Sashe 57
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*** *** ***
ABUJA
Hajiya Babba duk ta bi ta damu akan rashin amsa kiranta da Kanwarta Sadiya bata yi ba, batason kiran Mami tukunna.
Ihsan ta shigo da sallamarta ta yi shirin tafiya don tuni an fita da kayanta, sam lokacin ma batasan anfasa tafiyar da Ummi ba. Ganinta yasa Hajiya sakin fuska tana dubanta.
"A'a, d'iyata har an fito?"
Fuskar Ihsan ba walwala sosai ta amsa.
"Eh Hajiya, an fita da kaya ma."
Hajiya ta gyada kai.
"Zo ki zauna mu danyi wata magana."
Ta zauna a gefen Hajiyar kamar yanda ta umarceta.
"Ihsan inaso kiyimin kyakkyawar fahimta akan maganar da nakeson yi dake. Zamanki anan tare da mu yasa na fahimci kamar kina son Sadauki, ban tabbatar da hakan bane saida naji daga bakin Ikram. To sai kuma Sadauki ya zo mana da zancen Ummi tashi guda da sunan ita ya ke so da aure. Saidai ya amince zai hadaku tare ya aura. Ina fatan baki da matsala akan hakan?"
Takaici ya hana Ihsan magana, lallai ma ta yaya ake zaton za ta yi zaman kishi da 'yar aikin gidansu? Wannan ma jawowa kai raini ne wallahi. Haushin Hajiya ma ya hanata cewa uffan har lokacin kanta yana k'asa.
Hajiya ta yi shiru tana karantarta, sai kuma ta numfasa.
"Ki je Ihsan ki yi tunani, bazan matsamaki ba. Ke tawa ce, bazan k'i farincikinki ba kema, bazan kuma so k'untata miki akan wata ba. Dake da Sadauki abu daya na daukeku, babu wanda zanso shiga hakkinsa."
Ihsan ta sauke ajiyar zuciya.
'Kedai kome za ki ce daga baya ne kin riga kin nuna son danki fiye da kowa."
Cewar Ihsan a zuciya. Shigowar Binta ce ya katse maganar. Suka amsa sallamarta.
"Ya ce ta fito."
Ta mike Hajiya na mata adduar komawa lafiya itama tana godiyar abubuwan alherin da suka bata. Saida zata shiga motar ne ta dubi Ikram.
"Wai bada Ummi za mu tafi ba?" Kafin Ikram ta amsa Hajiya ta amsa.
"Ki je zata zo."
Ran Ihsan ya k'ara yin bak'i, kenan plan dinsu da Ikram ya tashi a banza? Niyyarsu da zarar ta koma Kano a koreta sai aga ta aurenta da Faruk, ranta ya yi wani irin daci, a fusace ta shiga motar ta banko murfin. Mamaki ya kama Hajiya, anya babu wata a k'asa? Daman ta lura kamar bata yi na'am da maganganunta ba. Haka ta bi bayan motar da kallo, tuni haushi da 6acin rai yasa Ikram juyawa ciki. Watakil nan gaba ma Ummi ta zama mai mulkar kowa a gidan, don taga alama ta samun kar6uwarta wajen Hajiya da Daddy. Acewarta DAN ADAM tara ya ke bai cika goma ba, zasu ga hali na butulci da Ummi za ta yi musu nan gaba indai akayi auren. Don ta sha jin labaru na irin hakan.
Ummi duk tana kallon abinda ke faruwa, daman tun jiya da dare Hajiya ta sanarmata an fasa tafiyar da ita, sannan Faruk ya kira ya bata tabbacin kada ta sake ta shirya da zummar komawa Kano, ta daina aikatau daga ranar.
Ta saki labulen kicin din gami da sauke ajiyar zuciya ranta ya danyi haske, ko babu komai alwashin da Ihsan ta ci akanta bazai tabbatu ba. Yanzu ita ina tasan zata ta samu motar garinsu idan suka korata? Saidai da tambaya kam. Ita har fargabar komawarta Ringim take, ko wane k'alubalen zata fuskanta a wajen Saude da Babanta?
"Ke!" Ta firgita matuk'a ta juyo idanunta a zare kirjinta a sama don ji tayi har numfashinta ma kamar yana barazanar daukewa. Ganin Binta yasa ta dafe kirjinta gami da rufe ido tana sauke ajiyar zuciya. Dariya sosai Binta ta sanya, Ummi ta girgiza kai.
"Wallahi ba ki ji yanda na tsorata ba, kai Binta saiki kashe mutum."
Binta cikin dariya ta daga mata hannu.
