Sashe 23
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shi dai tukinsa yake yi yana jin dan feeling na abinda ya kwana biyu bai yi ba, rabonsa da nanikar jikin wata kwana biyu fa cirrrr, kuma har mantawa yake yi saboda rashin lafiyar mamansa, ama yau sai yake jin wani feeling na neman damunsa
A nutse suka karasa cikin anguwar har kofar gidan
Sunna tsayawa Aminu ya nuna masu gidan yana faɗin " Ga gidan nan sir, ama inaga shi uncle din nata baya gidan dan yanzu a masalaci liman na fada min ko na ganshi? Yace sau biyu tana zuwa nemansa wai tunda ya fita dazu ransa a bace"
Honorable ne ya dube shi da kula ya ce" Ransa a bace? Kwananta a wani wajen ya saka ransa bacewa ko ina iyayenta ne ko hutu ya zo wajen uncle din nata?"
A hankali Yusuf ya jinginar da bayansa jikin kujerar motar yana sauke dubansa daga kan Mahaifiyarsa dake kallonsu yana jin Aminu na maimaitawa Honorable cewar RAUDA marainiya ce gaba da baya a hannun uncle din nata take
Shiru wajen ya dauka, na tarin alhinin jin maganar ne ko mene?
A sanyaye Mah ta sauko kafarta daga cikin motar bayan ta bude ta ajiye wayarta baba tana fadin" Bari Ni na shiga ka ga idan yana nan din sai ya maku iso"
Haka kawai ta ji zuciyarta ta buga mata jin labarin yarinyar, sai ta ji bari ta shiga ko sa ga marikinta su sanar masa ga asalin inda ta kwana ta yiwu da akace ya fita hankalinsa tashe ya daina fushi ya yi hakuri
Da ido YUSUF ya bita har ta bude karamar kofar gidan ta shiga sannan ya dawo da dubansa kan Aminu dake dan yiwa Ana shinfidar wasu daga cikin abinda Rauda ke ganni a gidan rikon nata
Salama Maman Yusuf ke yi tana karawa, ama ba amsa, sai murya dake tashi sama sama da alwashi kala kala wanda ya sakata dakatawa a dole tana tunanin ta koma ne ko ta shiga?
Ta daga kafa da nufin shigewa ciki ta ji sama sama murya na fadin" Rauda idan har ubanki ya shanye giya da kudina nice ajalinsa, kuma kema nice ajalinki ki rubuta ki ajiye, munafuka algunguma, ki bani kudina nace , ki tashi du gidan ubanda kika san zaki je ki samo min kudina ki je ki samo idan ba haka ba na wulakanta ki na je na dauko dayan shegen na yanka shi!"
Hankalin Mah ne ya mugun tashi, da sauri ta juya har tana jin kafarta zata tashi na ciwo ta fito ta nufo mota tana haki
Da sauri YUSUF ya bude motar ya fito ya kamo hannayenta yana kallon yadda take haki hankalinta tashe, Abu ma dake tsaye shi da Aminu gefe sun nitsa a labarin Rauda da sauri ya karaso yana kamota ba wata wata ya rungumeta a jikinsa yana fadin" Hey Madame, menene, me ya faru?"
Hankali tashe har hannayenta na rawa ta fadi abinda ta ji da ta shiga, da sauri ta ce" Wacece RAUDA? Inace wajen yarinyar da muka zo ne , me ta yiwa Mamanta take fadin kalaman nan a kanta innalilahi Wa inna ilaihi raj'une"
A nutse ya mayar da hannunsa ya rufe motar ya juyo yana kallon mahaifinsa dake faman fada mata kar ta daga hankalinta ba komai bane bari ya shiga ya gani
A tausashe ya ce" Aba bari na shiga na gani"
Yana fada ya juya ya nufi hanyar shiga, da sauri Aminu ya biyo shi yana fadin" Biya Muradi da zaka yi hakuri na tabo wata mace ta shiga, ka san matar nan da sharin tsiya, gashi bata gannin girman kowa kar ta lika maka wani sharin a banza a wofi"
Murmushi YUSUF ya yi masa ya nausa kansa ciki yana salamar da ta zame masa jiki ciki ciki
Yana shigowa Farisa ga fito daga bayi ta gama aikata kashinta na magariba da ya zame mata jiki suka yi ido hudu
Ido ta zuba masa kafin da sauri ta dubi kafarta dake dauke da dati harda zannin jikinta, zannin da ta wuni da shi shekaran jiya da jiya ne , yau fa har zata cenza tace bari dai ya karra kwana biyu sai ta cenza dan bata kayanma ai ba kyau,sai gashi an yi rantsatsen bako?
