Sashe 110
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya ji komai, ya kuma fahimci komai, ama ya kasa cewa komai har suka karasa bangaren Hajia suka tarar da Mah a nan din a bangaren na Hajia, da duku dukun nan, hakan ya basu mamaki su duka, har ya sa ya karasa da sauri gabanta yana dukawa da kokarin duba jikinta yana gaisheta da tambayar menene ko lafiya? shi kuwa BAH ya dauke kansa ɗan ya san sarai abinda ya hannata barci har ta yi samakon nan ya kuma karra daurar niyar matse mata lamba har sai ta saduda da kanta ta nemi sulhu, ya gaji, ya gaji ainun da ganninta tana wahalar da kanta bayan Addinin Musulunci ba haka yake ba, addinin musulunci sauki ne da shi sosai, kuma Allahn da ya halicemu gafurun rahim ne
Hajia ta saka sandarta ta zunguri kansa tana fadin" Kai dilla in ka ganta a nan ai da kaffafuwanta ta zo , sai ka tambayi mai dakin ko nice na summa ta zo ko? kai dai akoy sarkafar uwa!"
YUSUF ya juyo yana kallonta ya tabe baki kasa kasa ya ce" Wai wani ko kece kika summa, kina nan zaune sai kashe min iyaye kike , an ki a duba kin da wani hijab dinta haba a karkace"
Mah ta saka carbi zata kwada masa da sauri ya karasa kusan Bah ya zauna yana harde hannayensa ya sakarwa Hajia harara wace ke dariya tana fadin" Ja'iri da ka tsaya mana ka ga yadda y'ata zata zane min kai"
Da raha sosai wajen ya fara, sannan suka koma jimamin lamarin nan, inda Hajia ta tabatar da abinda suka yanke ita da Bah, kuma Mah ta tabatar da ta yarda sannan shima ya tabatar da yana tare da abinda aka yanke din kafin ya mike ya nufi bangarensa, hakama Bah ya yi ficewarsa aka bar Mah da Hajia, Mah ta mike ta nufi kicin din Hajia dan ba zata koma bangarenta ba sai komai ya daidaita kuma
Yana komawa ya nufi dakin RAUDA kai tsaye, dan ya tabata bata dakinsa
A lokacin Rauda ta yi wanka tuni ta yi sallah ta shiga saka turare a dakin nata da nufin gamawa ta shige kicin dan ta sama masu abincin kari ta ji ana buga mata kofa
ta dan yi jim dan tunanin ko waye, hakan ya sa ta nufi kofar ta kama ta bude tana buɗe baki ta ce" Wa.............."
Sai kuma ta yi dif a hankali ta yi shiru tana kallonsa
Shigar jikinta ya fara bi da kallo, da kwalin idannuwanta da jan bakin da ta dan shafa madaidaici ya sauke dubansa a kan hannayenta da ta rungume a kirjinta tana kallonsa a hankali ya ce" Morning aunty"
Ido ta kwalalo tana sauke hannayenta da wata irin kunya ta sada kanta ta ce" Lah yayanmu, ban kai da gaisheka ba fa ina mamakin ganninka a nan ne ban san me ka zo yi ba yi hakuri yayanmu, ina kwana an tashi lafiya?"
Shigowa ya yi da kyau ya ce" An tashin dai, lafiya kuma ai sai na zama ango, abinda ya kawo Ni kuwa zance na zo "
"ikon Allah, innalilahi " Ta fada a hankali tana zagaye shi ta karasa ta dauko hijabinta ta karaso zata wuce
hannunta daya ya kama ya janyota a slow ta zo gabansa da dayan hannunsa ya saka ya tareta yana dage gira ya ce" Kar ki gogeni mana kato da Ni, ke wai daga bugawa sai ki wani bude ba hijab dan kin ganni ki saka hijab, to mamanki bata ce maki ba hijabi tsakanina da ke bane ko kallon katon kwarata kike min"
"Na shiga uku" Ta fada tana rintse ido
Ya sake tare fuskarta ya ce" Mun shi shiga uku dai, ina zaki je dan na zo sai kace kin ga mai kwasar zancenki?"
