← Book details Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 116

Sashe 52

Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

69Ya bud'e dakinta, saidai Binta ya gani wacce ke yawo a
tsakar dakin tana jiran dawowarta, ganin Yalla6ai da kansa
yasa ta russunawa ta gaisheshi, batare da ya amsa ba ya
jefomata tambaya.
"Ina Ummi?"
Ta girgiza kai.
"Bata shigo ba tun bayan fitarta."
Ya juya kai tsaye wajen garden ya nufa, acan kuwa ya
ganota durkushe k'asan bishiyar mangwaro tana faman kuka
sosai. A gigice ya isa gareta ya durkusa kusa da ita. Jin
motsi ne yasa ta dago kanta da sauri, ganin shine yasa ta
numfasawa.
"Kaga abinda muka janyo ko? Ni nasan wannan lamari ba mai
yiwuwa bane."
Baisan sadda ya rik'o hannunta ba.
"Wa ya gayamaki bazai yiwu ba? Kada ki damu da abinda ya
faru domin na zo miki da kyakkyawan albishir, iyayena sun
amince da aurenmu."
Ta yi sakato tana kallonsa, babu alamun wasa ya ke yi,
ganin ta yi shiru ya girgiza hannunta.
"Ba mafarki ki ke ba fa Ummi, dagaske sun amince da
zancen aurenmu. Godiya ya kamata muyi ga Ubangiji."
Ta lumshe ido, ta rasa irin yanayin da ta ke ji a jikinta, ji ta
yi yana kokarin mik'ar da ita, a kunyace ta zare hannunta
daga nasa ta mik'e, jerawa sukayi suka soma tafiya tamkar
basu so, kallo daya idan kayi musu, zaka so kayita kallonsu
tsabar dacewa da sukayi da juna. Ya dubeta.
"Ummina shiru fa, kiyi magana please."
Ta share ruwan hawayen da suka k'i tsayuwa.
"Yaya Faruk."
Ya tsaya a gefen kujera mai lilo ya zauna, sannan ya yi mata
nuni da gefensa.
"Zauna nan."
Ba musu ta zauna jikinta a sanyaye. Ya juyo yana
fuskantarta yana ji tamkar ya had'iyeta don so da tsantsar
kauna.
"Ina sauraronki." Ya fada cikin kankan da murya tamkar
wanda baya son magana.
"Kamar fa 'yan uwanka ba..."
"Shiii.." Yasa yatsa a saman le66anta, ta kauda kai tana mai
takaicin yanda bayason ta kawomishi zancen abinda ya
kasance gaskiya kuma shima ya sani.
"Ya dace ka bani dama ka ji abinda zan fada Yaya Faruk,
akwai babbar matsala da kai ka ke mata kallon sassauk'a.
Yaya Faruk kana da labarin Ihsan na sonka?"
Ta karashe tana kallonsa, shima ita ya ke kallo, kenan dai
shi 6oyon ma da ya ke mata ta sani? Abu daya ne bazai iya
sanarmata ba, batun auren da Hajiya ta ce zaiyi da Ihsan don
bai dauki hakan mai yiwuwa ba, kuma ba wai don Hajiyartasa
bata isa ba, aa, sai don kokusa ba shi da tsarin had'a mata
biyu a gidansa. Saidai abinda ya ba shi mamaki, bai wuce ta
yacce akayi tasan da cewa Ihsan na kaunarsa ba.
Ya kauda fuskarsa yana mai dan hade gira.
"Ya akayi kika sani?"
Ta yi murmushi mai ciwo itama ta maida dubanta ga wata
shuka a wajen.
"Shi so ba'a 6oyonsa, itama nata ya fito fili, k'alilan ne
basu san tana sonka ba a gidan..."
"Kinga ya isa haka please, ya isa. Ke bakya kishina ne?
Bakya jin wani abu a ranki idan kina had'ani da wata bayan
ke? Bazan iya rayuwa da kowace mace ba bayan ke. Ummi
wai kinsan waye Umar Faruk kuwa?"
Ya k'arashe yana mai tsuramata ido da wani murmushi.
Daman ba kallonshi ta ke yi ba, wasa kawai ta ke yi da
yatsunta. Ya girgiza kai.
"Shikenan dai. Ban labari game da farin cikin da zaki yi
ranar da aka shafa fatiha?"
Maganar ma sai ta bata dariya, ta rufe fuskarta tana
