Sashe 56
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ko wanka baiyi ba, hankalinsa na ga abar kaunartasa. Zai so jin amsar da zata bawa Binta. Hakan yasa shi yin cak yana mai zubamata ido don sun ba shi baya.
Ummi ta yi murmushi wanda har gefen kumatunta ya lotsa. Batasan sadda ta soma magana ba.
"Ni nasan yanda nake jin Yaya Faruk a raina Binta, akwai da yawa daga abubuwa wanda ba sai ka 6ata lokaci wajen bayyanashi ba, watakil ya nuna kansa wataran. Ina son Yaya Faruk fiye da kaina, zan iya sadaukar da nawa farincikin don kawai ya samu nasa. Binta me zance ga mutumin da ya daraja ni ya nunawa duniya ni din mutum ce mai daraja? Ke kuwa idan ban kaunaceshi ba me zan mishi?"
Binta ta yi dariya.
"Tabbas kinyi gaskiya, kin kuma burgeni matuk'a. Allah Yasa wannan kauna taku ta d'ore har ku haayyafa ku tara zuri'a guda taku."
Kunya ta hanata amsawa face murmushi da tayi.
"Ameen." Jin muryarsa yasa duk suka juyo a razane, ta zaro ido duk ta bi ta diririce, shikenan ya ji abinda ta ce kenan? Ji ta yi kamar ta nutse a k'asa don kunya. Ita kuwa Binta tana yar dariya ta russuna ta gaisheshi, ya amsa fuska a sake yana duban Ummi. Ita dinma gaisheshi ta yi dakyar sakamakon harshenta da ta ji ya yi nauyi duk don tsabar kunya.
Ya amsa yana ji kamar ya nufeta ya rukunkume don dadin da kalamanta sukayi masa.
"Zo nan Ummi."
Ya fad'a gami da juyawa ya fita. Ta bi bayanshi da kallo, daga shi sai dogon wando da singilet bak'a.
Ta dubi Binta wacce ke zungurar kafadarta tana mata nuni da ta je. Ta yi murmushi mai bayyana hak'ora cikin muryar rad'a ta ce.
"Anya bai ji maganarmu ba?"
"Lallai ke dinnan, to meye idan ya ji? Daman kinason fadamishi kin kasa kinga ya hutar da ke."
Ta girgiza kai gami da wanke hannunta da handwash sannan ta mara mishi baya.
A tsaye ta tarar da shi wajen hanyar da zata sada ka da sashensa. Ya kura mata ido kamar ya hadiyeta. Ta kauda fuskarta ta karasa gareshi.
"Meyasa kike barin wayarki a daki sai nayita kira bakya d'agawa?'
Yana maganar cikin muryar shagwa6a kamar wani k'aramin yaro, abin ma sai ya bata dariya, idan yana wannan shagwa6ar wani kyau ya ke yi mata, ita dake mace ma bazata iya yinta ba.
"Ka yi hakuri, aiki ne mukeyi."
"Naji, maimaita abinda kika fad'awa Binta yanzu a kicin."
Ta zaro ido tana kallonsa fuskarta dauke da murmushi, shima murmushin ya yi ya daga mata gira.
"Kinyi zaton ban ji ba ko? Na ji dukkab tattaunawarku, oya idan dagaske ki ke maganarki ki cemin 'Ina sonka Faruk' na ji."
'Innalillahi...' Ta karantota har karshe a ranta, gaba daya ta diririce. Shi kuwa dagaske ya ke, don tsayuwarsa ya gyara yana jiranta.
"Kinyi shiru."
Ta hau wasa da yatsunta, murya a raunane ta ce.
"Ni..ni ban ta6a fad'a ba fa."
"Shiyasa nakeso ki fad'amin, ya zama ni ne farko nine kuma karshen wanda za ki fad'awa hakan ok?"
Ta runtse ido, yau ta shiga uku, ji ta ke yi kalaman sun yi mata nauyi da tsauri, bazata iya fad'a ba. Ya dan saka saman yatsansa manuniya ya zunguri hannunta.
"Kin yi shiru Ummina."