"Yi hakuri, daman cewa nayi bari nagani ko za ki tsoratan, na manta yanzu ke fa a tsorace kike da kowa ma."
Ta yi murmushi tana tattare tafarnuwar da ta zubar a k'asa don kid'ima.
"Na yi zaton Ikram ce ko Ihsan din ce ta dawo."
Sukayi dariya. Kafin kuma Ummi ta cigaba da 6arar tafarnuwa.
Binta ta dubeta sa'ilin da ta janyo robar kifin da ta saka a ruwa don ya yi kankara ta soma kokarin gyarawa.
"Wai ni don Allah meyasa ban ta6a jin kin fad'i wani daddad'an kalami na soyayya ba game da Yalla6ai? Sai nake ganin kamar ya fi sonki fiye da yanda ke kika daukeshi."
Wannan tambaya ta Binta, yasa Faruk cin burki daga kofar kicin don ya zo ne daman da niyyar tuhumar Ummi dalilinta na barin waya a daki ga shi yana ta kira.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
74
RINGIM
Bud'a ne ya cika gidan Baba Habiba sakamakon auren da aka daura na Zahraddeen da Khadija. Yawanci gaba daya danginta ne suak halarci bikin, daidaiku ne cikin dangin Malam Yahuza suka zo, wadanda zuwansu ma ba amfani awajen Baba Habiba don acewarta sun zo kwasar rahoto da gulma.
Ita da aminiyarta Saude sun yi shiga ta sutura har kala uku ana yi ana chanjawa, Amarya kuwa kusan kala biyar ta yi domin wannan ranar. Da yamma Amarya na cikin taron jama'a suna gaisawa, wata yar uwarsu ta zo kiranta.
"Kizo kinyi bak'i fa daga Kano." Ta bi bayanta da mamaki don iyakar saninta bata da kowa a Kano. Gabanta ya bada wani bugu mai karfi ganin Raihana cikin shiga ta wata shegiyar shadda mai tsadar gaske, daidai da sark'ar da dan kunnenta abin kallo ne, ballantana kuma idan ka dubi agogo da awarwaronta kasan na gwal ne. Tana da 'yar k'iba hakanan doguwa ce, ba laifi tana da kyau daidai gwargwado, wacce suke taren itama ta ci nata adon har ta gaji da haduwa. Murmushi Raihana ke jifanta da shi da wani dan iskan kallo wanda bai kyautu a matsayinta na yar uwarta mace ta yi mata ba. Ta daure ta k'ak'alo murmushin yak'e ganin cewa cikin mutane ne.
"A'a, Raihana kece a garinnamu? Sannunki da zuwa."
Raihana da har lokacin bata bar murmushi ba ta amsa.
"Yauwa Dijat , ke kuma haka akeyi?"
Dija ta rude gudun kada ta ce wani abu da mutane zasu dagosu, tana shirin kwa6arta Baba Habiba ta karaso wajen duk ta had'a zufa saboda shiga da fita. Ganinsu yasa ta washe baki kamar gonar auduga, ta bisu da kallo daga sama zuwa k'asa sannan ta dubi Dija.
"Wadannan fa?"
'K'awayena ne na yanar gizo, sun zo tayani murna ne."
"A'a sannunku kun ji ko? Ina wuninki?"
Ba kunya ta gaishesu, kasancewar suma yan duniya ne sai suka amsa.
"A'a baza'a barsu anan ba kinga nan a cike yake, kaisu gidan Saude su zauna. Bari na kar6o muku muk'ulli."
Daga haka ta karasa ga Saude ta Kar6o ta damk'awa Dija.
"Jeki can na kawomiki kazar ma ki ci acan kinga asiri a rufe." Ta fada cikin k'ank'an da murya. Dija ta murtuke fuska.
"Aa, ki barshi sai dare.". "To shikenan."
Ta ja su Raihana zuwa gidan Saude. Bayan sun zauna Raihana ta rik'o hannunta idanunta sun kada tsabar kishi.
"Ba ki kyautamin ba Dijat, yanzu wannan kwalliyar duk don Deen kikayi ba don ni na ganki na ji dadi ba? Haba Dijat, ba ki ta6a yimin kwalliya irin haka kin aikomin na gani ba." (Wa'iyazubillah)
Dija ta daure fuska gami da zame hannunta.
"Ki bar wannan magana mana Raihana, ke meyasa kike da sa6a alk'awari? Ban gargadeki kada ki zo gidanmu bane?"
Raihana ta yi raurau da fuska.
"To ya na iya tunda dai kin kashe wayarki kwana biyu bana samunki, ni kuma hankalina duk ya tashi na ji tsoron kada ki juyamin baya shine na zo."