Da sauri ta wuce shi ta yi cikin gidan har kamar zata kifa
Tana shiga ta ce" Mama, wa bilahilazi Balarabe a cikin gidanmu, Allah ka sa bakona ne , Allah Allah Farisa Allah amen"
Uwar dake daure da zani saman munafata ta dubeta itama yau din dai wankan nan bata yi shi ba, ta wuni a daki ko abinci bata ci ba ta ce" Balarabe kuma?, Farisa zan ci uban ubanki idan har baki daina kawo min shirme a yau ba, me zai kawo Balarabe anguwar nan dan ubanki?, ko wajen wannan ya zo ai ba zai shigo min gida ba ko?"
Da sauri ta tari uwar tana fadin" Allah ya sawaka ya zo wajenta ki ji kai mugun fata , kina ji ina adu'ar Allah ya sa wajena ya zo ki wani ce wajenta, ke Rauda gaskiya tashi ki shiga ciki kar ya ganki ki masa asirin da kika saba da munafukan idannuwan nan naki, Ni dai kuma kar ku bari ya gane ana neman baba Umaru gaskiya kar ku zubar min da mutincina!"
Magana take yi tamkar ta sako da sako, magana take yi ta rashin mutunci tana hantarar uwar da Raudar baki daya domin du ta gigice
Mikewa Rauda ta yi idannuwanta ko gannin kirki basa yi
Sama hijab ne a jikinta mai ruwan anta har kasa ama bashi da hannu ya dai kama fuskarta das ya fitar da zagayen fuskar nata, hakan ya sa fuskar ta fito fayau da ita sai lebenta da ya dan bushe da kuma idannuwanta da suka kara nutsewa suka yi luhu luhu
Niyarta ta sake komawa masalaci daga nan kuma ta nufi gidan giyar da yake zuwa, in dai yana cen shikenan sai ta dawo ta nutsu ta kuma ci gaba da yi masa addu'a, dan jikinta na bata mugun abin da ya ringa bata a ranar da zata iya kiran ranar da Azal ta fadawa ahalinta
Da sauri Farisa ta riko hijab din tana fadin" Rauda nace kar ki fita fa!"
Da kyar ta iya yiwa idannuwanta luuuuuuu ta bude bakinta ta fara magana ta ga an daga labule an shigo ama bata ga mai shigowar ba, a hargitse ta ce" Idan kika kuma taba min sutura da kazantar nan taki sai na karya maki hannu, idan kika kuma daga mun murya sai na janyo makogwaronki FARISA!"
Da sauri ta yi baya tana neman yin kusa da mamanta, dan ita ta sha'afa kan Wacece RAUDA ita kuma Mama tunda ta ga wanda ya shigo sai itama ta shiga kunce hijabin dake daure a kugunta tana kokarin sakin fuska ta ce" Barka da zuwa baki muka yi ne?"
A hankali Rauda ta juyo da niyar zagayesu ta fice idannuwanta suka sauka a kan fuskarsa ya zuba mata ido shima sannan ya dauke ya sake kallon hoton dake dakin daya kwal wanda kwarai ya san fuskar mutumen, ama a inda ya san mutumen a waje ne marar kyau, wajen da su mutanen suke kwalewa shi kuwa yakan je ne dan ya yi nasa kalar kwalewar shima
"Ba wajenki na zo ba" YUSUF ya fada a hade yana kaucewa daga nufo shin da Mama ta yi da kujera
A hade ya ce" Ke ?, menene ?"
