Sashe 18
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Haidar ya dubeshi yana mai kai bakinsa saitin kunnensa.
"Tsaya muyi hoto mana."
Yana murmushi yayi kokarin zillewa, abin saima ya bawa Haidar domin kuwa yafi kowa sanin Faruk bai fiyeson hoto ba. Ya dank'eshi, a hakan ma sunsha hotuna wajen jama'a masu wayoyi, dakyar ya tsaya yana duban Haidar fuskarsa dauke da wani hadadden murmushi, a haka aka daukesu.
Cikin masu daukar hoton, har da Iklima wacce gaba daya ta gama narkewa cikin so da kaunar Faruk wanda ya gama tafiya da ruhinta. Bata bi ta kan Hassana ba ta mara mishi baya da sauri tun baikai ga k'arasawa wajen yan uwansa ba wadanda su yake yiwa kallon abokai domin Faruk ba shi da babban amini ke6antacce da za'a kira nasa akoyaushe. Bazai rasa abokan ba, duk wata shawara acewarsa yayyunsa sun isheshi.
"Ina wuni Yaya Faruk." Muryar da ya tsinkaya kenan daga gefensa. Ya kai dubansa gareta, take kuma sai ya tsuke fuska tamkar ba shine ke murmushi ba yanzun. Kansa kawai ya gyada sannan yayi gaba. Da sauri ta juya itama tun baikai ga bata kunya ba. Tun kafin ta kai ga Hassana, take watsa mata harara har ta dangana da mazauninta. Alokacin ne ta samu damar yi mata magana.
"Ai ga irinta, saida nace kada kije amma kika k'i saurarona, yanzun da ya jefeki da kallon banza ai kinji dadi."
Tana maganar a fusace. Iklima idanunta akan Faruk wanda ke hira abinsa hankali kwance, ta murmusa.
"Yasan ya had'u ne shiyasa yake shan kamshi ga yanmata. Wallahi ina sonsa fa."
Hassana ta ta6e baki. "Shi kuma baisan da zamanki ba."
Sai alokacin ta dubeta tana harara.
"Wai me kikeson ki cemin? Kin manta alak'armu da shi ne?"
"Naga Ihsan ma k'arewar alak'a da shi ai." Hassana ta fada gami da jan dogon tsaki sannan ta cigaba da maganarta.
"Shi namiji idan yaga kin fiye zakemishi rainaki zaiyi wallahi, ki kula dakyau leema, kisan dai dabarar da zakiyi ki shawo kansa, amma idan har zaki cigaba da yi mishi irin wannan shishshigin agaban jama'a, toh fa zaki raina kanki."
Iklima tayi shiru tana sauraronta, ga dukkan alamu dai maganganun Hassana yana shigarta. Tayi na'am da shawararta na cewa ta dinga yi mishi ladabi a fili da kuma online.(chatting), a sannu idan suka saba sai tayi kokarin shawo kansa.
Haka aka tashi taron kowa cike da farinciki idan an cire Iklima wacce bataji dadi ko kadan ba na yanda Faruk ya gwatsaleta ba.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
25
Koda su Mami suka koma gida, ta tuntu6i Ummi akan dalilinta na barin wajen (party), bata 6oyemata yanda sukayi da Ihsan ba, da kukan da Faruk ya ga tana yi ya taimaka ya kawota gida. A take Mami ta nemi Ihsan a waya amma fir ta karyata tace batasan ma da zaman wata Ummi awajen ba. Ranar duka ne kawai Ummi bata ci ba, amman ta sha fad'an Mami sosai, acewarta bazata lamunci a dinga yiwa yaranta karya ba akan abinda bai zama halinsu ba.
Haka Ummi tana ji tana gani aka k'aryatata aka bata laifi, dole ta bawa Mami hakuri sannan ta bi umarninta ta chanjawa Fahad kayan bacci ta nemi makwancinta. Bacci gaba daya gagararta yayi don ta kasa tsaida hawayenta, sai wajen asuba ta samu ya dauketa.
