Sashe 27
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri Rauda ta karaso tana kallonta, jiki ba karfi da kuma tashin hankalin menene wannan din kuma ta ce" Hajia, lafiya?"
Mah ta kalli Rauda ta sauri dan har ta fara manta tare suke tsabar tashin hankali
Da sauri ta mika mata wayar tana fadin" Dan Allah, cire min cod ki saka min numbobin nan da zan fada maki ki min kiransu, dan Allah yata"
Wayar ta amsa tana kallon yannayin Mah,
A hankali ya kamma hannun na Mah ta zaunar da ita saman kujera tana kallonta a sanyaye ta ce" Mama, ki yi hakuri, ki fada min numbar na bude maki, ama ki yi hakuri ko menene kin ji?"
Mah dai so take kawai ta bude mata ta kira mata numbar, dan haka ta shiga fada mata cod dinsa har ta cire mata sannan ta shiga fada mata numbar Honorable
Tana fara rubuta numbar sunnan ya nuna kansa da sunnan *UBANA* , ta karanta sunnan ta karra sannan ta danna kiran ta mikawa Mama ta zauna tana kallonta, dan sai ta ji anya kuwa zata iya tafiya ta barta a wannan yannayin?
Wayar ba fara ringin ya daga, muryarsa wata iri a sanyaye sosai ya ce" Yusuf kun karasa wajen?"
Muryarta na rawa ta ce" Aban YUSUF, Yusuf din baya nan ai, ban san ina ya je ba, gashi ya kawo mu gidan nan na jeji kuma ya fita, ya bar min wayarsa harda su katinsa na shedar dan kasa, ina ya je? Me yake faruwa a fadar dan girman Allah? Ka fada min walahi zuciyata bugawa zata yi"
Rauda ta kawar da kanta dan bata so ta maida hankali kan maganar Maman, ama kuma haka kawai ta samu kanta da maimaita FADA a cikin zuciyarta
"ya Salam, ya Salam, ya Salam" Honorable ya fada yana mikewa ya fice daga cikin mutane ya nufi cen bangaren matansa dan ba kowa a irin wannan lokacin , kowa yana ɓangaren Hajia tare da marar lafiyar
Yana zuwa ya sake rage muryarsa sosai ya ce" Sai fa da na fada masa ,kar ya saki ya fito, Allah kadai ya san gawar fari cikin mu da sarki da shi Yusuf, ama Hajia na gannin jikin sarki ta rikice ta ce in sanar da Yusuf in yana ina ya je gidan nan ya zauna har sai Allah ya yi yadda ya yi ji sarki ya mike ko akasinsa sai ta bada umarnin Yusuf ya fito zai fito, shine ya fito?"
A rikice Mah ta ce" Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, me yake damun Sarkin? Me yasa baka fada min ba Ni ai da ka san na rike Yusuf duk abinsa ba zai fita ba ko? Wayo na shiga uku yanzu yaya zan yi?"
Shi dinma hankalin nasa a tashen yake ya ce" kin ga ki kwontar da hankalin ki, in sha Allah ba komai, wai sarki bashi da lafiya tun shekaran jiya yake cikin gudawa da amai matan suka rufe suka ki fada min, sai da Hajia ta matsa kan ko ina yake a kira mata shi ne amaryarsa ta zo a sace ta fada mata walahi bashi da lafiya bakina san wanda yake kansa ba, Hajia baba ta hanna a sanarwa kowa sai magani ake didika masa a boye wai ko zai tashi ya zamto sai sun wanke shi sun cenza masa tufafi dan baya jin fitar gudawar daga jikinsa, shine fa Hajia ta yi kirana ta sanar min, da na zo ban nemi kowa ba na je bangaren nasa na bude na shiga da karfi dan kiri kiri Hajia baba ta nunan yana hutawa baya so a dame shi, da na shiga na tarda shi yana cikin wani hali, dan ko gudawar yanzu ba abinda ke fita sai ruwa tsululu, karshema malamai ne kansa ana ta addu'a, na yi na yi a je asibiti kowa ya wani nuna min wai me za'a kai"
Wani irin Gwauron numfashi Mah ta sauke kirjinta na dokawa
Ta rasa me zata ce,
Ya Salam wannan lamari na tsoratata yana kuma daga mata hankali
A me aka ɗauki sarauta ne?
Me suka dauki duniya ne?