Rauda dake tsaye bayan ta dauke kanta tana tunanin me kuma ya kawo wannan gidansu ta dago yana kallonsa
Kwarai da ita yake,
Ke ? Menene? Eh lalle da ita yake , sai ta ji ba zata iya amsa shi ba ta sake dauke kanta da nufin ficewarta ta tafi suka ringa jiyo salama daga bakin kofa ta muryoyi masu dan yawa kuma maza ne
Gaban Rauda ne ya yanke ya fadi, daga tsayen da take sai ta matsa sosai ta yi ciki kadan dan ana amsawa masu salamar salamarsu ne Mama na fadin" To wai kuma su waye da daren nan Ni yau sai bakin mutane ke zuwar min!"
A tausashe Liman ya ce" Ba baki bane maman yara, su liman ne"
Itama sai ta samu kanta da yin tsittt kafin ta taho jiki ba kwari tana jin zuciyarta na dokawa jin su liman ne, su liman? Idan tana da tunani ba zata tuna yaushe liman ya taba sako ƙafarsa gidan nan ba, haka kuma ita dai ko a hanya ba abokin gaisawarta bane bale tace sunna gaisawa
Abu daya ta yi tunani an zo ne a mata nasiha da Umar dan kamar ai ana haka a anguwar sukan je dan wani tsirku su yiwa mace da mijinta nasiha ta rainin hankali, namijin dake zaune da matarsa bai isa ya mata nasiha ba sai sun je da wasu wandunansu tsalau tsalau wai sun zo nasiha
Tana fitowa bayan YUSUF ya fito ya ga harda iyayensa a yan shigowar da sauran mutanen da bai san su ba ama suma sunna ganninsa da mutuntawa sosai suka bashi hannu suka gaisa da daraja junna sai kuma ya ga fuskar mahaifiyarsa tamkar wace ta jike da hawaye nan take ya ji tamkar hankalinsa zai tashi, ama kuma ya yi iya yinsa ya dane yana kallon kowa ciki harda Rauda da ta fito da tabarma jin ana fadin a kawo tabarma, jikinta na rawa ta shinfida masu ta tsuguna tana bin ledar dake hannun Liman da kallo gabanta na ci gaba da faduwa
A tausashe Liman ya ce" Ina fatan na same ku lafiya, sannan ina baku hakurin zuwan da na yi maku a irin wannan lokacin"
Shiru ya yi yana neman dukan hanyar da ta dace ya sanar da abin dan shima hankalinsa a tashe yake sosai
A nutse suka karasa cikin anguwar har kofar gidan
Sunna tsayawa Aminu ya nuna masu gidan yana faɗin " Ga gidan nan sir, ama inaga shi uncle din nata baya gidan dan yanzu a masalaci liman na fada min ko na ganshi? Yace sau biyu tana zuwa nemansa wai tunda ya fita dazu ransa a bace"
Honorable ne ya dube shi da kula ya ce" Ransa a bace? Kwananta a wani wajen ya saka ransa bacewa ko ina iyayenta ne ko hutu ya zo wajen uncle din nata?"
A hankali Yusuf ya jinginar da bayansa jikin kujerar motar yana sauke dubansa daga kan Mahaifiyarsa dake kallonsu yana jin Aminu na maimaitawa Honorable cewar RAUDA marainiya ce gaba da baya a hannun uncle din nata take
Shiru wajen ya dauka, na tarin alhinin jin maganar ne ko mene?
A sanyaye Mah ta sauko kafarta daga cikin motar bayan ta bude ta ajiye wayarta baba tana fadin" Bari Ni na shiga ka ga idan yana nan din sai ya maku iso"
Haka kawai ta ji zuciyarta ta buga mata jin labarin yarinyar, sai ta ji bari ta shiga ko sa ga marikinta su sanar masa ga asalin inda ta kwana ta yiwu da akace ya fita hankalinsa tashe ya daina fushi ya yi hakuri
Da ido YUSUF ya bita har ta bude karamar kofar gidan ta shiga sannan ya dawo da dubansa kan Aminu dake dan yiwa Ana shinfidar wasu daga cikin abinda Rauda ke ganni a gidan rikon nata
Salama Maman Yusuf ke yi tana karawa, ama ba amsa, sai murya dake tashi sama sama da alwashi kala kala wanda ya sakata dakatawa a dole tana tunanin ta koma ne ko ta shiga?