Washegari suka shirya tafiya Abuja kai amarya. Da yawansu ta mota zasu tafi, ciki harda Mami. Hakan yasa da sassafe ta kammala komai, kasancewar kwana daya zasuyi ta amince Ummi ta zauna agidan tare da su Adnan. Ta mascara mata cewa ta rik'e amanarta. Daga haka sukayi sallama, ita da Ramma na binsu da adduar sauka lafiya.
Misalin karfe biyar na yamma, babu kowa a sashen Mami sai Ummi dake kwance a tsakar gida. Fahad da Adnan sun fice yawo, Ihsan kuwa har lokacin bata dawo ba, da alama da ita aka nufi Abuja, Ramma kuwa daman tun tafiyar Mami tana kammala ayyukanta ta bar gidan.
Muryar da ta ji tayi sallama ne yasa babu shiri ta mike zaune a matukar razane. 'Hajiya Binta?' Ta fad'a a ranta cike da mamaki. To mene ya kawota sashen Mami alhalin a baya ba shigowa takeyi ba?
Fuskar Hajiya Binta a sake ta k'arasa shigowa ciki tana d'an waige-waige.
"A'a Ummi, ba kowa ne sai ke kadai?"
Ummi ta russuna cikin ladabi ta amsa mata.
"Eh Hajiya. Ina wuni."
Hajiya ta zauna a saman wata kujerar roba cikin karamar murya kamar mai rad'a ta amsa.
"Lafiya lau Ummin Hajiya. Sai kyau kike k'arawa Masha Allah."
Murmushi ta dan yi mai kama da yak'e domin ba wani sabo tayi da ita ba, banda munanan kalamai da take watsamata aduk haduwarsu, babu abinda ke shiga tsakaninsu. Maganar Hajiya Binta wacce ta k'ara matsowa dab da ita ya katse tunaninta.
"Ummi ina neman wata alfarma daga gareki, matuk'ar kika amince kika yi yanda na sanyaki, toh ina miki rantsuwa da Allah zakiji dadin rayuwarki. Ina tabbatar miki sai kin samu 'yanci agidannan kamar kowace 'ya matukar kikayi yanda nace."
Ummi ta ji kanta yayi dumm. Ta rasa gane alkiblar da maganganun Hajiya Binta suka dosa. Ta dubeta duba na neman karin bayani. Hajiya Binta ta kara lek'en bayanta, bata ga wani ko wata dake tahowa ba. Ta fiddo wata bak'ar leda daga zaninta ta bud'eshi gami da nunawa Ummi. Ummi ta zaro ido cikin matukar kad'uwa ganin wani abu wanda aka duk'unkule da farin zare mai yawa wanda har ya zamana baka ganin komenene aciki sai zaren da yayi kamar bal.
Ji tayi ta soma gumi cikinta kuwa wani hautsinewa ya yi na ban mamaki.
Hajiya Binta wacce gaba daya ta gama kwadaituwa da samun cikar burinta ta cigaba da magana.
"Wannan kadai zaki ajiye a k'ark'ashin gadon uwardakinki, daga tsakiyar gadon, shikenan kin kammala mini komai. Wallahi Ummi zakiji dadin rayuwa fiye da zatonki. Zaki samu duniya yanda baki ta6a kawowa ba. Za kuma ki jera da yaran gidannan a zuwa makaranta mai tsada, a fannin ci da sha da kuma sutura. Rik'e kiyimin yanda nace."
Ummi na k'ok 'arin magana ta tsaidata ta hanyar damk'a mata abin a hannunta. Ta jefeta da murmushi.
"Zan nemeki gobe." Daga haka ta mik'e sai kuma ta dawo baya. Fuskarta a murtuke ta dubeta, duban da ya k'ara hautsinata.
"Karki soma yunk'urin tonamin asiri, muddin kika soma sai na lahira ya fiki jin dadi. Ki kula." Daga haka ta fice da sauri. A nan kofar shiga ta tarar da aminiyarta ta, Hajiya Luba wacce ke tsayuwar gadi kada wani ya taho ya iskesu. Tana ganinta cikin rad'a tace.
"Angama?" Hajiya Binta tayi dariya.
"Ta isa daman ta k'i?"
Sukayi dariya k'asa-k'asa gami da cafkewa sannan suka bar wajen da sauri.
Ummi ta shiga tsaka mai wuyaaa....!