A sanyaye hawaye na bale mata ta ce" Ai ba Yusuf ne abin a boye ba, kai ka san in dai abinda Hajia take nufi ne kaine abin a boye ba YUSUF dina ba, su cire Yusuf a duk wani abinda suke tunani, su fida d'ana daga rikicinsu, Aban Yusuf ka san ba zai taba yarda ya zauna kai kana cen din ba ko? Dan Allah ka fito Ku zo"
"Kar ki daga hankalinki, bari yanzu in fita in gani zan ganshi na dawo da shi, Ni sam bana son fitinar nan ta gidanmu, gashi dare ya yi ama kowa sai wani irin abu yake yi, kar ki daga min hankalinki dan Allah, gan.............."
"Yaya, ka fa zo, Hajia na kira" AISHA TA fada sama sama sannan ta juya da sauri ta koma
A dole ya katse kiran yana karra tabatarwa maman Yusuf cewar gayanan zuwa, kar ta daga hankalinta plz
A lokacin da ya shigo falon Hajia, inda sarki ke kwonce, matansa na nan a dole a irin wannan lokacin, da baban malamin masallacin gidan na zaune daf da shi sosai yana maimaita kalmar shahada, hakan ya sa gabansa ya yanke ya fadi kansa ya sara da sauri ya kai dubansa wajen Hajia inda take zaune kanta a kasa da carbinta tana ja idannuwanta a rintse tana ta ambaton sunnan Allah, dan a irin wannan lokacin ko waye kai dole zaka ji tsoron wanda ya isa ya busa kuma ya janye numfashin bawa, domin kakari na fitar rai shine ya cika falon, duk irin musun da uwar gidansa ke yi bakinta ya mutu ta kafe shi da kallo ta gaza furta koda a, sauran dake zaune kuwa an umarce su su masa addu'a ko su fita dan ba'a bukatar kowa ya daga murya a wajen
Sosai kirjinsa ke dokawa ya karaso da sauri ya duka ya rike hannun dan uwansa, wanda ya zamo tamkar ya dafa wani abu marar kasashi, kamar ba tsokar naman mutun ba mai dauke da kasusuwa da nama da jini, a hankali ya amshi hailalar da ake ta maimaita masa idannuwansa na kallon wajen da ya zarce tsayuwar dan Adam, sannu a hankali har yannayin dan rike hannun dan uwansa da ya yi ya saka baki daya hannunsa ya yi nauyi a hannun mahaifin Yusuf
Jiki ba laka ya sake damke hannun, wasu irin hawaye suka taru a cikin idannuwansa suka shiga zubowa a hankali saman kuncinsa ya gaza dagowa kunnayensa na jiyo masa furucin malan na sanar da sako mafi dukan zuciyar mahaifiya, Mata, ya'ya, yan uwa, dangi, da jama'ar gari baki daya, cewa RAI YA YI HALINSA
Kukan matan ne ya nemi hargitsa masa kwakwaluwa ya ringa jin tamkar ciwon shanyewar barin jiki zai kama shi, a birkice ya dago dubansa yana jin duhu zai mamaye shi, jiki ba karfi ya kama da kyar ya mike ama ina, abin ya zo masa kai tsaye kuma a irin lokacin da bai shirya ko tsamaci haka ba, duk da ita dama MUTUWA takenta kennan, bata zuwa a lokacin da ake tsumayinta dukda babu bawan dake zama yace zo na shirya sai wanda yake cikin halin yau i yau!, Mutuwa dai wannan mai tonon asiri a yau ta dauka, ta katse jin dadin Dubai zata nada na dubai, ta katse shan wahalar Dubai zata dora ta Dubai, mutuwa mai yanke dukan wani farin ciki ko nau'in wahala, a daidai lokacin da ya yi baya zai zube A'isha ta mike ta zuba masa ido abinda ke zuciyarta na zuciyarta, mahaifiyarta ta yi ta yi ta tashi dan ta agaji wanda take yiwa kallon shi ya rage a matsayin wanda zai hau kujerar dan uwansa ko salon kidan ya cenza domin idan har babu ɗaya tsayaye sarauta zata koma hannun kannin riga ana ji ana gani, a lokacin ne kuma Yusuf ya karaso jiki ba laka dan tun a kofa kunnayensa suke jiyo masa hargitsewar da masarautar ta dauka , a dole ya karaso yana jin gaba daya komai ya fice masa a rai, hankalinsa ya tashi, tashin hankali kala kala ya ziyarce shi, ciki harda tunanin mahaifinsa da abinda ke iya damun uban nasa