" kicin fa zan je yayanmu" Ta fada tana raraba kalmar, dan ya fara fin karfin ta walahi
"Mu je, ama ki ji tsoron Allah ki daina min halayar nan, sai in mance kece fa, ji wani yayanmu, wata magana a sanyaye bayan na san ba tsorona kike ji ba!" Ya fada yana juyar da ita ya nuna mata hanyar kicin din, a dole ta ja ta tsaya tana kallonsa yannayinta na nuni da rauninta a kansa, jiki ba karfi ta ce" Kicin fa na ce zan je?"
Da girarsa ya mata alamun eh sai me?, hakan ya sa a sanyaye ta ce" Kai Sarki ne YUSUF, me ya haɗaka da kicin? dan Allah ka yi hakuri idan yinwa kake ji yanzu yanzu zan kawo maka ko menene in sha Allah"
Fuskarta ya fara tsarewa da ido, sannan ya sauke duban a kan lebenta..............
Shi yasa ya guji sarauta............
Domin shi mutun ne da ya damu da ahali.......,
a lokacin da Bah ke nuna masa ya dace ya daina zuwa wajen Hajia da wajensa da Mah koda yaushe ya nuna masa shi yasa ya sa aka yi masa hanyoyin nan na baya.....domin ya rayu ne a haka, baya tunanin sarauta zata masa iyaka da iyayensa....uwa uba da RAUDA.
Bai san wani yare zai yiwa RAUDA a yanzu ba, abu daya tak ya sani shine idan kicin take zai iya zuwa ya bare mata tafarnuwa, idan mak'up zata yi yana iya rike mata jaka har a gama, yana iya tayata zabar sutura a shago idan hakan ta kama, yana iya tayata kada miya.........'..
Murmushi ya yi yana kallonta a hankali ya ce" Yinwa nake ji"
RAUDA ta sada dubanta daga nasa kasa kasa ta ce" Ohk, me zaka ci,me zan dafo?"
"You.................." Ya fada daga cen cikin makogwaronsa
A zabure ta kalle shi, tana ruko ido, hakan ya sa ya dan shafa kansa yana murmushi a hankali zai yi magana AMNAH dake nemansa a fujajan , har hanyar fita ta je dan ta je nemansa bangaren Mah Taj ya hannata fitar, shine ta nufo bangaren RAUDA duda zuciyarta na tabatar mata me zai yi a cen? Sai dai kiran da mahaifiyarta ta yi mata ya sa take neman nasa a fujajan dan so take ta je ta ji, wai an kawo samaci daga office din shugaban yan sanda ana neman iyayenta? ko lokacin hawa aikin bai gama cika ba ai, waye zai kai karar iyayenta ita a garin Tsatsunburum? ko waye bako ne, kuma shi shugaban yan sandan yau sai ta nuna masa sunne manyan garin, ta tabata dan bai san ita ke auren MALEEK bane ya kawo wannan gangancin, sai dai tana zuwa ta gansu a irin tsayuwar nan, da kuma irin yadda murmushi ke fita a fuskarsa
Maganarta ke neman bacewa a bakinta, ta kai ruwa ta kai mari ya fi a irga bale da ta ga ya zuba mata ido yana jiran ji daga bakinta hakama Rauda da ta juyo har sai da bayanta ya hadu da kirjinsa ta dan matso gana kadan ita dinma tana kallon Amnah din da jiran jin abinda ya kawo ta har nan wajen
AMNAH ta rintse idannuwanta saboda kanta da ya sarra, ta dantse lebenta ta sake saka idonta a cikin nasa
da kyar ta iya kankaro magana a bakinta harufan ba kaifi ta ce"
Duk yadda ta so yin tamkar bata ga RAUDA ba abin gagarar idannuwanta ya yi da bakinta, duk yadda ta so sharewa ta nuna wajen mijinta ta zo ta gaza hakan, har ta kasa tankwasa harshenta tana duban RAUDA da manta abinda ya shiga tsakaninsu saboda kishin dake ranta nata ta ce" Me kike yi a nan da mijina?"