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
26
Gaba d'aya gigicewa tayi, tayi sauri yarr da kullin a kasa kafin ta cigaba da ambaton Allah a fili. Ita kuwa Hajiya Binta me take nema haka a duniya da har zata iya yiwa wani asiri? Ummi a iyakar tsawon rayuwarta ta tsani mugunta ta tsani mai yinsa.
Ta k'ara kallon kullin cikin zubar hawaye, tunanin kada Adnan ya dawo ya isketa da shi yasa ta mike a gaggauce gami da daukarsa da hannun hagu don kuwa tsoro da kyankyaminsa take. Allah Yayi mata tsari da aikata mummunan aiki irin wannan. Shine addu'ar da take ta nanatawa a ranta. Kai tsaye ta nufi dakinta da shi ta kulle cikin bak'ar leda da zummar washegari idan zata makaranta ta yarr koda acikin kwata ne.
Bayan ta adana shi inda babu mai gani tunda ba mai shigowa dakinta, ta fito ta zauna jigum, gaba daya a tsorace take. Kuka kam ta sha, a karshe dai tayita addua akan Allah Ya ku6utar da ita daga sharrin Hajiya Binta.
Bayan dawowar su Adnan dole ta saki ranta kada su gane. Ya damkamata karamar robar (ice-cream) da suka siyo, suma suka zauna a falon suna kallo suna shan abinsu hankali kwance. Ita dai sha takeyi amma kokusa kallon baya gabanta, koda ta soma jin dadinsa da zarar ta tuna da Hajiya Binta sai jikinta yayi lakwas. Karshe rufe robar (ice cream) din tayi gami da shigewa daki bayan ta nemi zubomusu abinci sun tabbatar mata sun k'oshi. Daman ta ga alama, kawai dai gudun kada ace tayi laifi ya sanya ta tambaya.
A ranar Ummi dai bata runtsa ba, gani takeyi kamar wani abin zai sameta asanadin kullin da ke a dakinnata. Bata ta6a fatan ace tana da wayar hannu ba sai a wannan dare, da babu abinda zai hana ta sanarwa Antinta ko don ta bata shawarar yanda zatayi.
"Tsaya muyi hoto mana."
Yana murmushi yayi kokarin zillewa, abin saima ya bawa Haidar domin kuwa yafi kowa sanin Faruk bai fiyeson hoto ba. Ya dank'eshi, a hakan ma sunsha hotuna wajen jama'a masu wayoyi, dakyar ya tsaya yana duban Haidar fuskarsa dauke da wani hadadden murmushi, a haka aka daukesu.
Cikin masu daukar hoton, har da Iklima wacce gaba daya ta gama narkewa cikin so da kaunar Faruk wanda ya gama tafiya da ruhinta. Bata bi ta kan Hassana ba ta mara mishi baya da sauri tun baikai ga k'arasawa wajen yan uwansa ba wadanda su yake yiwa kallon abokai domin Faruk ba shi da babban amini ke6antacce da za'a kira nasa akoyaushe. Bazai rasa abokan ba, duk wata shawara acewarsa yayyunsa sun isheshi.
"Ina wuni Yaya Faruk." Muryar da ya tsinkaya kenan daga gefensa. Ya kai dubansa gareta, take kuma sai ya tsuke fuska tamkar ba shine ke murmushi ba yanzun. Kansa kawai ya gyada sannan yayi gaba. Da sauri ta juya itama tun baikai ga bata kunya ba. Tun kafin ta kai ga Hassana, take watsa mata harara har ta dangana da mazauninta. Alokacin ne ta samu damar yi mata magana.
"Ai ga irinta, saida nace kada kije amma kika k'i saurarona, yanzun da ya jefeki da kallon banza ai kinji dadi."
Tana maganar a fusace. Iklima idanunta akan Faruk wanda ke hira abinsa hankali kwance, ta murmusa.
"Yasan ya had'u ne shiyasa yake shan kamshi ga yanmata. Wallahi ina sonsa fa."
Hassana ta ta6e baki. "Shi kuma baisan da zamanki ba."
Sai alokacin ta dubeta tana harara.
"Wai me kikeson ki cemin? Kin manta alak'armu da shi ne?"