Da sauri ya karasa wajen da liman ya kama mahaifinsa yana masa sannu da nasiha irin wace ake yiwa wanda ya yi rashi ya zaunar da shi daf da mamacin wanda aka rufawa zanin gado sabo dal aka kuma tsawatarwa matan dake kuka kamar zasu tada dakin da hayaniyar kukansu
A hankali ya kai hwuiwoyinsa kasa, ya kama hannayen mahaifinsa ya zuba masa ido, a tausashe sosai ya ce" KA yi hakuri Abu, kar ka daga min hankali fiye da halin da nake ciki a yanzu dan Allah"
dumin hannunsa dake shiga cikin nasa ya saka shi jimke hannun da karfi sosai hawayensa na ci gaba da zuba tamkar an bude pampo
Hajia ta share hawaye a sanyaye bayan ta gama waya da asibiti ta dubi wajen da su YUSUF suke a tausashe ta ce" Ku ne alwalinsa, kunne ja gabarsa, Allah ya masa rahama, ku yi masa shinfida mai kyau, yanzu za'a zo a bashi kulawar da ta dace sai a kwana ana masa sauka, Allah ya jikan ka uban talakawa...."
Ta karshe muryarta na rawa sosai wani hawayen na sake bale mata, da kyar ta sake sharewa tana kallon Aban Yusuf da ya karaso da taimakawar Yusuf ya duka a gabanta ya kama hannayenta, kwarai shi ya dan irin radadin da take ji, shi ya san Wacece ita, tun sunna yara sukan yi mamakin jarumcinta, ama mahaifinsu ya taba fada masu, tsarin Sarautar garinsu dole sai da jajirtaciyar mace irinta, dan kuwa a gobe gobe da safe da zarar an birne mamacin za'a naɗa wani sarkin a ci gaba da zaman amsar gaisuwa, abinda zai zamo rikici na mamaki idan har akoy masu harin kujerar, kujera kuwa tabas akoy masu harinta na wajen gida da na cikin gida
A sanyaye ya ce" Ba zaki yi kuka sosai ba? Bana so abubuwa na dira maki a zuciya Hajia"
Mah ta kalli Rauda ta sauri dan har ta fara manta tare suke tsabar tashin hankali
Da sauri ta mika mata wayar tana fadin" Dan Allah, cire min cod ki saka min numbobin nan da zan fada maki ki min kiransu, dan Allah yata"
Wayar ta amsa tana kallon yannayin Mah,
A hankali ya kamma hannun na Mah ta zaunar da ita saman kujera tana kallonta a sanyaye ta ce" Mama, ki yi hakuri, ki fada min numbar na bude maki, ama ki yi hakuri ko menene kin ji?"
Mah dai so take kawai ta bude mata ta kira mata numbar, dan haka ta shiga fada mata cod dinsa har ta cire mata sannan ta shiga fada mata numbar Honorable
Tana fara rubuta numbar sunnan ya nuna kansa da sunnan *UBANA* , ta karanta sunnan ta karra sannan ta danna kiran ta mikawa Mama ta zauna tana kallonta, dan sai ta ji anya kuwa zata iya tafiya ta barta a wannan yannayin?
Wayar ba fara ringin ya daga, muryarsa wata iri a sanyaye sosai ya ce" Yusuf kun karasa wajen?"
Muryarta na rawa ta ce" Aban YUSUF, Yusuf din baya nan ai, ban san ina ya je ba, gashi ya kawo mu gidan nan na jeji kuma ya fita, ya bar min wayarsa harda su katinsa na shedar dan kasa, ina ya je? Me yake faruwa a fadar dan girman Allah? Ka fada min walahi zuciyata bugawa zata yi"
Rauda ta kawar da kanta dan bata so ta maida hankali kan maganar Maman, ama kuma haka kawai ta samu kanta da maimaita FADA a cikin zuciyarta
"ya Salam, ya Salam, ya Salam" Honorable ya fada yana mikewa ya fice daga cikin mutane ya nufi cen bangaren matansa dan ba kowa a irin wannan lokacin , kowa yana ɓangaren Hajia tare da marar lafiyar
Yana zuwa ya sake rage muryarsa sosai ya ce" Sai fa da na fada masa ,kar ya saki ya fito, Allah kadai ya san gawar fari cikin mu da sarki da shi Yusuf, ama Hajia na gannin jikin sarki ta rikice ta ce in sanar da Yusuf in yana ina ya je gidan nan ya zauna har sai Allah ya yi yadda ya yi ji sarki ya mike ko akasinsa sai ta bada umarnin Yusuf ya fito zai fito, shine ya fito?"
