Sashe 28
Azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ajiyar zuciya Hajia ta sauke mai karfi tana kallonsa a sanyaye ta ce" Idan na fashe da kuka zai dawo min ne?, yaya zan yi? Aban Yusuf na rasa uwa, uba, miji, yanzu kuma yau na rasa baban d'a, tabas mutuwa tawa ce ban dandana ba, Allah ya musu rahama ya bamu kyakkyawan karshe"
Yusuf dake kallon mahaifinsa a tausashe ya zuba mata ido yana kallonta
Tabas bata taɓa maganar da ta shiga zuciyarsa irin ta yau ba
Kansa ya dauke yana kallo likitoci suka shigo bisa jagorar A'isha, aka dora mamacin aka fice da shi bangaren da za'a kimtsa shi a cen din ne kuma za'a masa addu'a har garin Allah ya waye
Sai da aka fita da shi Hajia ta riko hannun mahaifin Yusuf tana kallonsa ta ce" BELLO, ka san me yake jiranka, sai da na hanna fitowar YUSUF, ama ya fito, ka ja shi ku koma gidan nan, sai na neme ku"
Wannan karon YUSUF din ne ya dubeta da kula , sannan ba da daga murya ba ya ce" Inaga ya dace ku mayar da maganar buya gefe, dan babu inda zan je ko ya je ga gawa kwonce, duk mai so ya zo ya gwada abinda ya fi iyawa, Allah ne mai komai, idan har Allah ya ƙaddara tare za'a birni gawarwakinmu a gobe buya ba zai hannamu mutuwa ba hajia "
Hajia ta zuba masa ido, zuciyarta na dokawa sosai, tana hangen abinda mijinta ya fada a kan yaron da bai ga girmansa ba bai san waye shi ba, ya Allah, ya Allah
A tausashe ya sake kama mahaifinsa ya mikkar ya rike shi sosai suka fita ya nufi bangarensa da shi, dan yana so ya fara samun nutsuwa kafin ya je a kwana wajen dan uwansa,
Yana fitowa A'isha ta dawo da sauri ta shige ciki wajen Hajia, yaronsa kuwa da sauri ya zo ya talaba masa mahaifinsa suka kama Abu sosai suka fice da shi ba Dar ko tsoron wani ya nufo shi
A'isha na shiga ta karasa wajen mahaifiyarta, a daidai lokacin Hajia ta sada kai ne hawaye sun tarun mata a cikin idannuwa sosai tana ta jan carbi tana godiya ga Allah da jarabawar da ta sameta , ta rasa yaronta Bama zata iya tashi ba bale ta je inda gawarsa take, sai dai dadin musulunci addu'a na tarda bawa a duk inda yake
Da sauri ta dago jin an zauna daf da ita ta zuba idannuwanta cikin na A'isha
A'isha ta dan ja numfashi tana kallonta ta ce" Hajia, waye zai fara shiga kabarin marigayi?"
Da mamaki sosai Hajia ta zuba mata ido, da yannayin muryarta da ta fara raunana saboda kukan dake cin zuciyarta ta ce" Dama akoy wanda zai fara shiga sama da BELLO da YUSUF ne?"
Da sauri da kuma mamaki ta zubawa mahaifiyar Tata ido, muryarta ta kasa boye mamakin ta ta ce" BELLO? Bellon da ya fada cewar baya ra'ayin sarauta Hajia?"
Wannan karon hawayen dake cikin idannuwan Hajia sun samu zubowa, ta saka bayan hannunta ta share tana kallonta ta ce" Fadarsa ce, ra'ayi ne na jin dadin harshe ya fada, kuma koda baya nan inace kin san ya haihu, domin ja gabar garina kin san ko wanene ko?"
A'isha ta kasa daidaita tsuguninta saboda kaffafuwanta da suke son neman fitinarta sakamakon tashin hankalin dake son damunta na amsar da ta san me ake nufi da ita wace da wahala idan har ba zata iya yin fito na fito da dangi a kan wannan ba, sai dai da kula sosai ta ce da mahaifiyar ta " dama akoy wanda ya cencata bayan RISLAN ne?, nagartar yana da ita, makaranci ne, malami ne, mai jin tsoron Allah ne, ba'a taba kama shi da wani laifi ba, kuma daidai gwargwado yana da kudi, me ake so a daurawa talakawa? Kar dai ace mashayi mazina................."
