← Book details Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 92 OF 116

Sashe 92

Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Sai wuraren karfe daya suka isa Gombe, kai tsaye Tudun Wada suka nufa, da yaran gidan ta soma tozali a kofar gidan, da gudu suka shiga ciki domin sanarwa jama'ar gidan, dariya kawai ta yi sannan ta ja jakarta ta hannu ta yi ciki, a zaure suka yi kici6us da Anti Halima wacce ta taho ganin ko dagaske suke, ai kuwa ta rungumeta suna murna gami da lale marhabin da Amarya. Suka karasa ciki, ganin Dada tsaye tana rarraba idanu na son ganin ta inda zata 6ullo yasa ta k'arasawa a guje gami da rungumeta, Dada ta dan tureta cike da farinciki. Kafadarta ta dafa.
"Use Hasiya, kun sha hanya."
Dariya ta yi. Haka suka yi ta nan da nan da ita kamar wannan ne ganinsu na farko da ita. 
   Saida ta gabatar da sallah sannan ta isa dakin Malam, yana kishingide yana gyangyadi saman darduma, sallamarta ce ta sanyashi wartsakewa yana mai amsawa fuska a sake. Bayan sun gaisa ne ya ke tambayar mutan Abuja. Bata jima sosai ba ta koma ciki. Sai yamma iyayensu maza suka dawo daga kasuwa, alokacin har direban da ya kawo Ummi ya juya bayan ya gabatar da sallah ya ci abinci. Malam Balarabe ya yi farinciki da ganin diyartasa. 
Sai bayan Magriba suka samu ke6ewa da Malam Balarabe, anan ta ke jin labarin zuwansa Ringim bayan tafiyarta, inda ya sanya gidansa a kasuwa, ya hada kan kudadensa ya sallami Haruna yaronsa mai tayashi aikin balangu a kasuwa sannan ya taho da zummar idan an siyar Malam Yahuza zai aikomishi da kudaden. Hakan ya yi mata dadi, shikenan sun rabu da Ringim kenan. Ya shiga bata labarin kiran da ya samu ta waya daga Daddy cewar kada ya yi komai na kayan daki shi zai yi don shima diyarsa ce, ya sanarmata koda ya ji hakan, ya ji abin banbarakwai, ya so tambayarta ta waya saidai yasan ba lallai ta samu labarin, koda ya sanarwa yan uwansa, su kansu sunyi mamaki, Malam da kansa ya sanya suka kira Daddy. Bayan an gaisa ya ce. 
   "To kai Alhaji ayi haka? Kwa daukarwa kanku nauyi har haka?"
Dariya Daddy ya yi ya nuna zai iya yiwa Ummin haka koda ace ba dansa za ta aura ba, acewarsa itama diyarsa ce." Jin haka har Malam saida ya yi kukan farinciki, ya yi mishi godiya da binsa da kyawawan addu'o'i, Daddy ya nuna bakomai, tunda har suka bawa dansa aurenta sun mishi komai a rayuwa. 
  Ummi jin dukkan lamarin ta ke yi wani iri, jikinta ya yi sanyi, ko kusa bata da masaniya kan abinda ake ciki a Abuja. 
  "Kada ki bani kunya Hasiya, ki yi kokarin bin mijinki tsakani da Allah, tabbas Umar yaro ne nutsastse, ki godewa Allah don kuwa kin yi babban sa'a, yana sonki kuma iyayensa suma suna sonki, ki zauna da su da zuciya daya, wanda zai yi maka haka a rayuwa lallai bai kamata ka yar da shi ba."
Har da hawayensa alokacin da ya ke fadin haka gareta, ita kanta saida ta share ruwan hawayen, acan kasan ranta kuwa, adduo'i ta ke ta jerowa ga Daddy da iyalinsa. 
    Kwanan Ummi biyu a Gombe, su Hajiya sun wuce Adamawa gaba dayansu har Modibbo. Saidai banda su Ihsan da sauran yaran masu zuwa makaranta da kuma surukansu. 
   Ita kuwa sosai su Abida suka shiga gyarata, duka-duka bikin a wannan lokacin bai fi saura kwanaki goma sha biyar ba, a bakin Dada ta ke jin cewa har mutanen Adamawa suma zasu zo. Dattijuwa Binta, tsohuwa mai ran karfe kenan Yaya ga Dattijo Manu(kakan Ummi) da zuri'arta wadanda rabonsu da Gomben tun rasuwar Inno.
    Gaba daya sai ta k'ara ji ta d'okantu da son ganinsu. 

