Sashe 2
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yaha ta rik'e k'ugu tana taunar cingam ta dubi Ummi. Ganin haka yasa Ummi kauda nata idanun cikin sauri.
"Don ubanki saura kiyi min halin kauyenci sai na shak'e ki kin mutu har lahira. Banason yawan kalle-kalle. Kiyi ladabi so..."
Sauran maganar ya mak'ale a fatar bakinta ganin an soma k'ok'arin bud'e k'ofar.
Maigadin ya d'an lek'o da kansa. Farin buzu ne. Ganin Yaha ya sanyashi sakin fuska.
"A'a mai yara, kaine?"
Hakanan yake kiranta. Tayi dariya.
"Ni ce dai Baba. Hajiyar na ciki ko?"
Ya bata hanya ta shigo yana amsa mata.
"Eh yana nan. Ina ka samo d'an garinmu?"
Ya fad'a yana duban Ummi wacce ta durkusa da rawar jiki ta gaisheshi.
Yaha ta dubeta tayi mata alamun ta mik'e.
"Wannan ba 'yar garinku bace. 'Yar Maiduguri ce."
"Anya? Yana kama da mu." Yaha dariya kawai ta d'anyi batace uffan ba.
Daga haka sukayi ciki.
Ummi na bin farfajiyar da kallo a sace don bataso Yaha ta kamata tana kallon bayan ta ja mata kunne. Babban gida ne sosai, an k'awatashi da shuke-shuke. Daga wajen ka rantse ba shi da wani kyau ko girma don kuwa ko fenti ba'ayi ba daga wajen.
Haka suka isa har bakin wata k'ofa. Yaha ta murd'a ta shiga. Suka cigaba da tafiya a doguwar barandar dake wajen har suka iso tsakar gidan. Acan bakin rariya, wata babbar mace dattijuwa ce ke zaune saman kujera irin ta tsakar gida tana wanke-wanke. Ganin Yaha ta washe baki.
"A'a, lale marhabin da Hajiya Yaha. Yau kuma zuwan rana ce?"
Yaha ta numfasa fuskarta na nuna gajiya.
"Bari kawai Ramma, duk a gajiye nake. Hajiyar na ciki mu k'arasa?"
Ramma fuska a sake ta amsa tana duban Ummi wacce ke takure jikin bango.
"Eh tana ciki." Ummi da sauri ta gaisheta. Ramma ta amsa. Har suka kama hanya Ramma na binta da kallo, yarinyar da alamu zasu d'asa da Hajiya Madina, don kuwa da alama nutsastsiya ce
DAN ADAM
@Rufaida Omar
04
"Sannu Ummi."
Muryar Amina ta katsemata tunani, ta dubeta, sukayi murmushi a tare.
"Yauwa."
Amina ta ninke abin sallar ta ajiye a gefe. Zama tayi a gefen katifa kusa da Ummi tana dubanta.
"Daga wane gari kuke?"
"Ringim." Ta amsa a takaice.
"Lallai, baku da nisa sosai."
Ummi zuwa yanzu ta dan saki jiki da Amina ganin irin yanda take janta a jiki. Wannan yasa itama bata ji nauyin tambayarta ba.
"Ke ba anan kusa kike ba?"
Ta gyada kai.
"Anan dai nayi rayuwata, amma mahaifina d'an Maradi ne can cikin jamhuriyar Nijar. Zama da neman abinci ne ya kawoshi Nijeriya sukayi aure da Innata, amma yanzu ya rasu, ya barmu mu hudu yaransa. Ni ce 'ya ta uku a cikinsu."
Ummi ta d'an tallafi kumatunta.
"Kema aiki kike yiwa Hajiya?"
Amina ta murmusa.
"Ni ina yiwa Hajiya Mama aiki ne, kanwar Hajiyarnan ce, abinda yasa kika ganni a gidannan, sunyi tafiya ne da mijinta da yaransu, shine dalilin da yasa na dawo nan da zama kafin su dawo."
Ummi ta jinjina kai cike da gamsuwa. A ranta ta ji babu dad'i, kenan itama wataran zata bar gidan ta barta?
"Ya dai Ummi? Kinyi shiru ina magana."
Ummi a sanyaye ta girgiza kai.
"Bakomai."
Jin haka yasa Amina yin murmushi.