Ta ja baya kadan ta hadiyi miyau.
"Ka yi hakuri don Allah."
Ya lura a tsorace ta ke ma, sai kawai ya yi murmushi.
"Ki ka ce ba ki da abinda za ki biyani? Ke kuwa ki ke da shi, kawo kunnenki ki ji."
Bata motsa ba, tuni shi kuwa ya matso da bakinsa dab da kunnenta. Maganar da ya fad'i ce ta rud'ar da ita, da gudu ta juya ta koma kicin. Ya bita da kallo yana dariya kafin ya juya ya soma tafiya. Wayarsa ta dauki k'ara, ganin Haidar ne yasa shi dauka da sallama. Bayan sun gaisa Haidar ya ce.
"Ya Man, na ji ka shiru, ka kuwa fad'awa su Daddy?"
Faruk yana taka matattakala yana murmushi ya shafi sumar kansa. Kafin ya soma kora mishi duk yanda akayi harma da rikicinsu da Dakta Ridwan da kuma cewar Hajiya na sai ya auri Ihsan ma.
"I just don't know what to do brother, ban ta6a son Ihsan ba, ban kuma ta6a yi mata kallon budurwa ba, ina mata kallon kanwata wacce ban bambanta ta da Baraka da Ikram ba."
Haidar wanda ya yi shiru ya soma magana.
"Duk wannan bai dameni ba, kamar yanda ku ka samu sa6ani da dan uwanka ba Faruk, zan so ka je ka sameshi har gida ku fahimci juna. Banason akan lamarin aurenka a samu rarrabuwar kai a family, it's something that never happen, so please don't let it now."
Ya gamsu matuka da zancen yayannasa. Daman shima ya sauko daga fushin da ya yi da Dakta saidai kunya ce ta hanashi zuwa gidansa ya ba shi hakuri, wai shine ya nemi yi mishi rashin kunya akan ya ta6a matar da ya ke ji cikin zuciya da gangar jikinsa. Maganar Haidar ta katseshi.
"Batu kuma na Ihsan, wannan ba yanda ka iya, ka zamo mai biyayya ga umarnin iyaye ko don ka cika d'a nagari. Ka yawaita addua akan neman za6in Allah ka ji?"
Ya zauna a karshen matattakala batare da ya bude kofa ya shiga ba falonnasa ba, murmushi dauke saman fuskarsa na jin dadin maganganun dan uwansa ya ce.
"Na ji Brother, zan yi yanda ka ce, bari na yi wanka nayi breakfast, zan je gidan Dakta idan ma ban sameshi ba zan shiga asibitin."
Ya ji dadin maganarsa.
"Yauwa that's my lovely brother, haka nake son ji. Nasan anjima zai shigo, gwara ka je kafin shigowarsa, nima ina nan tafe bayan Magriba idan Allah Ya yarda, don na k'ara ganin surukartamu da akai mana 6oyon fuskarta."
Dariya Faruk ya yi kafin suyi sallama ya mik'e ya fad'a d'akinsa.
*** *** ***
RINGIM
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
72
A farfajiyar gidan suka hadu da Anti Amarya wacce ta dawo daga gidan wata kawarta, ta lura da yanayinta saidai baki kawai ta saki tana kallonta, Hajiya Mama itama ganinta ne yasa ta dan saita kanta duk da kuwa bai hana komai 6oyuwa ba. Anan kofar gidan ma Adnan ya dawo daga yiwa wasu abokansa sallama sakamakon tafiyarsa da ta k'arato nan zuwa kwana biyu ya ci karo da ita, daga yanda ta amsa sallamarsa ma yasan ba lafiya ba, ta shiga mota direba ya ja suka bar wajen. Hawayenta ya kasa tsayuwa, wannan wane irin rana ce ta zo musu? Kamar yanzu ne suke wasa da dariya da kanwartasu, ace har lamari na aure ya had'asu rikici na ban mamaki. Wai yau Madina ce ke kiran sun ci amanarta, ta nuna suna mata son kai, wannan abu da me ya yi kama? Har take nuna basu suka haifi Ihsan ba ga da ga.