Harshenta ya datse saboda zazafan marin da Hajia ta sauke mata a saman kuncinta, rai bace sosai ta ce"
Asalamu alaikum, alhamdulilah mun tsaya bakin nan a free page, zamu nausa cikin labarin, domin AZAL din na gaba, rikicin na gaba, zazafar soyaya mai rikita zukata na gaba, darasi na gaba, kai ba zaka gane ba sai ka shigo mun tafi tare in sha Allah
Azal 16
A sanyaye sosai Hajia ta ce" Nana, dukda sarauta ce, hakane, a lokacin da aka ɗauki kukan rasa wani ake naɗa wani, sai na ga kamar kin yi gagawa da saurin neman zurowa cikin abinda yake iya zama shafafe sannan wanda ke wanze da maza a gabanki, Wacece ke? Shin bushewar zuciyarki har ta kai wajen nan ki dubeni ki kirayi YUSUF da sunnayen nan?, kar ki saka na zama yarinya kuma wace bata tsoron a je a dawo ya zamto na zauna nima ina tada maki jiya i yau, mai kashi a jikinsa ne zai zagi wani? Ko menene shi an jima da fadin waye shi a doron kasa, tun kafin a san zai girma aka gargadi garajena a kansa, dan shi din shine tsayayen namiji tsakanin maza, ko mahaifiyarsa ba zan iya gani in kyale tana wulakanta shi ba bale ke , ki kula, ki kuma godewa Allah a zaune nake yau, da ace kaffafuwana na iya tashi a daren nan sai an nada wanda ya dace da sarautar nan kafin a yi kowace irin magana, Nana ba zan so ace a rikicin rai da rai harda jinni daya ba, na fi so ace rikicin daga wajen gida yake fitowa, ama ki zage damtse shi din cen da ya tsole maki ido muruci ne, haka kuma Allah shi ke zamani idan har da rabon RILSAN ya hau mulki zai hau a gobe goben nan ama kar ki manta a kasar nan in har d'an mace ya hau mulki sai abin ya zamo babu mazan ko daya, ki sanyayawa ranki kar ki bari a gane abinda ke zuciyarki wanda nima nake daf da ganewa a yanzu!"
Gaba daya ƙafafuwan Nana nauyi suka yi mata, ta gaza motsawa daga inda take har na tsayin mintuna, sai da ta ga dare na karra yi ta mike ta fice ba tare da ta sake saka idannuwanta a cikin na mahaifiyarta ba ta nufi wajen da ta tabata RISLAN na nan ta saka aka yi mata kiransa
Tunda ya karaso ya ga yannayinta hankalinsa ya fara tashi, a tausashe bayan ya bi bayanta sun karra yin nesa kadan ya budi baki ya ce" Ki yi hakuri mama, Allah ya jikan aba sarki Allah ya sa ya huta, dama mu dukkanmu lokaci muke jira, Allah ya sa bakin wahalarsa kennan, ama a gaskiya iyalinsa basu kyautawa kansu ba,mama dama yana cikin wannan halin ama suka boye?"
"RISLAN, ba wannan ya kawo Ni ba, dangane da kujerar nan nake tsaye, domin kai nake so ka hau mulkin nan!" Nana ta fada kai tsaye tana katse maganar da yake yi a wani tausashe da wani karya harshe kamar mace, shi ba zai yi abu kaza kaza ba irin na maza sai da wani laluma da sanyaya magana
A dan tsorace ya kalleta ya ce" Mene? Mulki? Ni kuma?"
Zata bashi amsa ta yi dif sakamakon nufo hanyar da YUSUF ya yi hannunsa daya a wajen kunnansa ya aika kira , dayan hannun kuwa a dan jimke da alamu jira yake yi kawai a amsa masa kiran da ya aika
Da hannunsa ya dan dagawa RISLAN wanda ya nufo shi da sauri , hakan ya sa ya dan dakata yana jira ya gama wayar
Daga dayan bangaren RAUDA dake zaune idannuwa sun yi mata fulu fulu ɗan tashin hankali da tunani, ga wata bakuwar rayuwa, ko tace sabon tashin hankali na nufin nufota a tsiyace, dan Mah dake kwonce cikin wani irin yannayin da ya sakata shiga halin tsoro har ta dago kanta ta ɗora saman cinyarta a hankali tana mata karatu tana jin zafin jikin matar ya yi yawa hakan ya sa du take neman fita a hayacinta dan bata san yaya zata yi ba kuma, abin nema yake ya yiwa zuciyarta da tunanin ta yawa, sai take neman ta idasa fashewa da wani kukan da ya gama rike mata kirji da bakinta gaba daya, a irin lokacin ne wayar Mah ke ruri cikin kira'a tatausa tana neman agajin a daga
Kiran farko kasa dagawa ta yi, dukda ta ga sunnan mai mahimmanci ne a jiki, sai a kira na biyu ne ta daga muryarta a cen kurya ta furta" Asalamu alaikum"
Shiru ya yi da farko, a hankali ya kai dubansa fuskar RISLAN shi dinma muryarsa a tausashe sosai ya ce" Ina take?"