Dija ta ja tsaki sannan ta mik'e.
"Ina zuwa." Daga haka ta fice, Raihana da abokiyar tafiyarta, Saima, suka bita da kallo cike da shaawa.
Saima ta maido dubanta ga Raihana.
"Ashe dai a kauye ana samun mata har haka? Ke kam kinyi dace."
Ta daure fuska.
"To meye naki ciki?"
"Aa, bakomai ranki ya dade, ni mamakin ma da nakeyi ya zaayi kamarki ki zauna wai wannan ta gagareki juyawa? Haba Hanah, dubun da suka fi ta ma kin shawo kansu ta hanyar malamai balle kuma ita?"
Raihana ta numfasa.
"Ni wannan so nakeyi mata na gaske, ba don ta kafe akan wannan shegen Deen din ba da har aurenta zan so yi. (Waiyazubillah) saidai ya zo yana son yimin shigar sauri."
Saima ta jinjina kai, lallai ba karamin so take yiwa Dija ba, banda haka, manyan mata nawa ne suka so samun wannan damar amman ta k'i basu sai ita?
Duk yanda taso ta shawo kan Dija abu ya ci tura don kwata-kwata bata bada fuska ba, ta ce ko menene sai ta je Kaduna, haka gwuiwa a sake Raihana ta juya bayan ta bata makudan kudade da suka girgizata.
Washegari aka tattarata aka mik'a Kaduna gidan Deen, har lokacin Munira bata dawo ba tana Ringim don ta ce bazata iya ganin rawar kan da mijinta zaiyi akan yar uwarta ba da ta ci amanar yan uwantaka.
Gudu ta ke yi itama tana binta a guje suna k'ara runtumawa cikin dajin da babu gida gaba babu a baya, har ya kai ta taka k'aya, ta zube a wajen tana numfarfashi, takobi ne shar6e6iya sai kyalli ta ke, doguwar mace kyakkyawa ce rik'e da wuk'ar kafin akan idanunta ta fuskarta ta rikid'e zuwa kalar kore.
"Saina kasheki! Saina kasheki ke Makira!!"
Tana ihun kuka tana fadin kiyi hakuri na tuba Hasiya karkimin haka don Allah. Amma ina bata ko saurareta ba ta daga takobin nan, ai kuwa ta fasa k'ara.
ABUJA
Hajiya Babba duk ta bi ta damu akan rashin amsa kiranta da Kanwarta Sadiya bata yi ba, batason kiran Mami tukunna.
Ihsan ta shigo da sallamarta ta yi shirin tafiya don tuni an fita da kayanta, sam lokacin ma batasan anfasa tafiyar da Ummi ba. Ganinta yasa Hajiya sakin fuska tana dubanta.
"A'a, d'iyata har an fito?"
Fuskar Ihsan ba walwala sosai ta amsa.
"Eh Hajiya, an fita da kaya ma."
Hajiya ta gyada kai.
"Zo ki zauna mu danyi wata magana."
Ta zauna a gefen Hajiyar kamar yanda ta umarceta.
"Ihsan inaso kiyimin kyakkyawar fahimta akan maganar da nakeson yi dake. Zamanki anan tare da mu yasa na fahimci kamar kina son Sadauki, ban tabbatar da hakan bane saida naji daga bakin Ikram. To sai kuma Sadauki ya zo mana da zancen Ummi tashi guda da sunan ita ya ke so da aure. Saidai ya amince zai hadaku tare ya aura. Ina fatan baki da matsala akan hakan?"
Takaici ya hana Ihsan magana, lallai ma ta yaya ake zaton za ta yi zaman kishi da 'yar aikin gidansu? Wannan ma jawowa kai raini ne wallahi. Haushin Hajiya ma ya hanata cewa uffan har lokacin kanta yana k'asa.
Hajiya ta yi shiru tana karantarta, sai kuma ta numfasa.
"Ki je Ihsan ki yi tunani, bazan matsamaki ba. Ke tawa ce, bazan k'i farincikinki ba kema, bazan kuma so k'untata miki akan wata ba. Dake da Sadauki abu daya na daukeku, babu wanda zanso shiga hakkinsa."
Ihsan ta sauke ajiyar zuciya.
'Kedai kome za ki ce daga baya ne kin riga kin nuna son danki fiye da kowa."
Cewar Ihsan a zuciya. Shigowar Binta ce ya katse maganar. Suka amsa sallamarta.
"Ya ce ta fito."
Ta mike Hajiya na mata adduar komawa lafiya itama tana godiyar abubuwan alherin da suka bata. Saida zata shiga motar ne ta dubi Ikram.