RAUDA ta sake zuba mata tana kallonta, a zuciyarta kuwa tana ta maimaita adu'ar da ta koyawa kanta a kan lamarin Amnah, domin ta zauna ta yi wani dogon tunani dan ta gano menene wutar tsanar dake ruruwa a zuciyarta a kan Amnah, me ta yi mata da zafi bayan zagin rashin kunyar da rashin tarbiyyar da ta nuna mata bata samu ba a gidansu? ta gane daga su din dai sai auren wannan bawa ta ga gama yarda cewar shi din gagarumar rikicin rayuwarta ne, shi yasa ta zauna ta yiwa kanta shawarar in sha Allah zata koyi dauke kanta a kan wannan matar domin bata tunanin in har tace zata ci gaba da biye mata zasu haifi d'a mai ido, irin yadda idan ta riki wuyanta take ji a ranta bata so ta saki kar wata rana aikin gangan ya kaita aikata dana sani a kan abinda yake nata itama kuma halalinta
tinowa da ta yi natan ne halalinta ya sa ta ji zuciyarta na son daukan zafi da shi bayan yanzu yanzu tamkar ta fito masa a mutun ta sanar masa labarin zuciyarta, a kallon nan da suka yiwa junna a ranta babu abinda bata ayana na tarin kaunarsa da muradin sanar masa ba
Cire kanta ta yi a kansu baki daya bayan ta yi masu kallon tare sannan ta juya da nufin tafiyarta
Ya jima da gane karatun yarinyar nan koda da harara ta yi shi, hakan ya sa ya kasa kyaleta ta tafin ya riko hannunta ya dawo da ita yana kallon Amnah a tausashe ya ce" Amnah, yaya zaki fadi magana irin wannan?, Rauda fa matata ce, ko a dakina kika ganta ta zo dakin mijinta ne bale nan din dakinta ne fa"
A tausashe ya yi maganar, ama sai da ya sa hawaye suka taru a cikin idannuwanta,
hannayensu ta bi da kallo ta sake dora dubanta a kansa, matarsa? har fadi yake yi wai wannan yarinyar mai fada kamar mahaukaciya ce matarsa? ai walahi ko zata tafi tsirara sai ta raba auren nan nasu, ai wannan ba sa'ar su jera bace Bama bale ace su yi kishi, banza da ita!
Itama a tausashen sai dai tana wani daga ido ta ce" Magana nake so mu yi"
YUSUF ya sake riƙe hannun RAUDA dake son janyewa ta tafi, dan bata son abinda zai kuma hadata da wannan mai uwa da uban, salon a tabata kadan ta tarawa mutane iyayenta , ita kuwa da nata basa duniya sai dai ta kalle su ko? Allah ya sa Allah ke bada uwa da uba, ita marainiyar itama ya bata masu hankali da tunani ma kuwa
"Bismillah, ko mu karasa mu zauna?" Ya fada a tausashe yana jan hannun RAUDA ya nufi kujerar ta
Hajia ta saka sandarta ta zunguri kansa tana fadin" Kai dilla in ka ganta a nan ai da kaffafuwanta ta zo , sai ka tambayi mai dakin ko nice na summa ta zo ko? kai dai akoy sarkafar uwa!"
YUSUF ya juyo yana kallonta ya tabe baki kasa kasa ya ce" Wai wani ko kece kika summa, kina nan zaune sai kashe min iyaye kike , an ki a duba kin da wani hijab dinta haba a karkace"
Mah ta saka carbi zata kwada masa da sauri ya karasa kusan Bah ya zauna yana harde hannayensa ya sakarwa Hajia harara wace ke dariya tana fadin" Ja'iri da ka tsaya mana ka ga yadda y'ata zata zane min kai"
Da raha sosai wajen ya fara, sannan suka koma jimamin lamarin nan, inda Hajia ta tabatar da abinda suka yanke ita da Bah, kuma Mah ta tabatar da ta yarda sannan shima ya tabatar da yana tare da abinda aka yanke din kafin ya mike ya nufi bangarensa, hakama Bah ya yi ficewarsa aka bar Mah da Hajia, Mah ta mike ta nufi kicin din Hajia dan ba zata koma bangarenta ba sai komai ya daidaita kuma
Yana komawa ya nufi dakin RAUDA kai tsaye, dan ya tabata bata dakinsa
A lokacin Rauda ta yi wanka tuni ta yi sallah ta shiga saka turare a dakin nata da nufin gamawa ta shige kicin dan ta sama masu abincin kari ta ji ana buga mata kofa
ta dan yi jim dan tunanin ko waye, hakan ya sa ta nufi kofar ta kama ta bude tana buɗe baki ta ce" Wa.............."