A rikice Mah ta ce" Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, me yake damun Sarkin? Me yasa baka fada min ba Ni ai da ka san na rike Yusuf duk abinsa ba zai fita ba ko? Wayo na shiga uku yanzu yaya zan yi?"
Shi dinma hankalin nasa a tashen yake ya ce" kin ga ki kwontar da hankalin ki, in sha Allah ba komai, wai sarki bashi da lafiya tun shekaran jiya yake cikin gudawa da amai matan suka rufe suka ki fada min, sai da Hajia ta matsa kan ko ina yake a kira mata shi ne amaryarsa ta zo a sace ta fada mata walahi bashi da lafiya bakina san wanda yake kansa ba, Hajia baba ta hanna a sanarwa kowa sai magani ake didika masa a boye wai ko zai tashi ya zamto sai sun wanke shi sun cenza masa tufafi dan baya jin fitar gudawar daga jikinsa, shine fa Hajia ta yi kirana ta sanar min, da na zo ban nemi kowa ba na je bangaren nasa na bude na shiga da karfi dan kiri kiri Hajia baba ta nunan yana hutawa baya so a dame shi, da na shiga na tarda shi yana cikin wani hali, dan ko gudawar yanzu ba abinda ke fita sai ruwa tsululu, karshema malamai ne kansa ana ta addu'a, na yi na yi a je asibiti kowa ya wani nuna min wai me za'a kai"
Wani irin Gwauron numfashi Mah ta sauke kirjinta na dokawa
Ta rasa me zata ce,
Ya Salam wannan lamari na tsoratata yana kuma daga mata hankali
A me aka ɗauki sarauta ne?
Me suka dauki duniya ne?
A sanyaye hawaye na bale mata ta ce" Ai ba Yusuf ne abin a boye ba, kai ka san in dai abinda Hajia take nufi ne kaine abin a boye ba YUSUF dina ba, su cire Yusuf a duk wani abinda suke tunani, su fida d'ana daga rikicinsu, Aban Yusuf ka san ba zai taba yarda ya zauna kai kana cen din ba ko? Dan Allah ka fito Ku zo"
"Kar ki daga hankalinki, bari yanzu in fita in gani zan ganshi na dawo da shi, Ni sam bana son fitinar nan ta gidanmu, gashi dare ya yi ama kowa sai wani irin abu yake yi, kar ki daga min hankalinki dan Allah, gan.............."
"Yaya, ka fa zo, Hajia na kira" AISHA TA fada sama sama sannan ta juya da sauri ta koma
A dole ya katse kiran yana karra tabatarwa maman Yusuf cewar gayanan zuwa, kar ta daga hankalinta plz
A lokacin da ya shigo falon Hajia, inda sarki ke kwonce, matansa na nan a dole a irin wannan lokacin, da baban malamin masallacin gidan na zaune daf da shi sosai yana maimaita kalmar shahada, hakan ya sa gabansa ya yanke ya fadi kansa ya sara da sauri ya kai dubansa wajen Hajia inda take zaune kanta a kasa da carbinta tana ja idannuwanta a rintse tana ta ambaton sunnan Allah, dan a irin wannan lokacin ko waye kai dole zaka ji tsoron wanda ya isa ya busa kuma ya janye numfashin bawa, domin kakari na fitar rai shine ya cika falon, duk irin musun da uwar gidansa ke yi bakinta ya mutu ta kafe shi da kallo ta gaza furta koda a, sauran dake zaune kuwa an umarce su su masa addu'a ko su fita dan ba'a bukatar kowa ya daga murya a wajen
Sosai kirjinsa ke dokawa ya karaso da sauri ya duka ya rike hannun dan uwansa, wanda ya zamo tamkar ya dafa wani abu marar kasashi, kamar ba tsokar naman mutun ba mai dauke da kasusuwa da nama da jini, a hankali ya amshi hailalar da ake ta maimaita masa idannuwansa na kallon wajen da ya zarce tsayuwar dan Adam, sannu a hankali har yannayin dan rike hannun dan uwansa da ya yi ya saka baki daya hannunsa ya yi nauyi a hannun mahaifin Yusuf