"Wai bada Ummi za mu tafi ba?" Kafin Ikram ta amsa Hajiya ta amsa.
"Ki je zata zo."
Ran Ihsan ya k'ara yin bak'i, kenan plan dinsu da Ikram ya tashi a banza? Niyyarsu da zarar ta koma Kano a koreta sai aga ta aurenta da Faruk, ranta ya yi wani irin daci, a fusace ta shiga motar ta banko murfin. Mamaki ya kama Hajiya, anya babu wata a k'asa? Daman ta lura kamar bata yi na'am da maganganunta ba. Haka ta bi bayan motar da kallo, tuni haushi da 6acin rai yasa Ikram juyawa ciki. Watakil nan gaba ma Ummi ta zama mai mulkar kowa a gidan, don taga alama ta samun kar6uwarta wajen Hajiya da Daddy. Acewarta DAN ADAM tara ya ke bai cika goma ba, zasu ga hali na butulci da Ummi za ta yi musu nan gaba indai akayi auren. Don ta sha jin labaru na irin hakan.
Ummi duk tana kallon abinda ke faruwa, daman tun jiya da dare Hajiya ta sanarmata an fasa tafiyar da ita, sannan Faruk ya kira ya bata tabbacin kada ta sake ta shirya da zummar komawa Kano, ta daina aikatau daga ranar.
Ta saki labulen kicin din gami da sauke ajiyar zuciya ranta ya danyi haske, ko babu komai alwashin da Ihsan ta ci akanta bazai tabbatu ba. Yanzu ita ina tasan zata ta samu motar garinsu idan suka korata? Saidai da tambaya kam. Ita har fargabar komawarta Ringim take, ko wane k'alubalen zata fuskanta a wajen Saude da Babanta?
"Ke!" Ta firgita matuk'a ta juyo idanunta a zare kirjinta a sama don ji tayi har numfashinta ma kamar yana barazanar daukewa. Ganin Binta yasa ta dafe kirjinta gami da rufe ido tana sauke ajiyar zuciya. Dariya sosai Binta ta sanya, Ummi ta girgiza kai.
"Wallahi ba ki ji yanda na tsorata ba, kai Binta saiki kashe mutum."
Binta cikin dariya ta daga mata hannu.
"Yi hakuri, daman cewa nayi bari nagani ko za ki tsoratan, na manta yanzu ke fa a tsorace kike da kowa ma."
Ta yi murmushi tana tattare tafarnuwar da ta zubar a k'asa don kid'ima.
"Na yi zaton Ikram ce ko Ihsan din ce ta dawo."
Sukayi dariya. Kafin kuma Ummi ta cigaba da 6arar tafarnuwa.
Binta ta dubeta sa'ilin da ta janyo robar kifin da ta saka a ruwa don ya yi kankara ta soma kokarin gyarawa.
"Wai ni don Allah meyasa ban ta6a jin kin fad'i wani daddad'an kalami na soyayya ba game da Yalla6ai? Sai nake ganin kamar ya fi sonki fiye da yanda ke kika daukeshi."
Wannan tambaya ta Binta, yasa Faruk cin burki daga kofar kicin don ya zo ne daman da niyyar tuhumar Ummi dalilinta na barin waya a daki ga shi yana ta kira.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
74
RINGIM
Bud'a ne ya cika gidan Baba Habiba sakamakon auren da aka daura na Zahraddeen da Khadija. Yawanci gaba daya danginta ne suak halarci bikin, daidaiku ne cikin dangin Malam Yahuza suka zo, wadanda zuwansu ma ba amfani awajen Baba Habiba don acewarta sun zo kwasar rahoto da gulma.
Ita da aminiyarta Saude sun yi shiga ta sutura har kala uku ana yi ana chanjawa, Amarya kuwa kusan kala biyar ta yi domin wannan ranar. Da yamma Amarya na cikin taron jama'a suna gaisawa, wata yar uwarsu ta zo kiranta.
"Kizo kinyi bak'i fa daga Kano." Ta bi bayanta da mamaki don iyakar saninta bata da kowa a Kano. Gabanta ya bada wani bugu mai karfi ganin Raihana cikin shiga ta wata shegiyar shadda mai tsadar gaske, daidai da sark'ar da dan kunnenta abin kallo ne, ballantana kuma idan ka dubi agogo da awarwaronta kasan na gwal ne. Tana da 'yar k'iba hakanan doguwa ce, ba laifi tana da kyau daidai gwargwado, wacce suke taren itama ta ci nata adon har ta gaji da haduwa. Murmushi Raihana ke jifanta da shi da wani dan iskan kallo wanda bai kyautu a matsayinta na yar uwarta mace ta yi mata ba. Ta daure ta k'ak'alo murmushin yak'e ganin cewa cikin mutane ne.
