Sashe 70
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Acan kuwa Ummi ta tarar har Baraka ta shirya sun fice daga dakin ita da Intisar, ta goge inda ruwa ya 6ata kafin ta hau shara. Tana cikin yi itama Ikram ta fito, bayan ta kammala ta fito. Anan falon ta iske Hajiya da su Hajja sai kuwa Larai da Hafsatu dake jera kayan karin kumallo.
Ta ajiye ta karasa ta gaishesu kanta a kasa, suka amsa, Hajja ko ciki-ciki ta amsa tana karewa yanda yarinyar ta chanja ta wani murje.
Har Ummi ta bar wajen da kallo ta ke binta. Kafin ta kya6e baki.
"Wannan yarinya nan gaba sai ta ce bata sanmu ba.". Ta yi maganar ne da harshen fillanci ganin su Larai dake wajen ga kuma su Amal dake dudubniyarsu. Hajiya Babba 'yar dariya kawai ta yi na wayancewa don ita har ga Allah tana jin kaunar Ummi a ranta.
Ummi kasa sauka kasan ta yi jin muryoyin yan samarin Hajiyar tare da su Intisar ana hira, jin suna kokarin hayowa ne yasa ta juyawa da sauri har suna karo da Hafsatu. Ta numfasa.
"Don Allah Hafsatu taimaka ki karasamin da wannan."
Ba musu ta kar6a, ita kuwa da sauri ta koma ciki, zata shiga daki ne Hajiya Babba ta dubeta.
"Ummi kirawo yan uwannaki mu karya."
Dole ta nufi dakin su Jidda, ta tarar duk sun shirya, Jidda na sanyawa Ahmad wandon jeans. Ta gaishesu sannan ta isar da sak'on Hajiya Babba.
Wannan karon ma a darare ta ci abincin, idanun Faruk kacokam yana kanta ko kunyar su Hajiya ba ya ji. Yana kammalawa Modibbo ya ba shi maganin mura ya sha.
Karfe takwas saura suka kama haramar tafiya. Modibbo ya yi ta jan Ummi da wasa yana kiranta da amaryarsa. Ita kam kanta na kasa kawai tana dan murmushi har suka gama shiga mota. A mota wannan karon ita da su Amal suka zauna don har rige-rigen zama kusa da ita suke, shi kam Ma'aruf har lokacin bai sake da ita ba ya rike abinda Mominsa ta ce masa akanta.
Itama ta maida hankalinta ga yaran, duk a takure ta ke don duk dagowar da zata yi sukan hada ido da Faruk wanda ya saita madubi yanda zai dunga ganinta har Haidar na mishi dariya.
Ita kuwa damuwa ta yi jin yanda ya ke atishawa, tabbas mura ta kamashi. Garin ya danyi duhu, sunyi nisa aka soma yayyafi kafin kuma a soma ruwan ba mai karfi sosai ba, duk aka daga gilasai, abokan hirar nata duk sunyi bacci, wayarta ta yi karar shigowar sako, ta duba duk a nata zaton kamfani ne saidai Faruk dinne.
"Ko na dawo nan?"
Ta dan dago suka hada ido cikin madubi, ya narkar da ido, da hanzari ta kauda kanta. Shi Faruk bai kunyar ma a dagosu?
Bata kara kallon madubin ba, shi dinma murmushi ya yi kafin ya soma lumshe ido maganin mura na son sakashi bacci, can kuwa ya shimfida hankicif saman fuskarsa bacci ya yi awon gaba da shi. Itama tun tana kalle-kalle har nata baccin ya iso.
Haka dai har suka isa garin Abuja inda suka tarar ana ruwa kamar da bakin kwarya. Koda suka isa gidan Dakta ne ya yi amfani da lemar bayan motar ta kai yaran ciki, su Ikram kuwa iyayen son ruwa haka aka shiga a guje.
Ummi duk hankalinta na ga Faruk wanda ta ga yana shirin shiga ruwan shima, tana son ta haneshi saidai da kunya ainun, to ta ce masa me? Wata lemar Ikram ta daukomusu a ciki Binta na bin bayanta da guda uku, Hajiya ta shige tare da su Jidda, itama Binta ta mikamata tana dariyar murnar ganinta.
Ta kar6a gami da fitowa.
"Ni fa?"
Ya fada yana dubanta da dan daga murya don karar ruwa.
Binta ta dubeshi, Haidar ne kadai ke wajen yana bada umarni ga maaikatan masu shirin kwasar kaya cewa abar kayan har ruwa ya tsagaita. Sai kawai ta mikawa Binta lemar da sauri gudu-gudu ta yi ciki rike da takalman su Amal wanda suka cire a mota.
Faruk ya na murmushi ya kar6i lemar daga hannun Binta, itama ciki ta yi cike da shaawar yanda suke tafiyar da soyayyarsu.
Kai tsaye itama falon ta shiga.
"Aa, garin yaya kika shige? Kema biyewa Ikram ki ka yi kenan, maza tafi ki chanja kayannan."
Fadin Hajiya Babba kenan, ta ajiye takalman kafin ta nufi sama.
Babu k'ura ko kadan a gidan don su Binta sun gyara tsaf, Binta ce ta gyara kuryar Hajiya. Ita dai ta yi mamakin ganin dakinta tas, ta jinjina kai, tasan aikin su Binta ne, wai kenan har ita keda wannan matsayin.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
87
"Allah Mai Iko, abu ya yi kyau." Cewar Modibbo a sanyaye yana dan murmushi, tabbas yaso kwarai Faruk da Ihsan su yi aure, saidai kuma ba yanda zaiyi tunda Muhammad Modibbo ya daureshi da jijiyon jikinsa, ba zai kira Alhaji Kabir da bare ba don kuwa zumunta mai karfi ta auratayya ta shiga tsakani. (Za ku ji idan an shiga tuna baya)
Saidai a ganinsa wata kusan ai tafi wata, haka dai ya sanya alheri a lamarin. Alhaji Kabir ya dubi matasan yaran Hajiya Babba yana mai fad'ad'a fara'arsa.
"Yanzu Hajiya Fatima wadannan duk iyalinki ne? Masha Allah duk sun girma."
Hajiya Babba ta yi murmushi, zai iya mantasu kuwa a fuska don rabonta da shi tun tana goyon Faruk da ta je Adamawa, ko su Ikram bai sani ba. Hajiya Mama ce ta soma nunamishi yarannata.
"Wannan shi ne Usman, ga Ridwan nan babban likita, sai Haidar da karaminsu a maza Faruk."
Yana mamaki yana binsu da kallo da murmushi, idan kaga Alhaji Kabir ba za ka ce shi ya haifo Abubakar ba don kuwa shi farin bafulatani ne tas, dogo ne kuma siriri.
"Ai na dan gane Usman da Ridwan tun shigowata, wadannan ne dai bansani ba."
Ya nuna Haidar da Faruk. Akayi dariya, gaba dayansu yaran saida Modibbo ya yi mishi bayani akansu.
"Kenan dai Faruk kai ba ka yi aure ba? Me ka ke jira?"
"Ai shima yana niyyar yin, akwai wacce zai aura. Ina ta ke ne ma?"
Cewar Modibbo yana waige-waige. Ihsan ta ja tsaki a ranta. Haka kawai za'a dunga tsoma wata can cikin abin zuri'arsu, daidai da Faruk din haushinsa ta ke ji yanda duk ya gama lalacewa akan wacce bata ketare ta a komai ba.
Wata hirar da aka sanyo ce yasa Ikram wacce aka tura kiran Ummi ta yi mursusi ta gyara zama bata tafi ba, anan kuma Modibbo ya sanarmusu da batun zuwa Adamawa, aka bari sai idan anyi hutun makaranta.
Daga nan aka yi zaman cin abinci, Abubakar hankalinsa ya kasu biyu, ga tunanin yarinyar da ya gani mai kama da Inno, sannan ga kallon Ihsan wacce ya ke jin kamar ya sanyata a aljihu ya fice da ita ko babu komai irin kalarsa ce.
Mami na tare da yan uwanta wadanda Modibbo ya hadasu ya musu nasiha sosai, duk da har lokacin takan ji zafinsu saidai ganin irin mijin da diyarta ta samu na nunawa duniya kadai yasa ta sassauto aganinta ko babu komai ta burge. Wayarta ce ta yi kara wanda ya yi sanadin katsewar lomar da ta ke shirin kaiwa bakinta. Ta duba ta ga Yaha ce, ta dauka, bayan sun gaisa ne Yaha ke sanarmata cewar ta iso gidanta bata sameta ba. Mami ta yi murmushi.
"Kinsan gidanmu na Sharada ko?"
"Kayya Hajiya, na kwan biyu banje ba koda na shiga layin ba lallai na gane gidan ba."
"Karki damu ki taho sai ki kirani idan kin shigo."
Daga haka ta ajiye wayar, Hajiya Babba wacce sam bata da fushi sosai ta dubeta fuska a sake.
"Wacece zata zo?"
Mami ta amsa.
"Yaha ce wacce ta kawo Ummi, ta bukaci ganinta ne da kar6ar kudin wata na sanarmata bata wajena yanzu."
"Don bata wajenki idan kin fidda kudinki kin bayar sai cibi ya zama k'ari?"
Cewar Hajiya Mama a kufule don daman har lokacin bata gama hucewa ba. Mami ko kallonta bata yi ba, Hajiya Babba ce ta danyi dariya.
"Ke kuma menene abin daukar zafi to? Kefa haka ki ke ba dai zuciya ba Sadiya."
Ta maida abin wasa hakan yasa Hajiya Mama ta dan sake itama.
"Ai Madinar ce sai a hankali."
Mami itama dan murmushin ta yi kada ta bada su agaban surukai (Jidda da Fadila).
Ummi tana tare da Amina suna hira anan kicin tare da su Larai har sadda Larai suka tafi kai abinci. Alokacin Amina ta dubeta.
"Wallahi kar ki so kiga yanda fatarki ta kara kyau saidai kin rame don har gwara kafin zuwanki Abuja."
Ummi ta ta6a wuyanta tana murmushi.
"To Anti ba dole ba, nifa koyaushe cikin tunani na ke na wannan abu wallahi."
"Ya za ki yi to?"
Alokacin da Larai suka dawo ne ta dubesu.
"Wai kuwa kunsan cewa wannan saurayin da ya zo shi zai auri Ihsan?"
Amina da Ummi suka dubi juna ido waje kafin su dubeta.
"Anya kuwa?" Cewar Amina.
Ta ajiye ta karasa ta gaishesu kanta a kasa, suka amsa, Hajja ko ciki-ciki ta amsa tana karewa yanda yarinyar ta chanja ta wani murje.
Har Ummi ta bar wajen da kallo ta ke binta. Kafin ta kya6e baki.
"Wannan yarinya nan gaba sai ta ce bata sanmu ba.". Ta yi maganar ne da harshen fillanci ganin su Larai dake wajen ga kuma su Amal dake dudubniyarsu. Hajiya Babba 'yar dariya kawai ta yi na wayancewa don ita har ga Allah tana jin kaunar Ummi a ranta.
Ummi kasa sauka kasan ta yi jin muryoyin yan samarin Hajiyar tare da su Intisar ana hira, jin suna kokarin hayowa ne yasa ta juyawa da sauri har suna karo da Hafsatu. Ta numfasa.
"Don Allah Hafsatu taimaka ki karasamin da wannan."
Ba musu ta kar6a, ita kuwa da sauri ta koma ciki, zata shiga daki ne Hajiya Babba ta dubeta.
"Ummi kirawo yan uwannaki mu karya."
Dole ta nufi dakin su Jidda, ta tarar duk sun shirya, Jidda na sanyawa Ahmad wandon jeans. Ta gaishesu sannan ta isar da sak'on Hajiya Babba.
Wannan karon ma a darare ta ci abincin, idanun Faruk kacokam yana kanta ko kunyar su Hajiya ba ya ji. Yana kammalawa Modibbo ya ba shi maganin mura ya sha.
Karfe takwas saura suka kama haramar tafiya. Modibbo ya yi ta jan Ummi da wasa yana kiranta da amaryarsa. Ita kam kanta na kasa kawai tana dan murmushi har suka gama shiga mota. A mota wannan karon ita da su Amal suka zauna don har rige-rigen zama kusa da ita suke, shi kam Ma'aruf har lokacin bai sake da ita ba ya rike abinda Mominsa ta ce masa akanta.
Itama ta maida hankalinta ga yaran, duk a takure ta ke don duk dagowar da zata yi sukan hada ido da Faruk wanda ya saita madubi yanda zai dunga ganinta har Haidar na mishi dariya.
Ita kuwa damuwa ta yi jin yanda ya ke atishawa, tabbas mura ta kamashi. Garin ya danyi duhu, sunyi nisa aka soma yayyafi kafin kuma a soma ruwan ba mai karfi sosai ba, duk aka daga gilasai, abokan hirar nata duk sunyi bacci, wayarta ta yi karar shigowar sako, ta duba duk a nata zaton kamfani ne saidai Faruk dinne.
"Ko na dawo nan?"
Ta dan dago suka hada ido cikin madubi, ya narkar da ido, da hanzari ta kauda kanta. Shi Faruk bai kunyar ma a dagosu?
Bata kara kallon madubin ba, shi dinma murmushi ya yi kafin ya soma lumshe ido maganin mura na son sakashi bacci, can kuwa ya shimfida hankicif saman fuskarsa bacci ya yi awon gaba da shi. Itama tun tana kalle-kalle har nata baccin ya iso.
Haka dai har suka isa garin Abuja inda suka tarar ana ruwa kamar da bakin kwarya. Koda suka isa gidan Dakta ne ya yi amfani da lemar bayan motar ta kai yaran ciki, su Ikram kuwa iyayen son ruwa haka aka shiga a guje.
Ummi duk hankalinta na ga Faruk wanda ta ga yana shirin shiga ruwan shima, tana son ta haneshi saidai da kunya ainun, to ta ce masa me? Wata lemar Ikram ta daukomusu a ciki Binta na bin bayanta da guda uku, Hajiya ta shige tare da su Jidda, itama Binta ta mikamata tana dariyar murnar ganinta.
Ta kar6a gami da fitowa.
"Ni fa?"
Ya fada yana dubanta da dan daga murya don karar ruwa.
Binta ta dubeshi, Haidar ne kadai ke wajen yana bada umarni ga maaikatan masu shirin kwasar kaya cewa abar kayan har ruwa ya tsagaita. Sai kawai ta mikawa Binta lemar da sauri gudu-gudu ta yi ciki rike da takalman su Amal wanda suka cire a mota.
Faruk ya na murmushi ya kar6i lemar daga hannun Binta, itama ciki ta yi cike da shaawar yanda suke tafiyar da soyayyarsu.
Kai tsaye itama falon ta shiga.
"Aa, garin yaya kika shige? Kema biyewa Ikram ki ka yi kenan, maza tafi ki chanja kayannan."
Fadin Hajiya Babba kenan, ta ajiye takalman kafin ta nufi sama.
Babu k'ura ko kadan a gidan don su Binta sun gyara tsaf, Binta ce ta gyara kuryar Hajiya. Ita dai ta yi mamakin ganin dakinta tas, ta jinjina kai, tasan aikin su Binta ne, wai kenan har ita keda wannan matsayin.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
87
"Allah Mai Iko, abu ya yi kyau." Cewar Modibbo a sanyaye yana dan murmushi, tabbas yaso kwarai Faruk da Ihsan su yi aure, saidai kuma ba yanda zaiyi tunda Muhammad Modibbo ya daureshi da jijiyon jikinsa, ba zai kira Alhaji Kabir da bare ba don kuwa zumunta mai karfi ta auratayya ta shiga tsakani. (Za ku ji idan an shiga tuna baya)
Saidai a ganinsa wata kusan ai tafi wata, haka dai ya sanya alheri a lamarin. Alhaji Kabir ya dubi matasan yaran Hajiya Babba yana mai fad'ad'a fara'arsa.
"Yanzu Hajiya Fatima wadannan duk iyalinki ne? Masha Allah duk sun girma."
Hajiya Babba ta yi murmushi, zai iya mantasu kuwa a fuska don rabonta da shi tun tana goyon Faruk da ta je Adamawa, ko su Ikram bai sani ba. Hajiya Mama ce ta soma nunamishi yarannata.
"Wannan shi ne Usman, ga Ridwan nan babban likita, sai Haidar da karaminsu a maza Faruk."
Yana mamaki yana binsu da kallo da murmushi, idan kaga Alhaji Kabir ba za ka ce shi ya haifo Abubakar ba don kuwa shi farin bafulatani ne tas, dogo ne kuma siriri.
"Ai na dan gane Usman da Ridwan tun shigowata, wadannan ne dai bansani ba."
Ya nuna Haidar da Faruk. Akayi dariya, gaba dayansu yaran saida Modibbo ya yi mishi bayani akansu.
"Kenan dai Faruk kai ba ka yi aure ba? Me ka ke jira?"
"Ai shima yana niyyar yin, akwai wacce zai aura. Ina ta ke ne ma?"
Cewar Modibbo yana waige-waige. Ihsan ta ja tsaki a ranta. Haka kawai za'a dunga tsoma wata can cikin abin zuri'arsu, daidai da Faruk din haushinsa ta ke ji yanda duk ya gama lalacewa akan wacce bata ketare ta a komai ba.
Wata hirar da aka sanyo ce yasa Ikram wacce aka tura kiran Ummi ta yi mursusi ta gyara zama bata tafi ba, anan kuma Modibbo ya sanarmusu da batun zuwa Adamawa, aka bari sai idan anyi hutun makaranta.
Daga nan aka yi zaman cin abinci, Abubakar hankalinsa ya kasu biyu, ga tunanin yarinyar da ya gani mai kama da Inno, sannan ga kallon Ihsan wacce ya ke jin kamar ya sanyata a aljihu ya fice da ita ko babu komai irin kalarsa ce.
Mami na tare da yan uwanta wadanda Modibbo ya hadasu ya musu nasiha sosai, duk da har lokacin takan ji zafinsu saidai ganin irin mijin da diyarta ta samu na nunawa duniya kadai yasa ta sassauto aganinta ko babu komai ta burge. Wayarta ce ta yi kara wanda ya yi sanadin katsewar lomar da ta ke shirin kaiwa bakinta. Ta duba ta ga Yaha ce, ta dauka, bayan sun gaisa ne Yaha ke sanarmata cewar ta iso gidanta bata sameta ba. Mami ta yi murmushi.
"Kinsan gidanmu na Sharada ko?"
"Kayya Hajiya, na kwan biyu banje ba koda na shiga layin ba lallai na gane gidan ba."
"Karki damu ki taho sai ki kirani idan kin shigo."
Daga haka ta ajiye wayar, Hajiya Babba wacce sam bata da fushi sosai ta dubeta fuska a sake.
"Wacece zata zo?"
Mami ta amsa.
"Yaha ce wacce ta kawo Ummi, ta bukaci ganinta ne da kar6ar kudin wata na sanarmata bata wajena yanzu."
"Don bata wajenki idan kin fidda kudinki kin bayar sai cibi ya zama k'ari?"
Cewar Hajiya Mama a kufule don daman har lokacin bata gama hucewa ba. Mami ko kallonta bata yi ba, Hajiya Babba ce ta danyi dariya.
"Ke kuma menene abin daukar zafi to? Kefa haka ki ke ba dai zuciya ba Sadiya."
Ta maida abin wasa hakan yasa Hajiya Mama ta dan sake itama.
"Ai Madinar ce sai a hankali."
Mami itama dan murmushin ta yi kada ta bada su agaban surukai (Jidda da Fadila).
Ummi tana tare da Amina suna hira anan kicin tare da su Larai har sadda Larai suka tafi kai abinci. Alokacin Amina ta dubeta.
"Wallahi kar ki so kiga yanda fatarki ta kara kyau saidai kin rame don har gwara kafin zuwanki Abuja."
Ummi ta ta6a wuyanta tana murmushi.
"To Anti ba dole ba, nifa koyaushe cikin tunani na ke na wannan abu wallahi."
"Ya za ki yi to?"
Alokacin da Larai suka dawo ne ta dubesu.
"Wai kuwa kunsan cewa wannan saurayin da ya zo shi zai auri Ihsan?"
Amina da Ummi suka dubi juna ido waje kafin su dubeta.
"Anya kuwa?" Cewar Amina.