"Naga Ihsan ma k'arewar alak'a da shi ai." Hassana ta fada gami da jan dogon tsaki sannan ta cigaba da maganarta.
"Shi namiji idan yaga kin fiye zakemishi rainaki zaiyi wallahi, ki kula dakyau leema, kisan dai dabarar da zakiyi ki shawo kansa, amma idan har zaki cigaba da yi mishi irin wannan shishshigin agaban jama'a, toh fa zaki raina kanki."
Iklima tayi shiru tana sauraronta, ga dukkan alamu dai maganganun Hassana yana shigarta. Tayi na'am da shawararta na cewa ta dinga yi mishi ladabi a fili da kuma online.(chatting), a sannu idan suka saba sai tayi kokarin shawo kansa.
Haka aka tashi taron kowa cike da farinciki idan an cire Iklima wacce bataji dadi ko kadan ba na yanda Faruk ya gwatsaleta ba.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
25
Koda su Mami suka koma gida, ta tuntu6i Ummi akan dalilinta na barin wajen (party), bata 6oyemata yanda sukayi da Ihsan ba, da kukan da Faruk ya ga tana yi ya taimaka ya kawota gida. A take Mami ta nemi Ihsan a waya amma fir ta karyata tace batasan ma da zaman wata Ummi awajen ba. Ranar duka ne kawai Ummi bata ci ba, amman ta sha fad'an Mami sosai, acewarta bazata lamunci a dinga yiwa yaranta karya ba akan abinda bai zama halinsu ba.
Haka Ummi tana ji tana gani aka k'aryatata aka bata laifi, dole ta bawa Mami hakuri sannan ta bi umarninta ta chanjawa Fahad kayan bacci ta nemi makwancinta. Bacci gaba daya gagararta yayi don ta kasa tsaida hawayenta, sai wajen asuba ta samu ya dauketa.
Washegari suka shirya tafiya Abuja kai amarya. Da yawansu ta mota zasu tafi, ciki harda Mami. Hakan yasa da sassafe ta kammala komai, kasancewar kwana daya zasuyi ta amince Ummi ta zauna agidan tare da su Adnan. Ta mascara mata cewa ta rik'e amanarta. Daga haka sukayi sallama, ita da Ramma na binsu da adduar sauka lafiya.
Misalin karfe biyar na yamma, babu kowa a sashen Mami sai Ummi dake kwance a tsakar gida. Fahad da Adnan sun fice yawo, Ihsan kuwa har lokacin bata dawo ba, da alama da ita aka nufi Abuja, Ramma kuwa daman tun tafiyar Mami tana kammala ayyukanta ta bar gidan.
Muryar da ta ji tayi sallama ne yasa babu shiri ta mike zaune a matukar razane. 'Hajiya Binta?' Ta fad'a a ranta cike da mamaki. To mene ya kawota sashen Mami alhalin a baya ba shigowa takeyi ba?
Fuskar Hajiya Binta a sake ta k'arasa shigowa ciki tana d'an waige-waige.
"A'a Ummi, ba kowa ne sai ke kadai?"
Ummi ta russuna cikin ladabi ta amsa mata.
"Eh Hajiya. Ina wuni."
Hajiya ta zauna a saman wata kujerar roba cikin karamar murya kamar mai rad'a ta amsa.
"Lafiya lau Ummin Hajiya. Sai kyau kike k'arawa Masha Allah."
Murmushi ta dan yi mai kama da yak'e domin ba wani sabo tayi da ita ba, banda munanan kalamai da take watsamata aduk haduwarsu, babu abinda ke shiga tsakaninsu. Maganar Hajiya Binta wacce ta k'ara matsowa dab da ita ya katse tunaninta.
"Ummi ina neman wata alfarma daga gareki, matuk'ar kika amince kika yi yanda na sanyaki, toh ina miki rantsuwa da Allah zakiji dadin rayuwarki. Ina tabbatar miki sai kin samu 'yanci agidannan kamar kowace 'ya matukar kikayi yanda nace."