RAUDA ta dan hadiyi abinda ke mata kai kawo a wuya, ta dubi Mah da idannuwanta ke lumshe a hankali ta ce" Gatanan"
Duk irin yadda yake cikin zakuwa da son ta ba Mah wayar bai nuna a muryarsa ba, dan yanzunma Muryar wata iri da take bugun kanta ya furta" Please bani ita,"
A sanyaye ta cire wayar daga kunnenta ta dan dago hannun Mah da yake da dumi shima sosai ta dan matsa kasa kasa sosai ta ce" Hajia, waya ce, wannan da ya kawo mu ne, na saka maku a kunne?"
Mah ta lumshe mata ido, dan kanta sarawa yake yi sosai , sannan ta dan jimke mata hannu, hakan ya tabatar mata tana nufin eh ne
A nutse ta kara mata wayar tana kallon yadda Mah ke bude idannuwanta a hankali muryarta cen ciki sosai ta ce" Baka kyauta min ba"
Bata san me yace ba, ta dai ga ta gyada kai, sai kuma a raunane ta furta" Allah ya jikansa, ka zo gida YUSUF"
Magana ya yi mai dan tsayi, tana gyada kai kamar wani yaya da kanwarsa har dai ta saka hannunta ta dago wayar da hannun RAUDA ta kai wajen kunnen RAUDA sannan ta sauke kanta daga saman cinyar RAUDA din ta kwonta a nan dan gaba daya jikinta ya yi kamar ba nata ba ta lumshe idannuwanta tana ta addu'a a ranta
Rauda dake rike da waya tana jin saukar numfashin mutun, ama gannin ba'a yi magana ba itama sai ta ki yi ta ringa sauke numfashinta a hankali
Yusuf dake kallon mahaifinsa a tausashe ya zuba mata ido yana kallonta
Tabas bata taɓa maganar da ta shiga zuciyarsa irin ta yau ba
Kansa ya dauke yana kallo likitoci suka shigo bisa jagorar A'isha, aka dora mamacin aka fice da shi bangaren da za'a kimtsa shi a cen din ne kuma za'a masa addu'a har garin Allah ya waye
Sai da aka fita da shi Hajia ta riko hannun mahaifin Yusuf tana kallonsa ta ce" BELLO, ka san me yake jiranka, sai da na hanna fitowar YUSUF, ama ya fito, ka ja shi ku koma gidan nan, sai na neme ku"
Wannan karon YUSUF din ne ya dubeta da kula , sannan ba da daga murya ba ya ce" Inaga ya dace ku mayar da maganar buya gefe, dan babu inda zan je ko ya je ga gawa kwonce, duk mai so ya zo ya gwada abinda ya fi iyawa, Allah ne mai komai, idan har Allah ya ƙaddara tare za'a birni gawarwakinmu a gobe buya ba zai hannamu mutuwa ba hajia "
Hajia ta zuba masa ido, zuciyarta na dokawa sosai, tana hangen abinda mijinta ya fada a kan yaron da bai ga girmansa ba bai san waye shi ba, ya Allah, ya Allah
A tausashe ya sake kama mahaifinsa ya mikkar ya rike shi sosai suka fita ya nufi bangarensa da shi, dan yana so ya fara samun nutsuwa kafin ya je a kwana wajen dan uwansa,
Yana fitowa A'isha ta dawo da sauri ta shige ciki wajen Hajia, yaronsa kuwa da sauri ya zo ya talaba masa mahaifinsa suka kama Abu sosai suka fice da shi ba Dar ko tsoron wani ya nufo shi
A'isha na shiga ta karasa wajen mahaifiyarta, a daidai lokacin Hajia ta sada kai ne hawaye sun tarun mata a cikin idannuwa sosai tana ta jan carbi tana godiya ga Allah da jarabawar da ta sameta , ta rasa yaronta Bama zata iya tashi ba bale ta je inda gawarsa take, sai dai dadin musulunci addu'a na tarda bawa a duk inda yake
Da sauri ta dago jin an zauna daf da ita ta zuba idannuwanta cikin na A'isha
A'isha ta dan ja numfashi tana kallonta ta ce" Hajia, waye zai fara shiga kabarin marigayi?"
