Sashe 78
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Mutanen wajen suka yi sak, Ummi a guje ta fito daga gidansu kanta babu ko kallabi ta zubawa Saude ido jin abinda ta fad'a. Habiba fitsari ta soma saki a wando don kuwa bata ta6a tsammanin akwai ranar da Saude za ta yi mata haka ba!
Gaba daya waje ya dauki salati. Wuf Habiba ta fito bayan ta ture hannun Malam Yahuza wanda ya tokare kada Saude ta shigar mishi gida.
"K'arya ta ke yi! Ta haukace! Kada ku yarda karya ta ke min!!"
Saude wacce bata bar kyakyata dariya ba ta ce.
"Ina rantsuwa da Allah ita ta kasheta amman da sa hannuna!"
Ta karashe tana soshe-soshen jiki don haka kawai ta soma jin wani k'aik'ayi a fatar jikinta. Kafin wani ya yi yunkurin karasawa gareta Ummi cikin zafin nama ta k'arasa, ta rik'e kafadunta tana kuka cikin daga murya ta ce.
"Ki gayamin, dagaske kune ku ka kashe Ummana?"
Dariyar dai ta ke yi itama cikin kwaikwayon daga murya ta Ummi ta amsa.
"Eh! Ni da Habiba muka kasheta! Kema na so a kasheki saidai Habiba ta bada shawara a kyaleki nan gaba jari za ki zamarmana! Kuma kin zama." Ta karashe cikin dariya. Sai kuma tiryan-tiryan ta shiga bada labarin yanda komai ya faru.
Ummi batasan sadda ta fidda hannu a zafafe ta dauketa da mari hagu da dama ba, tana yi tana kuka da fadin.
"Ban yafemiki ba Saude(ta fada gatsal don girman ya fadi)! Ban yafemiki ba!!" Sai kuma ta durkushe tana kuka sosai, nan aka ankara Habiba ta gudu. Ai kuwa wasu matasa suka rufamata baya.
Ita kuwa Saude wacce bata ji marin Ummi ba asalima dariya kawai ta ke yi, ta karasa ga Malam Balarabe wanda ke kuka har da sheshsheka saidai ya kasa samun karfin zuwa ya rarrashi Ummi sai wasu matan makwafta ne suka zo suka dagata.
"Abdullahi kai mutumin kirki ne, ka so ni sosai, saidai ni tun daga ranar da ka yimin kishiya na tsaneka."
Ta cigaba da dariya sannan ta dora.
"Habiba kawata ta ban shawarar 6oye kishina kuma na bi, babu irin maganin da ban barbada muku ba a abinci kai da ita, sai kuma duk da haka ka fifita ta a kaina!"
Ta karashe ciki daga murya a fusace sannan ta dara.
"Kuma ta zo ta samu ciki." Fadin haka yasa Saude soma kuka duk mutane na kallonta cike da takaici har lokacin wadanda suka bi bayan Habiba basu dawo ba, Malam Balarabe da ya rasa ta cewa tagumi kawai ya yi yana hawaye yana dubanta, can kuma ta dora tana soshe-soshenta.
"Na sha gwada kashe Hasiya da dan cikinta ta hanyar duramata magunguna ina fakewa da fadin na gargajiya ne na kara lafiya, saidai banga wata illa da ya yi mata ba har zuwa sadda cikinta ya shiga wata tara ta soma nakuda muka kasheta muka bar jaririyar. A karshe na asirceka ka daina kaunarta, na saka dangin uwarta da danginka suka daina zuwa inda ku ke, amma Abdullahi duk wannan kaunar da na nunamaka bai hana ka sakeni ba?!!!"
Ta karashe tana mai dibar k'asa ta watsamishi ya rufe fuskarsa. Nan kuma ta hau tsalle da soshe-soshe, baiyi wata-wata ba ya soma yunkurin dukanta dattijan suka hana. Malam Sule makwafcinsa ya ce. "Ai dukanta yanzu kuma 6ata lokaci ne Malam Balarabe, ba ka ganin ma bata cikin hayyacinta?"
Malam Balarabe kawai sai ya juya ya shiga gidansa yana kuka, Ummi ta bi bayansa da sauri itama.
Habiba cikin sa'a aka cafkota, ana zuwa Malam Yahuza ya tsinke igiyar aurensa da ita, nan ta hau kuka da neman gafara, Malam Balarabe ya fito aka hada kansu sai ofishin yan sanda. Habiba da kanta ta yi bayani don Saude hauka ta ke yi tuburan tana faman kyakyata dariya.
Aka gark'amesu da zummar sai washegari a k'arasa maganar.