"A'a, Raihana kece a garinnamu? Sannunki da zuwa."
Raihana da har lokacin bata bar murmushi ba ta amsa.
"Yauwa Dijat , ke kuma haka akeyi?"
Dija ta rude gudun kada ta ce wani abu da mutane zasu dagosu, tana shirin kwa6arta Baba Habiba ta karaso wajen duk ta had'a zufa saboda shiga da fita. Ganinsu yasa ta washe baki kamar gonar auduga, ta bisu da kallo daga sama zuwa k'asa sannan ta dubi Dija.
"Wadannan fa?"
'K'awayena ne na yanar gizo, sun zo tayani murna ne."
"A'a sannunku kun ji ko? Ina wuninki?"
Ba kunya ta gaishesu, kasancewar suma yan duniya ne sai suka amsa.
"A'a baza'a barsu anan ba kinga nan a cike yake, kaisu gidan Saude su zauna. Bari na kar6o muku muk'ulli."
Daga haka ta karasa ga Saude ta Kar6o ta damk'awa Dija.
"Jeki can na kawomiki kazar ma ki ci acan kinga asiri a rufe." Ta fada cikin k'ank'an da murya. Dija ta murtuke fuska.
"Aa, ki barshi sai dare.". "To shikenan."
Ta ja su Raihana zuwa gidan Saude. Bayan sun zauna Raihana ta rik'o hannunta idanunta sun kada tsabar kishi.
"Ba ki kyautamin ba Dijat, yanzu wannan kwalliyar duk don Deen kikayi ba don ni na ganki na ji dadi ba? Haba Dijat, ba ki ta6a yimin kwalliya irin haka kin aikomin na gani ba." (Wa'iyazubillah)
Dija ta daure fuska gami da zame hannunta.
"Ki bar wannan magana mana Raihana, ke meyasa kike da sa6a alk'awari? Ban gargadeki kada ki zo gidanmu bane?"
Raihana ta yi raurau da fuska.
"To ya na iya tunda dai kin kashe wayarki kwana biyu bana samunki, ni kuma hankalina duk ya tashi na ji tsoron kada ki juyamin baya shine na zo."
Dija ta ja tsaki sannan ta mik'e.
"Ina zuwa." Daga haka ta fice, Raihana da abokiyar tafiyarta, Saima, suka bita da kallo cike da shaawa.
Saima ta maido dubanta ga Raihana.
"Ashe dai a kauye ana samun mata har haka? Ke kam kinyi dace."
Ta daure fuska.
"To meye naki ciki?"
"Aa, bakomai ranki ya dade, ni mamakin ma da nakeyi ya zaayi kamarki ki zauna wai wannan ta gagareki juyawa? Haba Hanah, dubun da suka fi ta ma kin shawo kansu ta hanyar malamai balle kuma ita?"
Raihana ta numfasa.
"Ni wannan so nakeyi mata na gaske, ba don ta kafe akan wannan shegen Deen din ba da har aurenta zan so yi. (Waiyazubillah) saidai ya zo yana son yimin shigar sauri."
Saima ta jinjina kai, lallai ba karamin so take yiwa Dija ba, banda haka, manyan mata nawa ne suka so samun wannan damar amman ta k'i basu sai ita?
Duk yanda taso ta shawo kan Dija abu ya ci tura don kwata-kwata bata bada fuska ba, ta ce ko menene sai ta je Kaduna, haka gwuiwa a sake Raihana ta juya bayan ta bata makudan kudade da suka girgizata.
Washegari aka tattarata aka mik'a Kaduna gidan Deen, har lokacin Munira bata dawo ba tana Ringim don ta ce bazata iya ganin rawar kan da mijinta zaiyi akan yar uwarta ba da ta ci amanar yan uwantaka.
Gudu ta ke yi itama tana binta a guje suna k'ara runtumawa cikin dajin da babu gida gaba babu a baya, har ya kai ta taka k'aya, ta zube a wajen tana numfarfashi, takobi ne shar6e6iya sai kyalli ta ke, doguwar mace kyakkyawa ce rik'e da wuk'ar kafin akan idanunta ta fuskarta ta rikid'e zuwa kalar kore.
"Saina kasheki! Saina kasheki ke Makira!!"
Tana ihun kuka tana fadin kiyi hakuri na tuba Hasiya karkimin haka don Allah. Amma ina bata ko saurareta ba ta daga takobin nan, ai kuwa ta fasa k'ara.