Sai kuma ta yi dif a hankali ta yi shiru tana kallonsa
Shigar jikinta ya fara bi da kallo, da kwalin idannuwanta da jan bakin da ta dan shafa madaidaici ya sauke dubansa a kan hannayenta da ta rungume a kirjinta tana kallonsa a hankali ya ce" Morning aunty"
Ido ta kwalalo tana sauke hannayenta da wata irin kunya ta sada kanta ta ce" Lah yayanmu, ban kai da gaisheka ba fa ina mamakin ganninka a nan ne ban san me ka zo yi ba yi hakuri yayanmu, ina kwana an tashi lafiya?"
Shigowa ya yi da kyau ya ce" An tashin dai, lafiya kuma ai sai na zama ango, abinda ya kawo Ni kuwa zance na zo "
"ikon Allah, innalilahi " Ta fada a hankali tana zagaye shi ta karasa ta dauko hijabinta ta karaso zata wuce
hannunta daya ya kama ya janyota a slow ta zo gabansa da dayan hannunsa ya saka ya tareta yana dage gira ya ce" Kar ki gogeni mana kato da Ni, ke wai daga bugawa sai ki wani bude ba hijab dan kin ganni ki saka hijab, to mamanki bata ce maki ba hijabi tsakanina da ke bane ko kallon katon kwarata kike min"
"Na shiga uku" Ta fada tana rintse ido
Ya sake tare fuskarta ya ce" Mun shi shiga uku dai, ina zaki je dan na zo sai kace kin ga mai kwasar zancenki?"
" kicin fa zan je yayanmu" Ta fada tana raraba kalmar, dan ya fara fin karfin ta walahi
"Mu je, ama ki ji tsoron Allah ki daina min halayar nan, sai in mance kece fa, ji wani yayanmu, wata magana a sanyaye bayan na san ba tsorona kike ji ba!" Ya fada yana juyar da ita ya nuna mata hanyar kicin din, a dole ta ja ta tsaya tana kallonsa yannayinta na nuni da rauninta a kansa, jiki ba karfi ta ce" Kicin fa na ce zan je?"
Da girarsa ya mata alamun eh sai me?, hakan ya sa a sanyaye ta ce" Kai Sarki ne YUSUF, me ya haɗaka da kicin? dan Allah ka yi hakuri idan yinwa kake ji yanzu yanzu zan kawo maka ko menene in sha Allah"
Fuskarta ya fara tsarewa da ido, sannan ya sauke duban a kan lebenta..............
Shi yasa ya guji sarauta............
Domin shi mutun ne da ya damu da ahali.......,
a lokacin da Bah ke nuna masa ya dace ya daina zuwa wajen Hajia da wajensa da Mah koda yaushe ya nuna masa shi yasa ya sa aka yi masa hanyoyin nan na baya.....domin ya rayu ne a haka, baya tunanin sarauta zata masa iyaka da iyayensa....uwa uba da RAUDA.
Bai san wani yare zai yiwa RAUDA a yanzu ba, abu daya tak ya sani shine idan kicin take zai iya zuwa ya bare mata tafarnuwa, idan mak'up zata yi yana iya rike mata jaka har a gama, yana iya tayata zabar sutura a shago idan hakan ta kama, yana iya tayata kada miya.........'..
Murmushi ya yi yana kallonta a hankali ya ce" Yinwa nake ji"
RAUDA ta sada dubanta daga nasa kasa kasa ta ce" Ohk, me zaka ci,me zan dafo?"