"Shikenan, tashi muje mu tattara falo da kicin kafin Hajiya tayi magana, ki dunga lura da dukkan abinda nakeyi, nasan karshe ke zaki maye gurbina."
Ummi bata ko damu ba, idan ana sabo da aikin wahala, ai yaci kuwa ace ta saba, ina take samun damar yin cikakken awa sadda tana gidan babanta batare da an had'ata da wani nannauyan aikin ba? Gashi anan har gatan da za'a gyara mata kai a bata wajen kwana tsaftatacce da abinci mai kyau ta samu. Ai babu abinda zata ce ga Ubangiji sai godiya.
Haka ta bi bayanta zugui-zugui suka fita. A falon suka iske Adnan da kannensa su biyu, wadanda ta ji Ramma ta ambacesu da Ihsan, Hanifa da Fahad wanda shi ne auta a d'akin nasu.
Adnan hankalinsa kacokam yana kan wayar hannunsa yana faman latse-latse, yayinda Ihsan ta dukufa wajen koyawa kannenta aikin gida da aka basu a makaranta. Shekarun Ihsan goma sha uku a duniya zata shiga na hud'u, sa'ar Ummi ce. Hanifa kuwa, tana da shekaru goma sha biyu bata da tazara tsakaninta da Ihsan, Fahad ne mai shekaru takwas a duniya. Daga kansa kuma, Hajiya Madina bata k'ara haihuwa ba.
Yaranta gaba daya su takwas ne cif, mata uku ne kafin zuwan Adnan duniya, Rahila, Na'ima, Aisha, gaba dayansu ukun suna gidajen aure.
Shigowarsu falon ne yasa su d'ago kai su dubesu. Adnan ya k'urawa Ummi ido fuskarsa a sake sannan ya maida dubansa ga Amina.
"Ummi sunanta ko?"
Amina ta gyada kai tana murmushi wanda ya riga ya zamto jikinta, ko kusa bata rabo da shi.
"Itace." Ummi ta durkusa ta gaisheshi da saurinta sannan ta gaida su Ihsan. Ai kuwa su Ihsan suka tuntsire da dariya. Adnan ya dauki filon kujera yana dariya ya jefi Ihsan da shi.
"(See you), mene abin dariyar? Ai na isa a gaisheni, kune dai daga yau kada ki k'ara gaishesu, na tabbatar kin girme musu." Ya karashe yana maida dubansa ga Ummin.
Ihsan ta jinjina kai.
"Tab, wallahi saidai mu tafa, na tabbatar bazata girmeni ba. Kuma idan ma aka ajiye wannan a gefe ai 'yar aikinmu ce dole ta girmama mu."
Ta karashe tana jifan Ummi da kallon eh sun isa. Ummi dai ta kara sunkuyar da kanta. Amina batace komai ba don kuwa bata fiye shiga harkar Ihsan ba, sanin da tayi mata na cewa ta tsani wasa da duk wani wanda yake karkashinsu. A ganinta, bai kai har a zauna a sakar mishi fuska ba.
Abin yakan bawa Amina mamaki, yarinya tun bata tafasa ba tana neman k'onewa? Ta tabbata nan gaba idan Ihsan tafi haka za'a ga abu.
"Zaki fara ko?" Cewar Adnan lokacin da ya mike tsaye.
Ihsan ta dara a karo na biyu sannan ta dubi su Hanifa.
"Malamai ku maido hankalinku mu cigaba. Nasoma jin bacci wallahi."
Wannan yasa su Hanifa nutsuwa don suna d'an shakkarta kasancewarta itama wani sa'in akwai masifa. Hakanan ta iya kaiwa mutum bugu, kodan ita din tana da jiki kamar kazar gona.
"Muje Ummi."
Sai lokacin Ummi ta mike, Amina daman tana tsaye bata russuna ba. Tasan Ummin itama don yau ta zo ne, amma ita kam tuni an wuce wajen, don wani lokacin bata daukar rainin Ihsan, saidai duk randa ta biyemata suka yi cacar baki ko yaya ne, toh fa tana shan zagi da gori wajen Hajiya Madina. Sam, bata daukar cin mutunci akan yaranta, komin girmanka, muddin ka ta6a mata yara toh fa zatasan yanda tayi ta rama. Idan kuwa daga matan gidan ne, acan fadar maigidan ake k'ulla musu k'ullalliya. Shi kuwa ya hau ya zauna.