Ummi da mahaifinta wannan ranar kasa bacci suka yi ga ciwon kai mai tsanani da Malam Balarabe ya kwana da shi, ita kanta Ummin da shi ta kwana sakamakon kuka da ta sha. Nafila kuwa a wannan daren ta yi shi hakanan addu'o'i. Babu wanda cikinsu ya ta6a kawo hakan, kowannensu tunaninsa bai wuce mutuwa Hasiya ta yi ba kawai ashe azzaluman ne suka kasheta.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
Gaba daya waje ya dauki salati. Wuf Habiba ta fito bayan ta ture hannun Malam Yahuza wanda ya tokare kada Saude ta shigar mishi gida.
"K'arya ta ke yi! Ta haukace! Kada ku yarda karya ta ke min!!"
Saude wacce bata bar kyakyata dariya ba ta ce.
"Ina rantsuwa da Allah ita ta kasheta amman da sa hannuna!"
Ta karashe tana soshe-soshen jiki don haka kawai ta soma jin wani k'aik'ayi a fatar jikinta. Kafin wani ya yi yunkurin karasawa gareta Ummi cikin zafin nama ta k'arasa, ta rik'e kafadunta tana kuka cikin daga murya ta ce.
"Ki gayamin, dagaske kune ku ka kashe Ummana?"
Dariyar dai ta ke yi itama cikin kwaikwayon daga murya ta Ummi ta amsa.
"Eh! Ni da Habiba muka kasheta! Kema na so a kasheki saidai Habiba ta bada shawara a kyaleki nan gaba jari za ki zamarmana! Kuma kin zama." Ta karashe cikin dariya. Sai kuma tiryan-tiryan ta shiga bada labarin yanda komai ya faru.
Ummi batasan sadda ta fidda hannu a zafafe ta dauketa da mari hagu da dama ba, tana yi tana kuka da fadin.
"Ban yafemiki ba Saude(ta fada gatsal don girman ya fadi)! Ban yafemiki ba!!" Sai kuma ta durkushe tana kuka sosai, nan aka ankara Habiba ta gudu. Ai kuwa wasu matasa suka rufamata baya.
Ita kuwa Saude wacce bata ji marin Ummi ba asalima dariya kawai ta ke yi, ta karasa ga Malam Balarabe wanda ke kuka har da sheshsheka saidai ya kasa samun karfin zuwa ya rarrashi Ummi sai wasu matan makwafta ne suka zo suka dagata.
"Abdullahi kai mutumin kirki ne, ka so ni sosai, saidai ni tun daga ranar da ka yimin kishiya na tsaneka."
Ta cigaba da dariya sannan ta dora.
"Habiba kawata ta ban shawarar 6oye kishina kuma na bi, babu irin maganin da ban barbada muku ba a abinci kai da ita, sai kuma duk da haka ka fifita ta a kaina!"
Ta karashe ciki daga murya a fusace sannan ta dara.
"Kuma ta zo ta samu ciki." Fadin haka yasa Saude soma kuka duk mutane na kallonta cike da takaici har lokacin wadanda suka bi bayan Habiba basu dawo ba, Malam Balarabe da ya rasa ta cewa tagumi kawai ya yi yana hawaye yana dubanta, can kuma ta dora tana soshe-soshenta.
"Na sha gwada kashe Hasiya da dan cikinta ta hanyar duramata magunguna ina fakewa da fadin na gargajiya ne na kara lafiya, saidai banga wata illa da ya yi mata ba har zuwa sadda cikinta ya shiga wata tara ta soma nakuda muka kasheta muka bar jaririyar. A karshe na asirceka ka daina kaunarta, na saka dangin uwarta da danginka suka daina zuwa inda ku ke, amma Abdullahi duk wannan kaunar da na nunamaka bai hana ka sakeni ba?!!!"
Ta karashe tana mai dibar k'asa ta watsamishi ya rufe fuskarsa. Nan kuma ta hau tsalle da soshe-soshe, baiyi wata-wata ba ya soma yunkurin dukanta dattijan suka hana. Malam Sule makwafcinsa ya ce. "Ai dukanta yanzu kuma 6ata lokaci ne Malam Balarabe, ba ka ganin ma bata cikin hayyacinta?"
Malam Balarabe kawai sai ya juya ya shiga gidansa yana kuka, Ummi ta bi bayansa da sauri itama.
Habiba cikin sa'a aka cafkota, ana zuwa Malam Yahuza ya tsinke igiyar aurensa da ita, nan ta hau kuka da neman gafara, Malam Balarabe ya fito aka hada kansu sai ofishin yan sanda. Habiba da kanta ta yi bayani don Saude hauka ta ke yi tuburan tana faman kyakyata dariya.
Aka gark'amesu da zummar sai washegari a k'arasa maganar.
Ummi da mahaifinta wannan ranar kasa bacci suka yi ga ciwon kai mai tsanani da Malam Balarabe ya kwana da shi, ita kanta Ummin da shi ta kwana sakamakon kuka da ta sha. Nafila kuwa a wannan daren ta yi shi hakanan addu'o'i. Babu wanda cikinsu ya ta6a kawo hakan, kowannensu tunaninsa bai wuce mutuwa Hasiya ta yi ba kawai ashe azzaluman ne suka kasheta.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR