Sashe 114
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
129-130
Kowaccensu ta yi shiru tana mamakin wannan kiran, Ummi zata zauna k'asa Mami ta nunamata kujera.
"Zauna nan Ummi kada ki takura."
Ba musu ta zauna kujerar da ke fuskantar Mamin hakanab Ihsan ta zauna gefenta saidai nesa da ita. Tsaf Mami na lura da yanda Ihsan ke faman cin magani, ta numfasa ranta babu dadi kafin ta soma magana.
"Abinda yasa na nemi da na ganku bai wuce fahimtar irin rashin jituwar da ke tsakaninku ba har zuwa wannan lokacin da ya ci ace komai da ku ka sanyawa zuciyoyinku ya kau. Matsalar ba daga Ummu ta ke ba sai daga ke." Ta nuna Ihsan wacce ta kara tamke fuska.
"Na lura kin sanyawa ranki kiyayya, muguwar kiyayya ta Ummi alhalin banga wani mugun abu da ta ta6a yi miki ba har ta cancanci hakan. Ihsan kina wasa da addininki, wannan ba d'abi'ar musulmin kwarai bane, ina mamakinki, ba ki da rik'o akan kowa sai akan Ummi, yarinyar da gatanan zan shaidi cewa takan yi kokari matuk'a wajen kulaki saidai ba za ki amsamata ba, ko sau daya ban ta6a ganin kin bita da kallon arziki ba. Anya kina son gamawa da duniya lafiya?"
A razane Ihsan ta dubi mahaifiyarta har idanunta sun ciko da ruwan hawaye saidai ta kasa cewa uffan. Mami ta jinjina kai cikin tabbatarwa.
"Hakika wannan hali ba inda zai kai ki a rayuwa, ke duk abinda ya faru bai zame miki ishara ba? Ni na haifeki, ni nasan halinki saidai ban ta6a saninki da nunawa mutum kiyayya ba sai akan Ummi."
"Ni Mami me ta yimin da zan k'i ta?" Ta fada cikin rawar murya idanunta cike da ruwan hawaye. A fusace Mami ta ke dubanta, Ummi ta dubi Ihsan kadan saidai ba ta ce uffan ba ta maida kanta k'asa.
"Shi nakeson a yau ki bude zuciyarki ki sanarmin, me Ummi ta yi miki ki ke k'in sakin jiki da ita kamar yanda sauran yan uwanki ke yi? Ko kinsan cewa nasha kamaki kin harararta? Fuskarki na nuni da tsantsar kiyayya gareta koyaushe. Annabinmu s.a.w ya hanemu da zurfafa kiyayya ga dan uwa musulmi.
Abu hurayrah ya ruwaito Annabi SAW ya ce "Na rantse da wanda raina ke hannunsa mutum ba zai shiga aljanna ba har sai ya mika wuya, sannan ba zaka mika wuya ba har sai kunso junanku. Ku yaɗa alkhairi zaku so junanku. Sannan ku guji kiyayya don kaifi gare ta, bance yana aske gashi ba amma yana aske addini."
Wannan kadai bai isheki hujjar da za ki yi watsi da makamanki ki rik'i Ummi yar uwa ba?
Mami ta cigaba da magana, ta inda ta shiga ba tanan ta ke fita ba har yanda ta fusata ya tayarwa Ihsan da Ummi hankali, musamman ma Ihsan wacce ke son mahaifiyarta ta sosai, kokadan batason abinda zai 6ata ranta, kuka sosai ta ke yi, ta mike ta nufi wajenta ta durkusa gami da riko hannunta.
"Ki gafartamin Mami, wallahi na daina, zan riki Ummi duk yanda ki ke so, Ummi don Allah ki yafemin abubuwan da na aikata gareki, bazan k'ara ba in sha Allah."
Ummi ta share hawayenta tana murmushi a hankali ta mike ta tako har wajen da suke, zama ta yi gami da riko hannayen Ihsan.
"Ban ta6a rikeki a raina ba daidai da rana daya, na yafemiki tun kafin ki rok'a, karki damu, nima ki gafartamin idan akwai abinda na yi miki da bansani ba."
Kunya ta rufe Ihsan, ta sauke kanta jiki a sanyaye.
"Ba abinda kikamin, idan ma kin yi to na yafemiki duniya da lahira."
Mami murmushi kawai ta ke yi, ko babu komai tana alfahari da Ihsan a fagen jin maganarta, da wuya ta sa6a umarninta.
Ta riko hannuwansu ta sanya cikin na juna.
"Allah Ya muku albarka, Ya kara hada kanku."
Ummi da Ihsan suka dubi juna suka yi murmushi alokacin da suka amsa da amin.
Tun daga wannan lokacin, suka dinke, idan ana zaune ana hira, Ihsan ta daina barin wajen idan ta ga Ummi, har takan tsokani Ummi cewa ita fa yayarta ce yanzu. Ummi dariya ta yi saboda rashin sabo da hakan daga gareta.
Su Intisar gaba daya sunyi mamaki.
"Ko kefa." Cewar Aisha yayar Ihsan a saitin kunnenta, ta dubeta kawai suka yi murmushi. Hatta Amina, saida Ummi ta kira a wayar ta sanarmata batun shirinsu don ranar yini kawai ta zo wanda shima Bellon dakyar ya amince don acewarsa bai isa ace ta soma fita ba.
Babu wanda bai yi murna da shirin Ihsan da Ummi ba.
"Wallahi kinsan me Ikram? Yanzu jin zuciyata nake wasai babu ko digon damuwa, ashe kiyayya babu dadi? Ni sai yanzu ma na ke kara fahimtar Ummi mutum ce, halayenta abin so da sha'awa." Abinda Ihsan ta fadawa Ikram kenan sadda suka shigo falon Mami bayan ta raka Ihsan din wajen mijinta da ya bukaci ganinta. Ikram murmushi ta yi.
"Kwata-kwata gaba bata yi ba ai, Allah Ya k'ara nisantamu daga shaidan."
"Amin."
Washegari aka yi shirin tafiya Adamawa tun karfe takwas na safiya, Ihsan nan ta shiga kuka sosai dakyar aka 6an6areta daga jikin Maminta, nan kuma ta kama hannun Fahad gam ta rike, shi kansa kuka ya ke kasancewar sun shaku da ita.
"Ya kamata ki samarwa Fahad k'ani."
Mami ta tuno furucin Mijinta a daren jiya, kwarai da zata kara haihuwa tasan ba karamin dadi zaiji ba, saidai kuma likita ya tabbatar mata cewa tsarin iyali na shan magunguna da ta yi ya janyomata matsala a mahaifa, abu ne mai wuya ta kara haihuwa sai ikon Allah, ya yi mata wannan bayanin ne sadda ta ga 6atan watanta kwanakin baya da har Hajiya Mama ta shawarceta da zuwa ganin likita ko ciki ne da ita.
Kwarai ta yi da na sanin yin tsarin iyali musamman ma da ya kasance ba da iznin mijinta ba.
Haka kukanta ya kasance biyu, da jimamin rabuwa da diyarta wacce kusan tafi kaunarta duk a yarannata idan an cire Adnan wanda Abban ke so sosai, sun shaku da ita yau ga aure ya raba.
Aka wuce gaba daya har su Hajiya Babba, Ummi kuwa a ranar suka wuce da su Jidda zuwa Abuja.
*** *** ***
A farkon zamantakewar Ihsan da Badiyya, sun sami matsala na kishi, saidai da ikon Allah komai ya zo ya wuce suke zamansu lafiya, ga Abubakar ya na takatsantsan sosai don ya rage kula yanmata musamman da ya ke 6arje Angoncinsa, hakanan ya rage hira a waya a gaban matansa gudun 6atawa wata cikinsu, yanmatan ma duk sai ya ke ji suna ba shi haushi, watan Ihsan biyu a gidan, ta samu ciki, murna wajen iyayen Abubakar ba a magana, shi kansa har kuka ya yi don tsananin farinciki. Ya zamana hankalinsa kacokam ya koma ga kula da Ihsan, Badiyya ta shiga tashin hankali matuka saidai ta yi jarumtar 6oyewa bata nuna ba. Da ita aka hadu aka yi ta kula da Ihsan.
Ummi cikinta ya shiga tara cif, a wannan lokacin sosai an soma shirye-shiryen bikin Ikram da Gidado, bata fita ko'ina banda asibiti, wataran kuwa ya kwasheta ya kaita gidan Hajiya ta wuni, komai ba bukatar mace da danta na haihuwa Faruk ya siya ya ajiye, haka itama kamar yanda aka Jidda ta yi mata bayani, ta sanya dukkan abin bukata na ranar farko ga macen da ta haihu cikin karamin akwati. Bata da aiki sai adduoi, da kallon kayan bebi, yau ma tana zaune saman gado ta bararraje tana kallon kayan jariran da Faruk ya siyo duk kuwa da cewar dauriya ce ta ke yi sakamakon mararta dake dan murdawa, Batula na aikin jera wasu cikin 'yar kwaba na saka kayan yara da Faruk ya siyo. Ta juyo gami da sakin murmushi
"Kai Anti, kullum idan Yaya ya siyo kaya sai kinyi zaman kallonsu."
Ummi ta numfasa tana dariya.
"Bari kawai Batula, wallahi idan ina kallon kayan sai na ji son bebi na k'ara shiga raina ne, yanzun ma ba ki ji yanda na ke ji ba, Allah dai Ya rabamu lafiya."
"Amin Anti." Fadin Batula cikin dariya.
Suka kammala hada komai suka maida duk Batula ce karfin aikin, ta mike saman gadon.
"Bari na kwanta ko ciwon marar nan zai yi sauki, inajinsa kadan-kadan."
Kowaccensu ta yi shiru tana mamakin wannan kiran, Ummi zata zauna k'asa Mami ta nunamata kujera.
"Zauna nan Ummi kada ki takura."
Ba musu ta zauna kujerar da ke fuskantar Mamin hakanab Ihsan ta zauna gefenta saidai nesa da ita. Tsaf Mami na lura da yanda Ihsan ke faman cin magani, ta numfasa ranta babu dadi kafin ta soma magana.
"Abinda yasa na nemi da na ganku bai wuce fahimtar irin rashin jituwar da ke tsakaninku ba har zuwa wannan lokacin da ya ci ace komai da ku ka sanyawa zuciyoyinku ya kau. Matsalar ba daga Ummu ta ke ba sai daga ke." Ta nuna Ihsan wacce ta kara tamke fuska.
"Na lura kin sanyawa ranki kiyayya, muguwar kiyayya ta Ummi alhalin banga wani mugun abu da ta ta6a yi miki ba har ta cancanci hakan. Ihsan kina wasa da addininki, wannan ba d'abi'ar musulmin kwarai bane, ina mamakinki, ba ki da rik'o akan kowa sai akan Ummi, yarinyar da gatanan zan shaidi cewa takan yi kokari matuk'a wajen kulaki saidai ba za ki amsamata ba, ko sau daya ban ta6a ganin kin bita da kallon arziki ba. Anya kina son gamawa da duniya lafiya?"
A razane Ihsan ta dubi mahaifiyarta har idanunta sun ciko da ruwan hawaye saidai ta kasa cewa uffan. Mami ta jinjina kai cikin tabbatarwa.
"Hakika wannan hali ba inda zai kai ki a rayuwa, ke duk abinda ya faru bai zame miki ishara ba? Ni na haifeki, ni nasan halinki saidai ban ta6a saninki da nunawa mutum kiyayya ba sai akan Ummi."