Haka Ummi ta taimaka suka kammala gyara komai na kicin sukayi wanke-wanke. Lokacin ana gabatar da sallar isha'i a masallacin unguwa.
A gurguje suka fito suka tattara falon, Ummi na lura da komai, a karshe bayan sun kammala, Amina ta fiddo dukkan abinda tasan zasu bukata wajen cin abinci ta jera bayan ta shimfid'a babbar ledar cin abinci a tsakar falon. Daga nan ta dubi Ummi.
"Jeki kiyi sallah, zan sanarwa Hajiya mun kammala."
"Toh."
Daga haka Amina ta mik'a wani d'an (Corridor) ita kuwa ta nufi dakinsu.
Har ta idar da sallar Amina bata dawo ba, nan kuma ta zauna ta soma gyangyadi don kuwa ba karamin gajiya tayi ba. Ta kwanta saman katifar dake shimfide ta mutum d'aya, wani dadi taji ya ratsata, yayinda iskar fanka ke kad'ata.
"Ashe nima zan kwana saman katifa wataran?"
Ta fad"a a fili. Tana nan kwance ta ji shigowar Amina. Da sauri kuma ta mik'e zaune tana mutsistsika ido.
"Har kin soma bacci wai? Taso mu ci abinci."
Ta mike ta bi bayanta, falon wayam, kadan-kadan ta dunga jiyo sautin dariya da hirarrakinsu daga can cikin da batasan iyaka zurfi da yanayinsa ba.
Amina ta kammala kwashe komai ta wanke na wankewa, tayi mamakin yanda bata nemi tayinta ba. Suka zauna suka ci tuwo da miya sukayi nak, a karshe suka sha ragowar romon kifi wanda duk an jagwalgwalashi da k'ayoyi, haka suka dan tsinci na tsinta suka zubda sauran.
Bayan sun kammala, Amina ta rufe kicin din bayan ta kashe fitila, ta rage fitilun falon sannan suka shige dakinsu suma.
"Bazasu dawo falon ba?" Cewar Ummi.
Ta gyada mata kai. "Ai kuma shikenan, acan babban falon Hajiya suka fi zama, matukar kinga sun shige, toh sai kuma wata safiyar, don daga nan kowa makwancinsa yake nufa."
Ummi ta jinjina kai kawai.
DAN ADAM
@Rufaida Omar
05
Bayan shigarsu Amina ta dubeta.
"Idan kika bi shawarwarin da zan baki, toh lallai zaki zauna da kowa lafiya a gidannan. Yanzu na lura kina tattare da gajiya, ki kwanta ki huta, gobe ma yi maganar idan Allah Ya kaimu da rai da lafiya. Kinji ko?"
Ta gyada kanta tana murmushi, haka kawai ta ji tana kaunar Amina.
"Toh Anti." Antin da ta kirata da shi ya sanyaya ranta sosai, itama ta ji tana kaunarta kamar yar uwarta ta jini. Tana mamakin uwar da ta haifi yarinya kyakkyawa har haka, ta juma iya barinta ta fito aikatau. Kodayake, rayuwa ce ke sanyawa wani lokacin, ba don rai yana so ba. Ita ta ta6a zaton zatayi wani aikatau? Ko a mafarki a'a.
Ta barwa Ummi katifa; ita kuwa tayi amfani da bargo ta shimfida a gefenta ta kwanta. Ummi na jin sadda take zuba ruwan addu'o'i, abin ya bata sha'awa. Daga nan bacci ya kwasheta batare da ta shirya ba.
■●♣♣♣♣♣▪▲♥♥♥★★★★★
"Don ubanki saura kiyi min halin kauyenci sai na shak'e ki kin mutu har lahira. Banason yawan kalle-kalle. Kiyi ladabi so..."
Sauran maganar ya mak'ale a fatar bakinta ganin an soma k'ok'arin bud'e k'ofar.
Maigadin ya d'an lek'o da kansa. Farin buzu ne. Ganin Yaha ya sanyashi sakin fuska.
"A'a mai yara, kaine?"
Hakanan yake kiranta. Tayi dariya.