"You.................." Ya fada daga cen cikin makogwaronsa
A zabure ta kalle shi, tana ruko ido, hakan ya sa ya dan shafa kansa yana murmushi a hankali zai yi magana AMNAH dake nemansa a fujajan , har hanyar fita ta je dan ta je nemansa bangaren Mah Taj ya hannata fitar, shine ta nufo bangaren RAUDA duda zuciyarta na tabatar mata me zai yi a cen? Sai dai kiran da mahaifiyarta ta yi mata ya sa take neman nasa a fujajan dan so take ta je ta ji, wai an kawo samaci daga office din shugaban yan sanda ana neman iyayenta? ko lokacin hawa aikin bai gama cika ba ai, waye zai kai karar iyayenta ita a garin Tsatsunburum? ko waye bako ne, kuma shi shugaban yan sandan yau sai ta nuna masa sunne manyan garin, ta tabata dan bai san ita ke auren MALEEK bane ya kawo wannan gangancin, sai dai tana zuwa ta gansu a irin tsayuwar nan, da kuma irin yadda murmushi ke fita a fuskarsa
Maganarta ke neman bacewa a bakinta, ta kai ruwa ta kai mari ya fi a irga bale da ta ga ya zuba mata ido yana jiran ji daga bakinta hakama Rauda da ta juyo har sai da bayanta ya hadu da kirjinsa ta dan matso gana kadan ita dinma tana kallon Amnah din da jiran jin abinda ya kawo ta har nan wajen
AMNAH ta rintse idannuwanta saboda kanta da ya sarra, ta dantse lebenta ta sake saka idonta a cikin nasa
da kyar ta iya kankaro magana a bakinta harufan ba kaifi ta ce"
Duk yadda ta so yin tamkar bata ga RAUDA ba abin gagarar idannuwanta ya yi da bakinta, duk yadda ta so sharewa ta nuna wajen mijinta ta zo ta gaza hakan, har ta kasa tankwasa harshenta tana duban RAUDA da manta abinda ya shiga tsakaninsu saboda kishin dake ranta nata ta ce" Me kike yi a nan da mijina?"
RAUDA ta sake zuba mata tana kallonta, a zuciyarta kuwa tana ta maimaita adu'ar da ta koyawa kanta a kan lamarin Amnah, domin ta zauna ta yi wani dogon tunani dan ta gano menene wutar tsanar dake ruruwa a zuciyarta a kan Amnah, me ta yi mata da zafi bayan zagin rashin kunyar da rashin tarbiyyar da ta nuna mata bata samu ba a gidansu? ta gane daga su din dai sai auren wannan bawa ta ga gama yarda cewar shi din gagarumar rikicin rayuwarta ne, shi yasa ta zauna ta yiwa kanta shawarar in sha Allah zata koyi dauke kanta a kan wannan matar domin bata tunanin in har tace zata ci gaba da biye mata zasu haifi d'a mai ido, irin yadda idan ta riki wuyanta take ji a ranta bata so ta saki kar wata rana aikin gangan ya kaita aikata dana sani a kan abinda yake nata itama kuma halalinta
tinowa da ta yi natan ne halalinta ya sa ta ji zuciyarta na son daukan zafi da shi bayan yanzu yanzu tamkar ta fito masa a mutun ta sanar masa labarin zuciyarta, a kallon nan da suka yiwa junna a ranta babu abinda bata ayana na tarin kaunarsa da muradin sanar masa ba
Cire kanta ta yi a kansu baki daya bayan ta yi masu kallon tare sannan ta juya da nufin tafiyarta
Ya jima da gane karatun yarinyar nan koda da harara ta yi shi, hakan ya sa ya kasa kyaleta ta tafin ya riko hannunta ya dawo da ita yana kallon Amnah a tausashe ya ce" Amnah, yaya zaki fadi magana irin wannan?, Rauda fa matata ce, ko a dakina kika ganta ta zo dakin mijinta ne bale nan din dakinta ne fa"
A tausashe ya yi maganar, ama sai da ya sa hawaye suka taru a cikin idannuwanta,
hannayensu ta bi da kallo ta sake dora dubanta a kansa, matarsa? har fadi yake yi wai wannan yarinyar mai fada kamar mahaukaciya ce matarsa? ai walahi ko zata tafi tsirara sai ta raba auren nan nasu, ai wannan ba sa'ar su jera bace Bama bale ace su yi kishi, banza da ita!
Itama a tausashen sai dai tana wani daga ido ta ce" Magana nake so mu yi"
YUSUF ya sake riƙe hannun RAUDA dake son janyewa ta tafi, dan bata son abinda zai kuma hadata da wannan mai uwa da uban, salon a tabata kadan ta tarawa mutane iyayenta , ita kuwa da nata basa duniya sai dai ta kalle su ko? Allah ya sa Allah ke bada uwa da uba, ita marainiyar itama ya bata masu hankali da tunani ma kuwa
"Bismillah, ko mu karasa mu zauna?" Ya fada a tausashe yana jan hannun RAUDA ya nufi kujerar ta