murmusawa.
Karaf akan idanun Ihsan wacce ta fito don bawa wani mai
wankin gidan ya siyo mata kati don kiran Maminta, ta jima
tsaye tana kallonsu basu sani ba, hawaye kawai ke zuba daga
idanunta. Ta k'arewa Ummi kallo, ta yi wani kyau a suturar
dake jikinta, sannan ta dubi Faruk wanda ya bawa inda ta ke
baya, ya wani duk'ar da kai a gaban Ummi yana lek'en
fuskarta kamar mai shirin kai mata sumba. Nan duniya ta ji
ta k'ara tsanar Ummi, ta k'ara tsanar Faruk da wai suke
takara a sonsa da ita. Ina ita ina had'a masoyi da wacce
tasan ta fi? Faruk ya cuceta, inama bai soma son Ummi ba
ita ya so? Katin da bata bada an siyomata kenan ba, da gudu
ta koam ciki tana rusa kuka, a kicin ta yada zango ta yi mai
isarta sannan ta fito ta fada bandakin dake falon ta wanke
fuskarta ta koma sama zuciyarta na wani irin zafi.
Daddy ya cigaba da yiwa Hajiya nasiha mai ratsa jiki gami
da nunamata shi fa lamari na aure ba'a dole, ya amince da
bukatarta na aurawa Faruk duk su biyun saidai su dage da
mik'a lamarin ga Allah kafin komai, a karshe ya ce su bar
maganar nan zuwa kwanaki uku. Hajiya ta aminta da hakan,
ta kuma sanarmishi cewar a gobe Ummi zata koma Kano.
"Badai don maganarnan ba?"
Ta girgiza kai tana dan murmushi duk don ta kwantarwa da
mijinya hankali.
"Ko kusa, saidai Madina ta buk'aci hakan tun ba yau ba,
daman ina shirin sanarmaka sai wannan al'amari ya 6ullo."
Ya jinjina kai alamun gamsuwa.
"Shikenan ai, Allah Ya nunamana. Shima Ridwan zan ganshi
gobe, banason abinda zai kawo rikici tsakaninsu."
"Hakane." Hajiya ta amsa kafin ta mike don kawomishi
ruwan lipton wanda ya saba sha duk dare.
*** *** ***
RINGIM
Abu kamar wasa, k'aramar magana ta zama babba, don kuwa
tuni Deen ya damk'awa Dija mak'udan kudi ta had'o
lefenta. Tare da Saude da Baba Habiba suka shigo kasuwar
Kano, nan suka shek'o kayayyaki masu dan karen kyau da
tsada don har saida Deen ya k'aramusu kud'i. Yan uwa
daidaiku ne kawai suka halarci ganin lefen don kuwa
acewarsu abin kunya ne da abin tirr irin wannan cin amana da
suka yi ga Munira. Kuma tabbas Allah bazai barsu ba, to ance
wanda ya yi nisa ba ya jin kira, ko a jikinsu wai an tsikari
kakkausa, Malam Yahuza abin na damunsa a kasan zuciya
saidai babu abinda zai iya cewa, haka zai zauna tare da
Balarabe mahaifi ga Ummi ya yi ta gayamishi bayason
auren, shima kasancewar ba wani kata6us ne da shi a gidansa
ba, saidai ya ce "To ya zaayi banda hakuri da addua? Matar
mutum babu makawa sai ya aureta indai Allah Ya kaddaro
tasa din ce." Haka suna gani matansu suka shiga shirye-
shirye, an kai Dija wajen bokanya yafi sau biyar ana mata
tsafe-tsafe don ta mallaki zuciyar Deen. Aikam sai
haukacewa ya ke k'ara yi akanta, Munira dai yanzu abin ma
ya ca6emata don hatta Yaransu ba shiga harkarsu ya ke ba,
idan ka gansu kasan suna cikin tashin hankali marar
misaltuwa.
Har ana washegari Asabar daurin aure, Deen bai samu
wata fuska daga yan uwansa ba, Munira kuwa a ranar ta
juma'a ta iso Ringim din suna k'ara jajanta lamarin da yan
uwanta, iyayenta kuwa nasiha kawai sukai ta binta da shi
akan ta yi hakuri ta rungumi kaddara.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
Chapter 52 · 0% Book details