Ran Hajiya Mama ya k'ara jagulewa, ta kasa hadiye kukanta, haka hawayenta ya yi ta zubowa tana daukesu da mayafinta. Babu abinda ta fi tunowa sai yanayin shakuwarsu tun suna k'anana har zuwa girmansu, yau sa6ani ya shiga tsakaninsu akan auren Ummi da Faruk.
Ta runtse ido.
'Madina ina kika mance tarbiyyar da iyayenmu suka bamu? Yaushe kika chanja daga kyawawan d'abi'unki? Ya akayi kika bari son 'yarki ya rufemiki ido har haka? Wannan abu abin kunya ne ya shiga kunnen iyayenmu. Abin kunya ne gareki idan Hajiya Babba ta ji wannan lamari.' Tana dukkan wadannan maganganun ne cikin zuciyarta. Akan hanya wayarta ta yi k'ara fiye da sau biyu amman ta kasa d'auka, tsoron dagawar ma takeyi, me zata iya cewa Hajiya Babba? Sam bazata iya da wannan abin kunyar ba wanda ta ke ganinsa tamkar a mafarki.
Adnan cikin sauri ya shiga wajen Maminsa, saidai bata falo hakan yasa ya nufi dayan falonnata, nan ma batanan, a karshe ya yanke hukunci shiga dakinta. Gefen gado ya sameta zaune tana kuka. Hankalinsa idan ya yi dubu to yau ya tashi, ya isa gabanta ya durkusa.
"Mami meke faruwa ne? Ga Hajiya Mama ta fita hankalinta a tashe tana hawaye, kema ga ki na tarar dake kina kuka, rasuwa akayi ne?"
Ta share hawayenta.
"Da rasuwa ce to da sauki don ansan tana kan kowa, wannan yafi mutuwa k'ona zuciya Adnan. Yau akan Ummi har Hajiya Mama ta mareni, sai nace tun tasowarmu da ita sa6ani irin haka bai ta6a shiga tsakaninmu ba."
Kansa ya danyi dum, ya kasa tantance tak'amaiman yanayin da ya shiga.
"Ummi kuma?" Ya furta yana dubanta.
"Kwarai kuwa." Ta kwashe maganat ta gayamishi, ya dan ji hankalinsa ya kwanta, daman ba yau ya fahimci akwai wani abu a zuciyar Faruk game da Ummi ba, shi yasan daman irin haka zata faru wataran, Faruk ya ce zai auri Ummi. Saidai Ihsan fa? Bai ta6a kawowa tana son Faruk ba. Tabbas shi bai ga aibu a had'asu ya auresu ba.
"Kayi shiru?"
Ya dago ya dubi mahaifiyarsa.
"Mami shi fa lamari na aure Allah ne Ya tsara abinsa, babu wanda zai chanja kaddararsa. Kuma..."
"Tashi ka ficemin! Shashasha kawai da baisan kishin nasa ba."
Sum-sum ya fice don ya lura ta shiga cikin zafi, da alama babu abinda zai iya fadamata a yanzun ta fahimta. Har ace ta manta irin gwagwarmayar da ta sha a baya wajen Abbansu, har ace zata mance komai na duniya rubutaccen al'amari ne, idan Allah Ya yi za'ayi, za'ayin?
Ya waigo yana mai dubanta, waya ya ga ta dauka ta na kokarin kira. Gabansa ya fad'i kada fa ta ce zata kira Hajiya Babba. Da sauri ya isa gareta ya rike hannunta.
"Don Allah Mami karkiyi haka, ki duba zumuncinku, kada a sanadin abinda bai kai ya kawo ba ki 6ata kyakkyawar alak'arku da yan uwanki wadanda kowa ya gani sai ya yi sha'awarta." Sai kuma jikinta ya danyi sanyi, ta dubeshi fuskarta har lokacin a daure.
"Tashi ka ficemin Adnan tun ban kai ga ta6a lafiyarka ba."