Ummi ta ji kanta yayi dumm. Ta rasa gane alkiblar da maganganun Hajiya Binta suka dosa. Ta dubeta duba na neman karin bayani. Hajiya Binta ta kara lek'en bayanta, bata ga wani ko wata dake tahowa ba. Ta fiddo wata bak'ar leda daga zaninta ta bud'eshi gami da nunawa Ummi. Ummi ta zaro ido cikin matukar kad'uwa ganin wani abu wanda aka duk'unkule da farin zare mai yawa wanda har ya zamana baka ganin komenene aciki sai zaren da yayi kamar bal.
Ji tayi ta soma gumi cikinta kuwa wani hautsinewa ya yi na ban mamaki.
Hajiya Binta wacce gaba daya ta gama kwadaituwa da samun cikar burinta ta cigaba da magana.
"Wannan kadai zaki ajiye a k'ark'ashin gadon uwardakinki, daga tsakiyar gadon, shikenan kin kammala mini komai. Wallahi Ummi zakiji dadin rayuwa fiye da zatonki. Zaki samu duniya yanda baki ta6a kawowa ba. Za kuma ki jera da yaran gidannan a zuwa makaranta mai tsada, a fannin ci da sha da kuma sutura. Rik'e kiyimin yanda nace."
Ummi na k'ok 'arin magana ta tsaidata ta hanyar damk'a mata abin a hannunta. Ta jefeta da murmushi.
"Zan nemeki gobe." Daga haka ta mik'e sai kuma ta dawo baya. Fuskarta a murtuke ta dubeta, duban da ya k'ara hautsinata.
"Karki soma yunk'urin tonamin asiri, muddin kika soma sai na lahira ya fiki jin dadi. Ki kula." Daga haka ta fice da sauri. A nan kofar shiga ta tarar da aminiyarta ta, Hajiya Luba wacce ke tsayuwar gadi kada wani ya taho ya iskesu. Tana ganinta cikin rad'a tace.
"Angama?" Hajiya Binta tayi dariya.
"Ta isa daman ta k'i?"
Sukayi dariya k'asa-k'asa gami da cafkewa sannan suka bar wajen da sauri.
Ummi ta shiga tsaka mai wuyaaa....!
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
26
Gaba d'aya gigicewa tayi, tayi sauri yarr da kullin a kasa kafin ta cigaba da ambaton Allah a fili. Ita kuwa Hajiya Binta me take nema haka a duniya da har zata iya yiwa wani asiri? Ummi a iyakar tsawon rayuwarta ta tsani mugunta ta tsani mai yinsa.
Ta k'ara kallon kullin cikin zubar hawaye, tunanin kada Adnan ya dawo ya isketa da shi yasa ta mike a gaggauce gami da daukarsa da hannun hagu don kuwa tsoro da kyankyaminsa take. Allah Yayi mata tsari da aikata mummunan aiki irin wannan. Shine addu'ar da take ta nanatawa a ranta. Kai tsaye ta nufi dakinta da shi ta kulle cikin bak'ar leda da zummar washegari idan zata makaranta ta yarr koda acikin kwata ne.
Bayan ta adana shi inda babu mai gani tunda ba mai shigowa dakinta, ta fito ta zauna jigum, gaba daya a tsorace take. Kuka kam ta sha, a karshe dai tayita addua akan Allah Ya ku6utar da ita daga sharrin Hajiya Binta.
Bayan dawowar su Adnan dole ta saki ranta kada su gane. Ya damkamata karamar robar (ice-cream) da suka siyo, suma suka zauna a falon suna kallo suna shan abinsu hankali kwance. Ita dai sha takeyi amma kokusa kallon baya gabanta, koda ta soma jin dadinsa da zarar ta tuna da Hajiya Binta sai jikinta yayi lakwas. Karshe rufe robar (ice cream) din tayi gami da shigewa daki bayan ta nemi zubomusu abinci sun tabbatar mata sun k'oshi. Daman ta ga alama, kawai dai gudun kada ace tayi laifi ya sanya ta tambaya.
A ranar Ummi dai bata runtsa ba, gani takeyi kamar wani abin zai sameta asanadin kullin da ke a dakinnata. Bata ta6a fatan ace tana da wayar hannu ba sai a wannan dare, da babu abinda zai hana ta sanarwa Antinta ko don ta bata shawarar yanda zatayi.