"Ni Mami me ta yimin da zan k'i ta?" Ta fada cikin rawar murya idanunta cike da ruwan hawaye. A fusace Mami ta ke dubanta, Ummi ta dubi Ihsan kadan saidai ba ta ce uffan ba ta maida kanta k'asa.
"Shi nakeson a yau ki bude zuciyarki ki sanarmin, me Ummi ta yi miki ki ke k'in sakin jiki da ita kamar yanda sauran yan uwanki ke yi? Ko kinsan cewa nasha kamaki kin harararta? Fuskarki na nuni da tsantsar kiyayya gareta koyaushe. Annabinmu s.a.w ya hanemu da zurfafa kiyayya ga dan uwa musulmi.
Abu hurayrah ya ruwaito Annabi SAW ya ce "Na rantse da wanda raina ke hannunsa mutum ba zai shiga aljanna ba har sai ya mika wuya, sannan ba zaka mika wuya ba har sai kunso junanku. Ku yaɗa alkhairi zaku so junanku. Sannan ku guji kiyayya don kaifi gare ta, bance yana aske gashi ba amma yana aske addini."
Wannan kadai bai isheki hujjar da za ki yi watsi da makamanki ki rik'i Ummi yar uwa ba?
Mami ta cigaba da magana, ta inda ta shiga ba tanan ta ke fita ba har yanda ta fusata ya tayarwa Ihsan da Ummi hankali, musamman ma Ihsan wacce ke son mahaifiyarta ta sosai, kokadan batason abinda zai 6ata ranta, kuka sosai ta ke yi, ta mike ta nufi wajenta ta durkusa gami da riko hannunta.
"Ki gafartamin Mami, wallahi na daina, zan riki Ummi duk yanda ki ke so, Ummi don Allah ki yafemin abubuwan da na aikata gareki, bazan k'ara ba in sha Allah."
Ummi ta share hawayenta tana murmushi a hankali ta mike ta tako har wajen da suke, zama ta yi gami da riko hannayen Ihsan.
"Ban ta6a rikeki a raina ba daidai da rana daya, na yafemiki tun kafin ki rok'a, karki damu, nima ki gafartamin idan akwai abinda na yi miki da bansani ba."
Kunya ta rufe Ihsan, ta sauke kanta jiki a sanyaye.
"Ba abinda kikamin, idan ma kin yi to na yafemiki duniya da lahira."
Mami murmushi kawai ta ke yi, ko babu komai tana alfahari da Ihsan a fagen jin maganarta, da wuya ta sa6a umarninta.
Ta riko hannuwansu ta sanya cikin na juna.
"Allah Ya muku albarka, Ya kara hada kanku."
Ummi da Ihsan suka dubi juna suka yi murmushi alokacin da suka amsa da amin.
Tun daga wannan lokacin, suka dinke, idan ana zaune ana hira, Ihsan ta daina barin wajen idan ta ga Ummi, har takan tsokani Ummi cewa ita fa yayarta ce yanzu. Ummi dariya ta yi saboda rashin sabo da hakan daga gareta.
Su Intisar gaba daya sunyi mamaki.
"Ko kefa." Cewar Aisha yayar Ihsan a saitin kunnenta, ta dubeta kawai suka yi murmushi. Hatta Amina, saida Ummi ta kira a wayar ta sanarmata batun shirinsu don ranar yini kawai ta zo wanda shima Bellon dakyar ya amince don acewarsa bai isa ace ta soma fita ba.
Babu wanda bai yi murna da shirin Ihsan da Ummi ba.
"Wallahi kinsan me Ikram? Yanzu jin zuciyata nake wasai babu ko digon damuwa, ashe kiyayya babu dadi? Ni sai yanzu ma na ke kara fahimtar Ummi mutum ce, halayenta abin so da sha'awa." Abinda Ihsan ta fadawa Ikram kenan sadda suka shigo falon Mami bayan ta raka Ihsan din wajen mijinta da ya bukaci ganinta. Ikram murmushi ta yi.