Da mamaki sosai Hajia ta zuba mata ido, da yannayin muryarta da ta fara raunana saboda kukan dake cin zuciyarta ta ce" Dama akoy wanda zai fara shiga sama da BELLO da YUSUF ne?"
Da sauri da kuma mamaki ta zubawa mahaifiyar Tata ido, muryarta ta kasa boye mamakin ta ta ce" BELLO? Bellon da ya fada cewar baya ra'ayin sarauta Hajia?"
Wannan karon hawayen dake cikin idannuwan Hajia sun samu zubowa, ta saka bayan hannunta ta share tana kallonta ta ce" Fadarsa ce, ra'ayi ne na jin dadin harshe ya fada, kuma koda baya nan inace kin san ya haihu, domin ja gabar garina kin san ko wanene ko?"
A'isha ta kasa daidaita tsuguninta saboda kaffafuwanta da suke son neman fitinarta sakamakon tashin hankalin dake son damunta na amsar da ta san me ake nufi da ita wace da wahala idan har ba zata iya yin fito na fito da dangi a kan wannan ba, sai dai da kula sosai ta ce da mahaifiyar ta " dama akoy wanda ya cencata bayan RISLAN ne?, nagartar yana da ita, makaranci ne, malami ne, mai jin tsoron Allah ne, ba'a taba kama shi da wani laifi ba, kuma daidai gwargwado yana da kudi, me ake so a daurawa talakawa? Kar dai ace mashayi mazina................."
Harshenta ya datse saboda zazafan marin da Hajia ta sauke mata a saman kuncinta, rai bace sosai ta ce"
Asalamu alaikum, alhamdulilah mun tsaya bakin nan a free page, zamu nausa cikin labarin, domin AZAL din na gaba, rikicin na gaba, zazafar soyaya mai rikita zukata na gaba, darasi na gaba, kai ba zaka gane ba sai ka shigo mun tafi tare in sha Allah
Azal 16
A sanyaye sosai Hajia ta ce" Nana, dukda sarauta ce, hakane, a lokacin da aka ɗauki kukan rasa wani ake naɗa wani, sai na ga kamar kin yi gagawa da saurin neman zurowa cikin abinda yake iya zama shafafe sannan wanda ke wanze da maza a gabanki, Wacece ke? Shin bushewar zuciyarki har ta kai wajen nan ki dubeni ki kirayi YUSUF da sunnayen nan?, kar ki saka na zama yarinya kuma wace bata tsoron a je a dawo ya zamto na zauna nima ina tada maki jiya i yau, mai kashi a jikinsa ne zai zagi wani? Ko menene shi an jima da fadin waye shi a doron kasa, tun kafin a san zai girma aka gargadi garajena a kansa, dan shi din shine tsayayen namiji tsakanin maza, ko mahaifiyarsa ba zan iya gani in kyale tana wulakanta shi ba bale ke , ki kula, ki kuma godewa Allah a zaune nake yau, da ace kaffafuwana na iya tashi a daren nan sai an nada wanda ya dace da sarautar nan kafin a yi kowace irin magana, Nana ba zan so ace a rikicin rai da rai harda jinni daya ba, na fi so ace rikicin daga wajen gida yake fitowa, ama ki zage damtse shi din cen da ya tsole maki ido muruci ne, haka kuma Allah shi ke zamani idan har da rabon RILSAN ya hau mulki zai hau a gobe goben nan ama kar ki manta a kasar nan in har d'an mace ya hau mulki sai abin ya zamo babu mazan ko daya, ki sanyayawa ranki kar ki bari a gane abinda ke zuciyarki wanda nima nake daf da ganewa a yanzu!"