Ta daga kafa da nufin shigewa ciki ta ji sama sama murya na fadin" Rauda idan har ubanki ya shanye giya da kudina nice ajalinsa, kuma kema nice ajalinki ki rubuta ki ajiye, munafuka algunguma, ki bani kudina nace , ki tashi du gidan ubanda kika san zaki je ki samo min kudina ki je ki samo idan ba haka ba na wulakanta ki na je na dauko dayan shegen na yanka shi!"
Hankalin Mah ne ya mugun tashi, da sauri ta juya har tana jin kafarta zata tashi na ciwo ta fito ta nufo mota tana haki
Da sauri YUSUF ya bude motar ya fito ya kamo hannayenta yana kallon yadda take haki hankalinta tashe, Abu ma dake tsaye shi da Aminu gefe sun nitsa a labarin Rauda da sauri ya karaso yana kamota ba wata wata ya rungumeta a jikinsa yana fadin" Hey Madame, menene, me ya faru?"
Hankali tashe har hannayenta na rawa ta fadi abinda ta ji da ta shiga, da sauri ta ce" Wacece RAUDA? Inace wajen yarinyar da muka zo ne , me ta yiwa Mamanta take fadin kalaman nan a kanta innalilahi Wa inna ilaihi raj'une"
A nutse ya mayar da hannunsa ya rufe motar ya juyo yana kallon mahaifinsa dake faman fada mata kar ta daga hankalinta ba komai bane bari ya shiga ya gani
A tausashe ya ce" Aba bari na shiga na gani"
Yana fada ya juya ya nufi hanyar shiga, da sauri Aminu ya biyo shi yana fadin" Biya Muradi da zaka yi hakuri na tabo wata mace ta shiga, ka san matar nan da sharin tsiya, gashi bata gannin girman kowa kar ta lika maka wani sharin a banza a wofi"
Murmushi YUSUF ya yi masa ya nausa kansa ciki yana salamar da ta zame masa jiki ciki ciki
Yana shigowa Farisa ga fito daga bayi ta gama aikata kashinta na magariba da ya zame mata jiki suka yi ido hudu
Ido ta zuba masa kafin da sauri ta dubi kafarta dake dauke da dati harda zannin jikinta, zannin da ta wuni da shi shekaran jiya da jiya ne , yau fa har zata cenza tace bari dai ya karra kwana biyu sai ta cenza dan bata kayanma ai ba kyau,sai gashi an yi rantsatsen bako?
Da sauri ta wuce shi ta yi cikin gidan har kamar zata kifa
Tana shiga ta ce" Mama, wa bilahilazi Balarabe a cikin gidanmu, Allah ka sa bakona ne , Allah Allah Farisa Allah amen"
Uwar dake daure da zani saman munafata ta dubeta itama yau din dai wankan nan bata yi shi ba, ta wuni a daki ko abinci bata ci ba ta ce" Balarabe kuma?, Farisa zan ci uban ubanki idan har baki daina kawo min shirme a yau ba, me zai kawo Balarabe anguwar nan dan ubanki?, ko wajen wannan ya zo ai ba zai shigo min gida ba ko?"
Da sauri ta tari uwar tana fadin" Allah ya sawaka ya zo wajenta ki ji kai mugun fata , kina ji ina adu'ar Allah ya sa wajena ya zo ki wani ce wajenta, ke Rauda gaskiya tashi ki shiga ciki kar ya ganki ki masa asirin da kika saba da munafukan idannuwan nan naki, Ni dai kuma kar ku bari ya gane ana neman baba Umaru gaskiya kar ku zubar min da mutincina!"
Magana take yi tamkar ta sako da sako, magana take yi ta rashin mutunci tana hantarar uwar da Raudar baki daya domin du ta gigice
Mikewa Rauda ta yi idannuwanta ko gannin kirki basa yi
Sama hijab ne a jikinta mai ruwan anta har kasa ama bashi da hannu ya dai kama fuskarta das ya fitar da zagayen fuskar nata, hakan ya sa fuskar ta fito fayau da ita sai lebenta da ya dan bushe da kuma idannuwanta da suka kara nutsewa suka yi luhu luhu
Niyarta ta sake komawa masalaci daga nan kuma ta nufi gidan giyar da yake zuwa, in dai yana cen shikenan sai ta dawo ta nutsu ta kuma ci gaba da yi masa addu'a, dan jikinta na bata mugun abin da ya ringa bata a ranar da zata iya kiran ranar da Azal ta fadawa ahalinta
Da sauri Farisa ta riko hijab din tana fadin" Rauda nace kar ki fita fa!"