Ya tashi jiki a sanyaye ya fice, bata fasa kiran ba saidai jin da ya yi Ihsan ta kira ta ke tambayar ko ta taho, hankalinsa ya dan kwanta.
Ummi ta yi murmushi wanda har gefen kumatunta ya lotsa. Batasan sadda ta soma magana ba.
"Ni nasan yanda nake jin Yaya Faruk a raina Binta, akwai da yawa daga abubuwa wanda ba sai ka 6ata lokaci wajen bayyanashi ba, watakil ya nuna kansa wataran. Ina son Yaya Faruk fiye da kaina, zan iya sadaukar da nawa farincikin don kawai ya samu nasa. Binta me zance ga mutumin da ya daraja ni ya nunawa duniya ni din mutum ce mai daraja? Ke kuwa idan ban kaunaceshi ba me zan mishi?"
Binta ta yi dariya.
"Tabbas kinyi gaskiya, kin kuma burgeni matuk'a. Allah Yasa wannan kauna taku ta d'ore har ku haayyafa ku tara zuri'a guda taku."
Kunya ta hanata amsawa face murmushi da tayi.
"Ameen." Jin muryarsa yasa duk suka juyo a razane, ta zaro ido duk ta bi ta diririce, shikenan ya ji abinda ta ce kenan? Ji ta yi kamar ta nutse a k'asa don kunya. Ita kuwa Binta tana yar dariya ta russuna ta gaisheshi, ya amsa fuska a sake yana duban Ummi. Ita dinma gaisheshi ta yi dakyar sakamakon harshenta da ta ji ya yi nauyi duk don tsabar kunya.
Ya amsa yana ji kamar ya nufeta ya rukunkume don dadin da kalamanta sukayi masa.
"Zo nan Ummi."
Ya fad'a gami da juyawa ya fita. Ta bi bayanshi da kallo, daga shi sai dogon wando da singilet bak'a.
Ta dubi Binta wacce ke zungurar kafadarta tana mata nuni da ta je. Ta yi murmushi mai bayyana hak'ora cikin muryar rad'a ta ce.
"Anya bai ji maganarmu ba?"
"Lallai ke dinnan, to meye idan ya ji? Daman kinason fadamishi kin kasa kinga ya hutar da ke."
Ta girgiza kai gami da wanke hannunta da handwash sannan ta mara mishi baya.
A tsaye ta tarar da shi wajen hanyar da zata sada ka da sashensa. Ya kura mata ido kamar ya hadiyeta. Ta kauda fuskarta ta karasa gareshi.
"Meyasa kike barin wayarki a daki sai nayita kira bakya d'agawa?'
Yana maganar cikin muryar shagwa6a kamar wani k'aramin yaro, abin ma sai ya bata dariya, idan yana wannan shagwa6ar wani kyau ya ke yi mata, ita dake mace ma bazata iya yinta ba.
"Ka yi hakuri, aiki ne mukeyi."
"Naji, maimaita abinda kika fad'awa Binta yanzu a kicin."
Ta zaro ido tana kallonsa fuskarta dauke da murmushi, shima murmushin ya yi ya daga mata gira.
"Kinyi zaton ban ji ba ko? Na ji dukkab tattaunawarku, oya idan dagaske ki ke maganarki ki cemin 'Ina sonka Faruk' na ji."
'Innalillahi...' Ta karantota har karshe a ranta, gaba daya ta diririce. Shi kuwa dagaske ya ke, don tsayuwarsa ya gyara yana jiranta.
"Kinyi shiru."
Ta hau wasa da yatsunta, murya a raunane ta ce.
"Ni..ni ban ta6a fad'a ba fa."
"Shiyasa nakeso ki fad'amin, ya zama ni ne farko nine kuma karshen wanda za ki fad'awa hakan ok?"
Ta runtse ido, yau ta shiga uku, ji ta ke yi kalaman sun yi mata nauyi da tsauri, bazata iya fad'a ba. Ya dan saka saman yatsansa manuniya ya zunguri hannunta.
"Kin yi shiru Ummina."
Ta ja baya kadan ta hadiyi miyau.
"Ka yi hakuri don Allah."