"Kwata-kwata gaba bata yi ba ai, Allah Ya k'ara nisantamu daga shaidan."
"Amin."
Washegari aka yi shirin tafiya Adamawa tun karfe takwas na safiya, Ihsan nan ta shiga kuka sosai dakyar aka 6an6areta daga jikin Maminta, nan kuma ta kama hannun Fahad gam ta rike, shi kansa kuka ya ke kasancewar sun shaku da ita.
"Ya kamata ki samarwa Fahad k'ani."
Mami ta tuno furucin Mijinta a daren jiya, kwarai da zata kara haihuwa tasan ba karamin dadi zaiji ba, saidai kuma likita ya tabbatar mata cewa tsarin iyali na shan magunguna da ta yi ya janyomata matsala a mahaifa, abu ne mai wuya ta kara haihuwa sai ikon Allah, ya yi mata wannan bayanin ne sadda ta ga 6atan watanta kwanakin baya da har Hajiya Mama ta shawarceta da zuwa ganin likita ko ciki ne da ita.
Kwarai ta yi da na sanin yin tsarin iyali musamman ma da ya kasance ba da iznin mijinta ba.
Haka kukanta ya kasance biyu, da jimamin rabuwa da diyarta wacce kusan tafi kaunarta duk a yarannata idan an cire Adnan wanda Abban ke so sosai, sun shaku da ita yau ga aure ya raba.
Aka wuce gaba daya har su Hajiya Babba, Ummi kuwa a ranar suka wuce da su Jidda zuwa Abuja.
*** *** ***
A farkon zamantakewar Ihsan da Badiyya, sun sami matsala na kishi, saidai da ikon Allah komai ya zo ya wuce suke zamansu lafiya, ga Abubakar ya na takatsantsan sosai don ya rage kula yanmata musamman da ya ke 6arje Angoncinsa, hakanan ya rage hira a waya a gaban matansa gudun 6atawa wata cikinsu, yanmatan ma duk sai ya ke ji suna ba shi haushi, watan Ihsan biyu a gidan, ta samu ciki, murna wajen iyayen Abubakar ba a magana, shi kansa har kuka ya yi don tsananin farinciki. Ya zamana hankalinsa kacokam ya koma ga kula da Ihsan, Badiyya ta shiga tashin hankali matuka saidai ta yi jarumtar 6oyewa bata nuna ba. Da ita aka hadu aka yi ta kula da Ihsan.
Ummi cikinta ya shiga tara cif, a wannan lokacin sosai an soma shirye-shiryen bikin Ikram da Gidado, bata fita ko'ina banda asibiti, wataran kuwa ya kwasheta ya kaita gidan Hajiya ta wuni, komai ba bukatar mace da danta na haihuwa Faruk ya siya ya ajiye, haka itama kamar yanda aka Jidda ta yi mata bayani, ta sanya dukkan abin bukata na ranar farko ga macen da ta haihu cikin karamin akwati. Bata da aiki sai adduoi, da kallon kayan bebi, yau ma tana zaune saman gado ta bararraje tana kallon kayan jariran da Faruk ya siyo duk kuwa da cewar dauriya ce ta ke yi sakamakon mararta dake dan murdawa, Batula na aikin jera wasu cikin 'yar kwaba na saka kayan yara da Faruk ya siyo. Ta juyo gami da sakin murmushi
"Kai Anti, kullum idan Yaya ya siyo kaya sai kinyi zaman kallonsu."
Ummi ta numfasa tana dariya.
"Bari kawai Batula, wallahi idan ina kallon kayan sai na ji son bebi na k'ara shiga raina ne, yanzun ma ba ki ji yanda na ke ji ba, Allah dai Ya rabamu lafiya."
"Amin Anti." Fadin Batula cikin dariya.
Suka kammala hada komai suka maida duk Batula ce karfin aikin, ta mike saman gadon.
"Bari na kwanta ko ciwon marar nan zai yi sauki, inajinsa kadan-kadan."