"Ni ce dai Baba. Hajiyar na ciki ko?"
Ya bata hanya ta shigo yana amsa mata.
"Eh yana nan. Ina ka samo d'an garinmu?"
Ya fad'a yana duban Ummi wacce ta durkusa da rawar jiki ta gaisheshi.
Yaha ta dubeta tayi mata alamun ta mik'e.
"Wannan ba 'yar garinku bace. 'Yar Maiduguri ce."
"Anya? Yana kama da mu." Yaha dariya kawai ta d'anyi batace uffan ba.
Daga haka sukayi ciki.
Ummi na bin farfajiyar da kallo a sace don bataso Yaha ta kamata tana kallon bayan ta ja mata kunne. Babban gida ne sosai, an k'awatashi da shuke-shuke. Daga wajen ka rantse ba shi da wani kyau ko girma don kuwa ko fenti ba'ayi ba daga wajen.
Haka suka isa har bakin wata k'ofa. Yaha ta murd'a ta shiga. Suka cigaba da tafiya a doguwar barandar dake wajen har suka iso tsakar gidan. Acan bakin rariya, wata babbar mace dattijuwa ce ke zaune saman kujera irin ta tsakar gida tana wanke-wanke. Ganin Yaha ta washe baki.
"A'a, lale marhabin da Hajiya Yaha. Yau kuma zuwan rana ce?"
Yaha ta numfasa fuskarta na nuna gajiya.
"Bari kawai Ramma, duk a gajiye nake. Hajiyar na ciki mu k'arasa?"
Ramma fuska a sake ta amsa tana duban Ummi wacce ke takure jikin bango.
"Eh tana ciki." Ummi da sauri ta gaisheta. Ramma ta amsa. Har suka kama hanya Ramma na binta da kallo, yarinyar da alamu zasu d'asa da Hajiya Madina, don kuwa da alama nutsastsiya ce
DAN ADAM
@Rufaida Omar
04
"Sannu Ummi."
Muryar Amina ta katsemata tunani, ta dubeta, sukayi murmushi a tare.
"Yauwa."
Amina ta ninke abin sallar ta ajiye a gefe. Zama tayi a gefen katifa kusa da Ummi tana dubanta.
"Daga wane gari kuke?"
"Ringim." Ta amsa a takaice.
"Lallai, baku da nisa sosai."
Ummi zuwa yanzu ta dan saki jiki da Amina ganin irin yanda take janta a jiki. Wannan yasa itama bata ji nauyin tambayarta ba.
"Ke ba anan kusa kike ba?"
Ta gyada kai.
"Anan dai nayi rayuwata, amma mahaifina d'an Maradi ne can cikin jamhuriyar Nijar. Zama da neman abinci ne ya kawoshi Nijeriya sukayi aure da Innata, amma yanzu ya rasu, ya barmu mu hudu yaransa. Ni ce 'ya ta uku a cikinsu."
Ummi ta d'an tallafi kumatunta.
"Kema aiki kike yiwa Hajiya?"
Amina ta murmusa.
"Ni ina yiwa Hajiya Mama aiki ne, kanwar Hajiyarnan ce, abinda yasa kika ganni a gidannan, sunyi tafiya ne da mijinta da yaransu, shine dalilin da yasa na dawo nan da zama kafin su dawo."
Ummi ta jinjina kai cike da gamsuwa. A ranta ta ji babu dad'i, kenan itama wataran zata bar gidan ta barta?
"Ya dai Ummi? Kinyi shiru ina magana."
Ummi a sanyaye ta girgiza kai.
"Bakomai."
Jin haka yasa Amina yin murmushi.
"Shikenan, tashi muje mu tattara falo da kicin kafin Hajiya tayi magana, ki dunga lura da dukkan abinda nakeyi, nasan karshe ke zaki maye gurbina."
Ummi bata ko damu ba, idan ana sabo da aikin wahala, ai yaci kuwa ace ta saba, ina take samun damar yin cikakken awa sadda tana gidan babanta batare da an had'ata da wani nannauyan aikin ba? Gashi anan har gatan da za'a gyara mata kai a bata wajen kwana tsaftatacce da abinci mai kyau ta samu. Ai babu abinda zata ce ga Ubangiji sai godiya.
