ba lalle ya iya samun lokacin aika sakon ba, abu daya ya sani YUSUF sarki ne, ya kuma yarda da sarautarsa dan a hawansa zuwa yanzu ya jinjina masa fiye da kima, Yusuf ya yi rawar gani a garinsa yana cikin yi, Yusuf bai dogara da albashi gwamnati ba irin na wasu sarakan, a yanzu haka tun hawansa har zuwa yau bai san me gwamnati ke zuba masa ba matsayin albashi, shi yasa a lokacin da ake rigimar sarauta wa za'a Hauda yace sunna da sarki sama da wanda zai iya rike su ne? ai nasu da sarki sai wanda zai iya rike su, idan har rayuwar suke son gannin cenzawarta, kwarai Hajia baba ta yi gaskiya da tace da su me suke jira? duk wanda yake da ja ya kwatanta ya kawo wanda ya fi shi, YUSUF tun bai zama sarki ba yana taimakawa talakawan garinsa a boye bale da ya zama sarki, karami ne a cikin manya mai manyan kudade a dole rana tsaka manyan suka ce da MALEEK *BABA*
YUSUF kuwa murmushi ya yi yana karra jin sanyi a zuciyarsa
A rayuwa ko waye kai, ya zamo kana da abokin sirri, wanda idan dadi ya samu zaka tunkare shi da shi kai tsaye haka kuma wahala, tsakaninsa da shaheed sukan yi kiran tsakiyar dare dan kawai su yi jayayya a kan ball, haka kuma sukan yi dan su yi maganar sirrin su a tsakaninsu, gaskiya daya ce, amana daya ce, sunna shawartar junna da shawarwari masu kyau sunna kuma amintar junna da zuciya daya
A nutse ya koma saman gadon nan, cikin dabara ya dorata saman kirjinsa a hankali yana shafa kanta har barci ya fara fizgarsa , a kasan zuciyarsa yana yarda da akace abin nan fa na dadi ne, bai taba tunanin shi YUSUF zai iya wayar gari, gashi ga RAUDA a daki daya wani abu ya hanna shi far mata ba, sai gashi yannayin da zuciyarsa ke ciki a yau ya ki wani yunkurin dan ba zai so ya sauke mata wani fushi ko tashin hankalin a kanta ba, zai fi so ko menene ya zo masu a nutse yadda abin zai zama baban tarihi a rayuwarsu....da wannan barcin ya dauke shi shima mai sanyi da nutsuwar dake jikinsa har kiran sallah ya tashe shi, ko nace ya tashe su gaba daya
Irin yadda yanzunma take boye fuska ya saka shi nishadi , irin yadda take hade jikinta tana murzar yan yatsu ya saka shi yi mata kallon y'ar shilar amarya har a cikin ransa, sai kuma ya ringa jin tamkar zai yi bincike a duniyarta, domin tunda yake bai taba motsi da nufin bincikar Wacece RAUDA ba, sai iya abinda ta fada da bakinta a ranar da suka je gidan su shi da Bah da Mah, da wanda ta fada bayan ta gama koke koken uncle din ta, wato dai sama sama gefe gefe ya san RAUDA, ya hanna kansa bincikar Wacece ita dan baban tsoronsa kar garin bincike binciken ya bincikawa kansa ciwon da zai zame masa ila a rayuwa
Da wannan ya fice a dakin ya nufi masalaci, itama ta dauki hijabinta dake kasa da kwanukan nan da gudu gudu ta gudu nata bangaren ko wayarta bata iya tsayawa dauka ba, tsoronta daya kar ya kuma samun ta a dakin ya hannata zuwa nata dakin, wannan abu da ya aikata mata jiya zuwa yau kuwa ya gama like mata a zuciya, zuciyarta banda kiran d'an Mah ba abinda take yi a boye
Kamar yadda suka saba daga masalaci shi da Bah suke nufowa bangaren Hajia baba hakan ce ta faru yauma
Sai dai a hanya Bah din ya sanar masa abinda ya faru a jiya shi da Mah da kuma abinda suke da niyar yankewa shi da Hajia