Ya lura a tsorace ta ke ma, sai kawai ya yi murmushi.
"Ki ka ce ba ki da abinda za ki biyani? Ke kuwa ki ke da shi, kawo kunnenki ki ji."
Bata motsa ba, tuni shi kuwa ya matso da bakinsa dab da kunnenta. Maganar da ya fad'i ce ta rud'ar da ita, da gudu ta juya ta koma kicin. Ya bita da kallo yana dariya kafin ya juya ya soma tafiya. Wayarsa ta dauki k'ara, ganin Haidar ne yasa shi dauka da sallama. Bayan sun gaisa Haidar ya ce.
"Ya Man, na ji ka shiru, ka kuwa fad'awa su Daddy?"
Faruk yana taka matattakala yana murmushi ya shafi sumar kansa. Kafin ya soma kora mishi duk yanda akayi harma da rikicinsu da Dakta Ridwan da kuma cewar Hajiya na sai ya auri Ihsan ma.
"I just don't know what to do brother, ban ta6a son Ihsan ba, ban kuma ta6a yi mata kallon budurwa ba, ina mata kallon kanwata wacce ban bambanta ta da Baraka da Ikram ba."
Haidar wanda ya yi shiru ya soma magana.
"Duk wannan bai dameni ba, kamar yanda ku ka samu sa6ani da dan uwanka ba Faruk, zan so ka je ka sameshi har gida ku fahimci juna. Banason akan lamarin aurenka a samu rarrabuwar kai a family, it's something that never happen, so please don't let it now."
Ya gamsu matuka da zancen yayannasa. Daman shima ya sauko daga fushin da ya yi da Dakta saidai kunya ce ta hanashi zuwa gidansa ya ba shi hakuri, wai shine ya nemi yi mishi rashin kunya akan ya ta6a matar da ya ke ji cikin zuciya da gangar jikinsa. Maganar Haidar ta katseshi.
"Batu kuma na Ihsan, wannan ba yanda ka iya, ka zamo mai biyayya ga umarnin iyaye ko don ka cika d'a nagari. Ka yawaita addua akan neman za6in Allah ka ji?"
Ya zauna a karshen matattakala batare da ya bude kofa ya shiga ba falonnasa ba, murmushi dauke saman fuskarsa na jin dadin maganganun dan uwansa ya ce.
"Na ji Brother, zan yi yanda ka ce, bari na yi wanka nayi breakfast, zan je gidan Dakta idan ma ban sameshi ba zan shiga asibitin."
Ya ji dadin maganarsa.
"Yauwa that's my lovely brother, haka nake son ji. Nasan anjima zai shigo, gwara ka je kafin shigowarsa, nima ina nan tafe bayan Magriba idan Allah Ya yarda, don na k'ara ganin surukartamu da akai mana 6oyon fuskarta."
Dariya Faruk ya yi kafin suyi sallama ya mik'e ya fad'a d'akinsa.
*** *** ***
RINGIM
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
72
A farfajiyar gidan suka hadu da Anti Amarya wacce ta dawo daga gidan wata kawarta, ta lura da yanayinta saidai baki kawai ta saki tana kallonta, Hajiya Mama itama ganinta ne yasa ta dan saita kanta duk da kuwa bai hana komai 6oyuwa ba. Anan kofar gidan ma Adnan ya dawo daga yiwa wasu abokansa sallama sakamakon tafiyarsa da ta k'arato nan zuwa kwana biyu ya ci karo da ita, daga yanda ta amsa sallamarsa ma yasan ba lafiya ba, ta shiga mota direba ya ja suka bar wajen. Hawayenta ya kasa tsayuwa, wannan wane irin rana ce ta zo musu? Kamar yanzu ne suke wasa da dariya da kanwartasu, ace har lamari na aure ya had'asu rikici na ban mamaki. Wai yau Madina ce ke kiran sun ci amanarta, ta nuna suna mata son kai, wannan abu da me ya yi kama? Har take nuna basu suka haifi Ihsan ba ga da ga.