    Duka-duka su Hajiya kwanansu biyar a Adamawa suka dawo har da wasu cikin yan uwansu wadanda sai bayan biki zasu koma, wasu kuwa sai dab da biki sannan zasu iso. 
  Shirye-shirye sosai akeyi, ba ga nan Abuja da mutan Kano ba, ba kuma ga can Gomben ba. 
    Amarya Ummi ta murzu iya murzuwa, idan ka ganta sai kace bata ta6a shiga rana ba tunda ta zo duniua tsabar kyau da murjewa da fatarta ta yi, ga shi kuma daman lokaci ne na damuna ba ranar ake yi sosai ba. Kayan gyara mace kuwa, har gajiya ta ke yi da sha, don Dada bata barta ba, haka suma surukan Dadan, (Anti Halima da Abida), daga sun ke6e da ita suke duramata. Kusan kullum sai sun kai ukun dare suna waya da ango wanda ya nuna gaba daya kewarta ya isheshi, har rantsuwa ya yi mata akan wani lokacin ji ya ke kamar ya yi tsuntsuwa ya biyota Gombe. Dariya kawai ta ke yi wani lokacin, wani lokacin kuwa tausayi ya ke bata. 
  Amina kuwa, tun kafin tafiyarsu Hajiya Adamawa ta kirata akan ta dawo.  Ana sauran kwana biyar biki da yamma tana zaune ta gama yin sirace na gyaran fata, hannunta rike da kofi wanda aka kad'a madara da wani gumba, su Abida sun sanyata gaba har da wasu yayyunta daga Jar Kwami akan sai ta shanye, kiran Amina ya shigo wayarta, dakyar suka bata wayar don da fari sun k'i wai sai ta shanye, wayar duk ta koma yaluwa, aun gaisa ta ke sanarmata cewar ta iso Gombe tana tasha wai ta yi mata kwatancen unguwarsu, ai Ummi daskarewa ta yi a zaune don mamaki, gani ta ke wasa kawai ta ke yi, saida ta rantse sannan ta saki dariyar murna.
  "Bari na bada a yi miki kwatance."
Ta mikawa Abida wayar, nan ta kwatantawa direban Adaidaitan. 
  Ummi kasa zama ta yi, zata mike suka dakatar da ita, batasan sadda ta kwankwade maganin ba don hankalinta ya tafi ga Antinta. Dariya suke mata saidai bata ko sauraresu ba ta sanya dogon hijabi ta yi sashen Dada cike da mamakin yanda akayi Hajiya Mama ta barta ta zo.
  "Dada! Dada!!"
Suka yi kici6us a kofa.
"Lafiya Boddo?"
  Ta rungumeta.
"Ga Anti Amina nan zuwa, ta Kano wacce na baki labarinta."
Itama Dadan ta hau farinciki.
"Kai Alhamdulillah, shiga ki yi wanka kafin ta karaso, bari na hadamiki ruwan dumin."
Ai da gudu ta shige ciki ta dauki roban sabulunta, sosanta shanye a saman igiya ta ja, Dada da kanta ta hadamata ruwan wanka ta fad'a. 
Tana daga bandaki ta ji muryar Amina na gaggaisawa da mutanen gidan dake mata lale. Ai sauri-sauri ta shiga yi, tana fitowa ta ajiye bokitin sabulun anan kofar dakin Dada, hannunta rike da soson ta fada ciki sai jikin Amina, suka hau dariya. Dada ta kai mata dundu a baya.
"Ke kam Allah Ya sauwaka miki, kai Boddo, a jik'e fa ki ke."
Ummi na dariya ta mike zaune,
"Wallahi murnar ganinta ne, ta yimin bazata." Dada ta kar6i sosannata ta fita tana dariya. 
   Amina wacce ke dubanta fuska a washe ta kamo hannunta ta zauna gefenta.
"Wai kece kodai mafarki nake yi?" Cewar Amina.
"Ai Anti ni zan ce ina mafarki ma wallahi, ban ta6a zaton za ki zo Gombe [truncated by WhatsApp]
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

111

  "Asiri ya tonu, bayan dawowar su Mami daga Adamawa da kwana biyu Abban Adnan cikin dare idanunsa ya gane mishi Hajiya Binta na tone-tone bayan windon dakinsa, bai ma gane kowacece ba, Mami ce a dakinnasa ita dinma idanunta biyu, ganin ya fita da sauri ta mara mishi baya, saida suka zagaya suka isketa tana kokarin binne wasu layu, ke wallahi idan karshen mugunta ya zo babu mai iya tserar da mutum idan ba Allah ba, kuma daman shi Allah ba Ya zalunci, mata ta rude, har kusan sakinta ya yi, itace har da durkusawa neman alfarma wajen Mami akan ta taimaka ta tayata rokar gafararsa. A daren bai sauraresu ba, kiris ya rage a saketa saidai ta ci darajar 'ya'yanta, dakyar da sudin goshi ta samu ya yafemata, saida Mami ta sanya baki sosai. Amma fa nima ina daga kicin ina aiki na ji Mamin suna hira da Hajiya Mama don gida ta zo ta sameta. Tun daga lokacin kuwa jikin Hajiya Bintar ya yi sanyi, har sashen Mami ta je ta fayyacemata mugun kullin da ta yi mata Abba ya juyamata baya da kuma yanda ta so had'e baki da ke amma ba ki bata goyon baya ba, tana kuka ta nemi gafarar Mamin, yanzu ba ki ga idan kin je gidan ki ka shiga sashenta yanda zata kar6eki ba, wallahi sai kinyi mamaki, duk ta yi sanyi har sashen Mami ta biyo Hajiya Mama suka gaisa, Iklima itama yanzu duk ta chanja kodayake ance ita wani saurayi ne ya yaudareta ya kaita gidan masu zaman kansu zai yi mata fyade, kinsan Iklima yar son zuwa party, dakyar Allah Ya kwaceta a hannunsa sakamakon zuwan yan sanda kame, aka hada har ita, saida ta kwana biyu a kaso Abba ya ce babu inda zai taka ya je belinta, sai fa can cikin yan uwan Ummanta ne suka je suka yo, ranar kuwa ta ci duka wajensa don har  makaranta ya hanata zuwa yanzu ya ce aure zaiyi mata."
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
Chapter 92 · 0% Book details