Jiki ba laka ya sake damke hannun, wasu irin hawaye suka taru a cikin idannuwansa suka shiga zubowa a hankali saman kuncinsa ya gaza dagowa kunnayensa na jiyo masa furucin malan na sanar da sako mafi dukan zuciyar mahaifiya, Mata, ya'ya, yan uwa, dangi, da jama'ar gari baki daya, cewa RAI YA YI HALINSA
Kukan matan ne ya nemi hargitsa masa kwakwaluwa ya ringa jin tamkar ciwon shanyewar barin jiki zai kama shi, a birkice ya dago dubansa yana jin duhu zai mamaye shi, jiki ba karfi ya kama da kyar ya mike ama ina, abin ya zo masa kai tsaye kuma a irin lokacin da bai shirya ko tsamaci haka ba, duk da ita dama MUTUWA takenta kennan, bata zuwa a lokacin da ake tsumayinta dukda babu bawan dake zama yace zo na shirya sai wanda yake cikin halin yau i yau!, Mutuwa dai wannan mai tonon asiri a yau ta dauka, ta katse jin dadin Dubai zata nada na dubai, ta katse shan wahalar Dubai zata dora ta Dubai, mutuwa mai yanke dukan wani farin ciki ko nau'in wahala, a daidai lokacin da ya yi baya zai zube A'isha ta mike ta zuba masa ido abinda ke zuciyarta na zuciyarta, mahaifiyarta ta yi ta yi ta tashi dan ta agaji wanda take yiwa kallon shi ya rage a matsayin wanda zai hau kujerar dan uwansa ko salon kidan ya cenza domin idan har babu ɗaya tsayaye sarauta zata koma hannun kannin riga ana ji ana gani, a lokacin ne kuma Yusuf ya karaso jiki ba laka dan tun a kofa kunnayensa suke jiyo masa hargitsewar da masarautar ta dauka , a dole ya karaso yana jin gaba daya komai ya fice masa a rai, hankalinsa ya tashi, tashin hankali kala kala ya ziyarce shi, ciki harda tunanin mahaifinsa da abinda ke iya damun uban nasa
Da sauri ya karasa wajen da liman ya kama mahaifinsa yana masa sannu da nasiha irin wace ake yiwa wanda ya yi rashi ya zaunar da shi daf da mamacin wanda aka rufawa zanin gado sabo dal aka kuma tsawatarwa matan dake kuka kamar zasu tada dakin da hayaniyar kukansu
A hankali ya kai hwuiwoyinsa kasa, ya kama hannayen mahaifinsa ya zuba masa ido, a tausashe sosai ya ce" KA yi hakuri Abu, kar ka daga min hankali fiye da halin da nake ciki a yanzu dan Allah"
dumin hannunsa dake shiga cikin nasa ya saka shi jimke hannun da karfi sosai hawayensa na ci gaba da zuba tamkar an bude pampo
Hajia ta share hawaye a sanyaye bayan ta gama waya da asibiti ta dubi wajen da su YUSUF suke a tausashe ta ce" Ku ne alwalinsa, kunne ja gabarsa, Allah ya masa rahama, ku yi masa shinfida mai kyau, yanzu za'a zo a bashi kulawar da ta dace sai a kwana ana masa sauka, Allah ya jikan ka uban talakawa...."
Ta karshe muryarta na rawa sosai wani hawayen na sake bale mata, da kyar ta sake sharewa tana kallon Aban Yusuf da ya karaso da taimakawar Yusuf ya duka a gabanta ya kama hannayenta, kwarai shi ya dan irin radadin da take ji, shi ya san Wacece ita, tun sunna yara sukan yi mamakin jarumcinta, ama mahaifinsu ya taba fada masu, tsarin Sarautar garinsu dole sai da jajirtaciyar mace irinta, dan kuwa a gobe gobe da safe da zarar an birne mamacin za'a naɗa wani sarkin a ci gaba da zaman amsar gaisuwa, abinda zai zamo rikici na mamaki idan har akoy masu harin kujerar, kujera kuwa tabas akoy masu harinta na wajen gida da na cikin gida
A sanyaye ya ce" Ba zaki yi kuka sosai ba? Bana so abubuwa na dira maki a zuciya Hajia"