Ran Hajiya Mama ya k'ara jagulewa, ta kasa hadiye kukanta, haka hawayenta ya yi ta zubowa tana daukesu da mayafinta. Babu abinda ta fi tunowa sai yanayin shakuwarsu tun suna k'anana har zuwa girmansu, yau sa6ani ya shiga tsakaninsu akan auren Ummi da Faruk.
Ta runtse ido.
'Madina ina kika mance tarbiyyar da iyayenmu suka bamu? Yaushe kika chanja daga kyawawan d'abi'unki? Ya akayi kika bari son 'yarki ya rufemiki ido har haka? Wannan abu abin kunya ne ya shiga kunnen iyayenmu. Abin kunya ne gareki idan Hajiya Babba ta ji wannan lamari.' Tana dukkan wadannan maganganun ne cikin zuciyarta. Akan hanya wayarta ta yi k'ara fiye da sau biyu amman ta kasa d'auka, tsoron dagawar ma takeyi, me zata iya cewa Hajiya Babba? Sam bazata iya da wannan abin kunyar ba wanda ta ke ganinsa tamkar a mafarki.
Adnan cikin sauri ya shiga wajen Maminsa, saidai bata falo hakan yasa ya nufi dayan falonnata, nan ma batanan, a karshe ya yanke hukunci shiga dakinta. Gefen gado ya sameta zaune tana kuka. Hankalinsa idan ya yi dubu to yau ya tashi, ya isa gabanta ya durkusa.
"Mami meke faruwa ne? Ga Hajiya Mama ta fita hankalinta a tashe tana hawaye, kema ga ki na tarar dake kina kuka, rasuwa akayi ne?"
Ta share hawayenta.
"Da rasuwa ce to da sauki don ansan tana kan kowa, wannan yafi mutuwa k'ona zuciya Adnan. Yau akan Ummi har Hajiya Mama ta mareni, sai nace tun tasowarmu da ita sa6ani irin haka bai ta6a shiga tsakaninmu ba."
Kansa ya danyi dum, ya kasa tantance tak'amaiman yanayin da ya shiga.
"Ummi kuma?" Ya furta yana dubanta.
"Kwarai kuwa." Ta kwashe maganat ta gayamishi, ya dan ji hankalinsa ya kwanta, daman ba yau ya fahimci akwai wani abu a zuciyar Faruk game da Ummi ba, shi yasan daman irin haka zata faru wataran, Faruk ya ce zai auri Ummi. Saidai Ihsan fa? Bai ta6a kawowa tana son Faruk ba. Tabbas shi bai ga aibu a had'asu ya auresu ba.
"Kayi shiru?"
Ya dago ya dubi mahaifiyarsa.
"Mami shi fa lamari na aure Allah ne Ya tsara abinsa, babu wanda zai chanja kaddararsa. Kuma..."
"Tashi ka ficemin! Shashasha kawai da baisan kishin nasa ba."
Sum-sum ya fice don ya lura ta shiga cikin zafi, da alama babu abinda zai iya fadamata a yanzun ta fahimta. Har ace ta manta irin gwagwarmayar da ta sha a baya wajen Abbansu, har ace zata mance komai na duniya rubutaccen al'amari ne, idan Allah Ya yi za'ayi, za'ayin?
Ya waigo yana mai dubanta, waya ya ga ta dauka ta na kokarin kira. Gabansa ya fad'i kada fa ta ce zata kira Hajiya Babba. Da sauri ya isa gareta ya rike hannunta.
"Don Allah Mami karkiyi haka, ki duba zumuncinku, kada a sanadin abinda bai kai ya kawo ba ki 6ata kyakkyawar alak'arku da yan uwanki wadanda kowa ya gani sai ya yi sha'awarta." Sai kuma jikinta ya danyi sanyi, ta dubeshi fuskarta har lokacin a daure.
"Tashi ka ficemin Adnan tun ban kai ga ta6a lafiyarka ba."
Ya tashi jiki a sanyaye ya fice, bata fasa kiran ba saidai jin da ya yi Ihsan ta kira ta ke tambayar ko ta taho, hankalinsa ya dan kwanta.