Gaba daya ƙafafuwan Nana nauyi suka yi mata, ta gaza motsawa daga inda take har na tsayin mintuna, sai da ta ga dare na karra yi ta mike ta fice ba tare da ta sake saka idannuwanta a cikin na mahaifiyarta ba ta nufi wajen da ta tabata RISLAN na nan ta saka aka yi mata kiransa
Tunda ya karaso ya ga yannayinta hankalinsa ya fara tashi, a tausashe bayan ya bi bayanta sun karra yin nesa kadan ya budi baki ya ce" Ki yi hakuri mama, Allah ya jikan aba sarki Allah ya sa ya huta, dama mu dukkanmu lokaci muke jira, Allah ya sa bakin wahalarsa kennan, ama a gaskiya iyalinsa basu kyautawa kansu ba,mama dama yana cikin wannan halin ama suka boye?"
"RISLAN, ba wannan ya kawo Ni ba, dangane da kujerar nan nake tsaye, domin kai nake so ka hau mulkin nan!" Nana ta fada kai tsaye tana katse maganar da yake yi a wani tausashe da wani karya harshe kamar mace, shi ba zai yi abu kaza kaza ba irin na maza sai da wani laluma da sanyaya magana
A dan tsorace ya kalleta ya ce" Mene? Mulki? Ni kuma?"
Zata bashi amsa ta yi dif sakamakon nufo hanyar da YUSUF ya yi hannunsa daya a wajen kunnansa ya aika kira , dayan hannun kuwa a dan jimke da alamu jira yake yi kawai a amsa masa kiran da ya aika
Da hannunsa ya dan dagawa RISLAN wanda ya nufo shi da sauri , hakan ya sa ya dan dakata yana jira ya gama wayar
Daga dayan bangaren RAUDA dake zaune idannuwa sun yi mata fulu fulu ɗan tashin hankali da tunani, ga wata bakuwar rayuwa, ko tace sabon tashin hankali na nufin nufota a tsiyace, dan Mah dake kwonce cikin wani irin yannayin da ya sakata shiga halin tsoro har ta dago kanta ta ɗora saman cinyarta a hankali tana mata karatu tana jin zafin jikin matar ya yi yawa hakan ya sa du take neman fita a hayacinta dan bata san yaya zata yi ba kuma, abin nema yake ya yiwa zuciyarta da tunanin ta yawa, sai take neman ta idasa fashewa da wani kukan da ya gama rike mata kirji da bakinta gaba daya, a irin lokacin ne wayar Mah ke ruri cikin kira'a tatausa tana neman agajin a daga
Kiran farko kasa dagawa ta yi, dukda ta ga sunnan mai mahimmanci ne a jiki, sai a kira na biyu ne ta daga muryarta a cen kurya ta furta" Asalamu alaikum"
Shiru ya yi da farko, a hankali ya kai dubansa fuskar RISLAN shi dinma muryarsa a tausashe sosai ya ce" Ina take?"
RAUDA ta dan hadiyi abinda ke mata kai kawo a wuya, ta dubi Mah da idannuwanta ke lumshe a hankali ta ce" Gatanan"
Duk irin yadda yake cikin zakuwa da son ta ba Mah wayar bai nuna a muryarsa ba, dan yanzunma Muryar wata iri da take bugun kanta ya furta" Please bani ita,"
A sanyaye ta cire wayar daga kunnenta ta dan dago hannun Mah da yake da dumi shima sosai ta dan matsa kasa kasa sosai ta ce" Hajia, waya ce, wannan da ya kawo mu ne, na saka maku a kunne?"
Mah ta lumshe mata ido, dan kanta sarawa yake yi sosai , sannan ta dan jimke mata hannu, hakan ya tabatar mata tana nufin eh ne
A nutse ta kara mata wayar tana kallon yadda Mah ke bude idannuwanta a hankali muryarta cen ciki sosai ta ce" Baka kyauta min ba"
Bata san me yace ba, ta dai ga ta gyada kai, sai kuma a raunane ta furta" Allah ya jikansa, ka zo gida YUSUF"
Magana ya yi mai dan tsayi, tana gyada kai kamar wani yaya da kanwarsa har dai ta saka hannunta ta dago wayar da hannun RAUDA ta kai wajen kunnen RAUDA sannan ta sauke kanta daga saman cinyar RAUDA din ta kwonta a nan dan gaba daya jikinta ya yi kamar ba nata ba ta lumshe idannuwanta tana ta addu'a a ranta
Rauda dake rike da waya tana jin saukar numfashin mutun, ama gannin ba'a yi magana ba itama sai ta ki yi ta ringa sauke numfashinta a hankali