← Book details Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 116

Sashe 59

Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Habiba da Saude suna komowa Ringim kai tsaye wajen bokanyarsu suka zarce. Suna isa bayan anmusu iso suka shiga gami da zubewa agaban Uwar Biyu mai bori. Habiba ta zayyanemata dukkan yanda ya faru a mafarki.
   Ta mike ta soma jijjige jiggigenta da kad'e-kad'e kafin ta zauna fuska a murtuke sai kuma ta kyakyace da dariya wanda ya razanasu ya kada yan hanjin cikinsu. Maganarta ta katse tunaninsu.
   "Karki damu kanki! Wannan ba komai bane sai shaida na cewar diyarta na nan tafe da wata gagarumar nasara a rayuwa wanda zai iya janyo tonon silili kala-kala ciki harda mutuwar auren daya a cikinku! Abubuwa da yawa a rufe su ke nakasa fahimta amman ina mai tabbatarmuku ba mai kyau bane gareku! Wannan duk ba damuwa bane idan ni Ade Mai Bori na raye to ba bazai afku ba ko kadan!"
   Cikinsu ya k'ulle tsabar rud'u, Saude har fitsari ta soma a wando, Habiba da ta soma had'a gumi ga jiki da ya dauki rawa ta daure ta soma magana cike da dauriya.
  "Mudai yanzu bokanya da ke muka dogara, ki taimakemu ki fiddamu wannan hatsari."  (Waiyazubillah)
      Dariya na hauka Ade Mai Bori ta yi kafin ta yiwa kanta kirari cikin karaji sannan ta dubesu fuska murtuke.
"Zan yi muku aiki fiye da yanda na rufemuku bakin shegu a baya! Me ku ke bukata?"
  Saude ta riga Habiba magana.
"Idan da hali a kashe Ummi!"
Ta tsaya ta gama tsaface-tsafacenta kafin ta dubesu idanuwa a zazzare.
"A'a! Na duba wannan bazai yiwu ba!"
Saude da hawaye ya tahomata ta kasa magana sai rawar jiki, Habiba ta cafe.
  "Bokanya nidai a haukatar da ita yanda bazata yi amfani ba koda ta zo."
  Ta gama tabbatarwa da ba mai yiwuwa bane ba a hanyar tsafinta, saidai bata son ko kusa ta nuna gazawarta har karo na biyu hakan yasa ta kyakyacewa da dariya.
"Angama!!! Ko garinnan ba zata ta6a waiwaye ba!!!"
  Ransu ya danyi sanyi, suka had'a duk kudaden dake jikinsu wanda ya kai dubu ashirin suka ajiyemata. Haka suka baro wajen hankali tashi, Saude suna fita ta ke6e bayan gini ta rage mararta, tana ji cikinta na kad'a saidai ta danne har su isa gida ta kasaye. A hanya babu wanda ya iya magana kowanne tunaninsa ya ke yi, duk tunaninsu ya basu cewar karshensu fa ya kusanto. Babu babban abinda ya k'ara hargitsasu sai mutuwar auren dayansu da Bokanya ta ambata. 
    Ko kan wa zai fad'a???