Da kyar ta iya yiwa idannuwanta luuuuuuu ta bude bakinta ta fara magana ta ga an daga labule an shigo ama bata ga mai shigowar ba, a hargitse ta ce" Idan kika kuma taba min sutura da kazantar nan taki sai na karya maki hannu, idan kika kuma daga mun murya sai na janyo makogwaronki FARISA!"
Da sauri ta yi baya tana neman yin kusa da mamanta, dan ita ta sha'afa kan Wacece RAUDA ita kuma Mama tunda ta ga wanda ya shigo sai itama ta shiga kunce hijabin dake daure a kugunta tana kokarin sakin fuska ta ce" Barka da zuwa baki muka yi ne?"
A hankali Rauda ta juyo da niyar zagayesu ta fice idannuwanta suka sauka a kan fuskarsa ya zuba mata ido shima sannan ya dauke ya sake kallon hoton dake dakin daya kwal wanda kwarai ya san fuskar mutumen, ama a inda ya san mutumen a waje ne marar kyau, wajen da su mutanen suke kwalewa shi kuwa yakan je ne dan ya yi nasa kalar kwalewar shima
"Ba wajenki na zo ba" YUSUF ya fada a hade yana kaucewa daga nufo shin da Mama ta yi da kujera
A hade ya ce" Ke ?, menene ?"
Rauda dake tsaye bayan ta dauke kanta tana tunanin me kuma ya kawo wannan gidansu ta dago yana kallonsa
Kwarai da ita yake,
Ke ? Menene? Eh lalle da ita yake , sai ta ji ba zata iya amsa shi ba ta sake dauke kanta da nufin ficewarta ta tafi suka ringa jiyo salama daga bakin kofa ta muryoyi masu dan yawa kuma maza ne
Gaban Rauda ne ya yanke ya fadi, daga tsayen da take sai ta matsa sosai ta yi ciki kadan dan ana amsawa masu salamar salamarsu ne Mama na fadin" To wai kuma su waye da daren nan Ni yau sai bakin mutane ke zuwar min!"
A tausashe Liman ya ce" Ba baki bane maman yara, su liman ne"
Itama sai ta samu kanta da yin tsittt kafin ta taho jiki ba kwari tana jin zuciyarta na dokawa jin su liman ne, su liman? Idan tana da tunani ba zata tuna yaushe liman ya taba sako ƙafarsa gidan nan ba, haka kuma ita dai ko a hanya ba abokin gaisawarta bane bale tace sunna gaisawa
Abu daya ta yi tunani an zo ne a mata nasiha da Umar dan kamar ai ana haka a anguwar sukan je dan wani tsirku su yiwa mace da mijinta nasiha ta rainin hankali, namijin dake zaune da matarsa bai isa ya mata nasiha ba sai sun je da wasu wandunansu tsalau tsalau wai sun zo nasiha
Tana fitowa bayan YUSUF ya fito ya ga harda iyayensa a yan shigowar da sauran mutanen da bai san su ba ama suma sunna ganninsa da mutuntawa sosai suka bashi hannu suka gaisa da daraja junna sai kuma ya ga fuskar mahaifiyarsa tamkar wace ta jike da hawaye nan take ya ji tamkar hankalinsa zai tashi, ama kuma ya yi iya yinsa ya dane yana kallon kowa ciki harda Rauda da ta fito da tabarma jin ana fadin a kawo tabarma, jikinta na rawa ta shinfida masu ta tsuguna tana bin ledar dake hannun Liman da kallo gabanta na ci gaba da faduwa
A tausashe Liman ya ce" Ina fatan na same ku lafiya, sannan ina baku hakurin zuwan da na yi maku a irin wannan lokacin"
Shiru ya yi yana neman dukan hanyar da ta dace ya sanar da abin dan shima hankalinsa a tashe yake sosai