  Koda suka isa a gidan Saude suka yada zango, saida Saude ta rage cikinta sannan ta samu zama don su tattauna, alokacin kuma Mariya ta shigo gidan daga gidan makwafciyarsu acan ta kwana. 
  "Habiba, kinji kuma sabuwar masifa ko?"
Habiba ta numfasa.
"Hum, bari kawai Saude, wallahi don ba ki ji yanda kwakwalwata ta dauki chaji ba, kai wannan jarabar da me ta yi kama? Da nasan akwai wannan ranar tafe wallahi da sadda na gama da shegiya lokacin zan gama da ita itama. Ni na yi zaton shikenan ta zama hanyar arziki ashe akwai sauran rina a kaba?"
  Saude ta share gumi da mayafinta.
  "Wallahi dadin da naji daya ne, na cewa da Bokanya ta yi zata haukata mana ita, kinga shikenan sai daga nan ta k'ara gaba, idan ma ta samu motar da ta kad'eta, mun huta."
  Habiba ta saki fuska.
"Allah Yasa hakan."
"Ameen dai."
  Nan suka cigaba da maganar, hankalin Saude ya kai ga diyarta Mariya da ta zura hannu a wando ta yi shiru tana kallonsu. Cikin tsawa ta ce. "Ke ciremin hannu daga nan tun ban bubbugeki ba!"
  Habiba ta mik'e gwuiwa a sake.
"Atoh, ki ka sani ko k'aik'ayi ne?"
"Ai ina zaton haka, mantawa na yi ma ina son kar6omata maganin sanyi wajen Bokanya, wannan yawan soshe-soshen ya isheni."
  "Yafi dai kam idan ba so ki ke ta diyarki ta 6aci tun yanzu ba. Bari na je na huta gajiyar bikinnan tunda hankali ya kwanta."
Saude ta taka mata har kofar gida kafin su yi sallama itama ta koma ga harkokin gabanta batare da ta k'ara maida hankali ga yarinyar ba....!
                    ***  ***  ***
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
76
                       ABUJA
  Faruk kuwa yanda sukayi da Haidar ya yi, ya shirya ya wuce gidan Dakta.  Bai iskeshi ba sai Jidda da ta hau shi da tsiya akan ta ji da auren wacce kuma ya 6ige.
"Amman wallahi ka bamu kunya."
Ya watsamata wani kallo yaso ya tanka sai kuma ya tuna maganganun Haidar, bazai so kam zumunci ya 6aci ba. Ya yi kwafa.
"Kin fa ci darajar yarana, da a yau za ki koma Ghana."
Ta yi dariyar k'ular da shi.
"Dad'in abun ba kauye na tashi ba ballantana na tsoraci komawa."
  Bai ko k'ara kallonta ba ya fice yana murmushin kinyi kad'an.
   Kai tsaye asibitin da Dakta Ridwan ya ke ya isa. Duk da ba ranar aiki ba ya shiga don duba wata mai nak'uda da ta samu 'yar tangard'a, ya yi nasarar ciro bebin lafiya yana cikin dinketa ne, ya hango kaninnasa daga jikin windo kasancewar windon gilas ne, ya dubi nos dake gefensa cikin fad'a.
"Ba ki da hankali ne? Ta ya ya za'a barmin windo bud'e ina aiki?"
  "I'm sorry Sir."
Daga haka ta karasa cikin sauri ta saki labulen, murmushi Faruk ya yi ya zura hannuwa a aljihu kafin ya wuce kai tsaye ofishin Dakta. Zama ya yi akan kujerarsa yana kalle-kalle kafin ya ta6e baki.
"Wani aikin sai likita, duk wani jagwal suna gani."
Ya k'arashe kafin idanunsa ya kai ga dan karamin frame din dake saman teburin, su hud'u ne a hoton wanda akayi musu ran bikin Ridwan din.  Idanun Faruk a rufe don lokacin ma bai zama cikakken matashi ba, su kuwa sun dubeshi suna dariya aka yi hoton. Murmushi ya yi, shi kam haka Allah Ya yishi bai fiyeson hoto ba. Duk da dai yayyunnasa sun ce bikinsa ne da baizo ba, muddin ya tashi aure watakil ma da kansa zai dunga kiran mai hoton ya dauka. Yakan yi dariya don yana ganin lamarin wasa kawai.
   Baifi mintuna goma ba sai ga Dakta ya shigo. Yana ganinsa ya tsaya ya daure fuska.
  "Get out of my office."
Ya fada yana mishi nuni da k'ofa. Faruk ya mike tsaye ya na dubansa fuskarsa dauke da damuwa. Ganin ba shi da niyya yasa Dakta soma tattara abin amfaninsa zai wuce gida don daman abinda ya shigo da shi kenan, da sauri ya sha gabansa ya rungumeshi.
"Please forgive me brother, kayimin dukkan hukuncin da kaga ya dace da ni." Ya dago jikinsa yana dubansa da idanunsa wadanda suke nuni da gaskiyar abinda ya ke fad'a. 
  "Amma kada ka hukuntani ta hanyar dauke fara'arka daga gareni da kuma fita harkata."
  Jikin Ridwan ya yi sanyi, daman dauriya kawai ya ke yi don tun bayan barinsa gidan Daddy, ya ji babu dadi, yasan kaninnasu mai son farincikinsu ne, ta ya ya shi ya kasa kar6ar abinda yazo musu da shi da hannu bibbiyu ko don faranta ransa?
  Ya dafa kafadarsa.
"Kamin laifi Lil, saidai na yi maka uzuri tunda baka ta6a yimin makamancinsa ba. Karka damu ya wuce."
  Ran Faruk ya yi sanyi, tare suka jera suna tafiya, Ridwan na k'ara nunamishi dalilin da yasa ya nuna rashin goyon bayansa.
"Gani nake kamar ka wuce ajin yarinyar ne, na kuma yi tunanin kodai wani asirin ta yi maka? Amman ka yo hakuri."
Faruk ya yi murmushi.
"Babu abinda ta yimin, ka manta muna dagewa awajen adduar neman tsari? Duk da dai akwai kaddara, amma bama fatanta. Wannan kauna ce daga Allah nake jinta game da ita."
Suka dubi juna sukayi dariya, ya bugi kafadarsa.
"Lil ne da soyayya? Kamar ranar nan ba zata zo ba."
  Faruk ya shafi sumarsa yana shagwa6e fuska. Hanashi wucewa ya yi suka nufi gidan Ridwan din da niyyar zuwa yamma su wuce gidan gaba daya. Ta (whatsapp) ya sanarwa da Haidar cewar sun shirya. Ya aikomishi da rawa na mace har abin ya sanyashi dariya.
  Jidda ganinsu yasa ta hau cakar Faruk akan batun Ummi, shi kuma ya ce ta yi ta gama aure ne babu fashi sai idan Allah baiyiba. Shi kam Dakta na jinsu saidai baisa baki ba, saida ya kula da Jiddar na neman korar mishi k'ani yasa shi tsawatarmata dole ta saki hirar ta yi shigewarta daki da alama dai 'yar bayan Ihsan ce.
Chapter 59 · 0% Book details