Haka ta bi bayanta zugui-zugui suka fita. A falon suka iske Adnan da kannensa su biyu, wadanda ta ji Ramma ta ambacesu da Ihsan, Hanifa da Fahad wanda shi ne auta a d'akin nasu.
Adnan hankalinsa kacokam yana kan wayar hannunsa yana faman latse-latse, yayinda Ihsan ta dukufa wajen koyawa kannenta aikin gida da aka basu a makaranta. Shekarun Ihsan goma sha uku a duniya zata shiga na hud'u, sa'ar Ummi ce. Hanifa kuwa, tana da shekaru goma sha biyu bata da tazara tsakaninta da Ihsan, Fahad ne mai shekaru takwas a duniya. Daga kansa kuma, Hajiya Madina bata k'ara haihuwa ba.
Yaranta gaba daya su takwas ne cif, mata uku ne kafin zuwan Adnan duniya, Rahila, Na'ima, Aisha, gaba dayansu ukun suna gidajen aure.
Shigowarsu falon ne yasa su d'ago kai su dubesu. Adnan ya k'urawa Ummi ido fuskarsa a sake sannan ya maida dubansa ga Amina.
"Ummi sunanta ko?"
Amina ta gyada kai tana murmushi wanda ya riga ya zamto jikinta, ko kusa bata rabo da shi.
"Itace." Ummi ta durkusa ta gaisheshi da saurinta sannan ta gaida su Ihsan. Ai kuwa su Ihsan suka tuntsire da dariya. Adnan ya dauki filon kujera yana dariya ya jefi Ihsan da shi.
"(See you), mene abin dariyar? Ai na isa a gaisheni, kune dai daga yau kada ki k'ara gaishesu, na tabbatar kin girme musu." Ya karashe yana maida dubansa ga Ummin.
Ihsan ta jinjina kai.
"Tab, wallahi saidai mu tafa, na tabbatar bazata girmeni ba. Kuma idan ma aka ajiye wannan a gefe ai 'yar aikinmu ce dole ta girmama mu."
Ta karashe tana jifan Ummi da kallon eh sun isa. Ummi dai ta kara sunkuyar da kanta. Amina batace komai ba don kuwa bata fiye shiga harkar Ihsan ba, sanin da tayi mata na cewa ta tsani wasa da duk wani wanda yake karkashinsu. A ganinta, bai kai har a zauna a sakar mishi fuska ba.
Abin yakan bawa Amina mamaki, yarinya tun bata tafasa ba tana neman k'onewa? Ta tabbata nan gaba idan Ihsan tafi haka za'a ga abu.
"Zaki fara ko?" Cewar Adnan lokacin da ya mike tsaye.
Ihsan ta dara a karo na biyu sannan ta dubi su Hanifa.
"Malamai ku maido hankalinku mu cigaba. Nasoma jin bacci wallahi."
Wannan yasa su Hanifa nutsuwa don suna d'an shakkarta kasancewarta itama wani sa'in akwai masifa. Hakanan ta iya kaiwa mutum bugu, kodan ita din tana da jiki kamar kazar gona.
"Muje Ummi."
Sai lokacin Ummi ta mike, Amina daman tana tsaye bata russuna ba. Tasan Ummin itama don yau ta zo ne, amma ita kam tuni an wuce wajen, don wani lokacin bata daukar rainin Ihsan, saidai duk randa ta biyemata suka yi cacar baki ko yaya ne, toh fa tana shan zagi da gori wajen Hajiya Madina. Sam, bata daukar cin mutunci akan yaranta, komin girmanka, muddin ka ta6a mata yara toh fa zatasan yanda tayi ta rama. Idan kuwa daga matan gidan ne, acan fadar maigidan ake k'ulla musu k'ullalliya. Shi kuwa ya hau ya zauna.
Haka Ummi ta taimaka suka kammala gyara komai na kicin sukayi wanke-wanke. Lokacin ana gabatar da sallar isha'i a masallacin unguwa.
A gurguje suka fito suka tattara falon, Ummi na lura da komai, a karshe bayan sun kammala, Amina ta fiddo dukkan abinda tasan zasu bukata wajen cin abinci ta jera bayan ta shimfid'a babbar ledar cin abinci a tsakar falon. Daga nan ta dubi Ummi.
"Jeki kiyi sallah, zan sanarwa Hajiya mun kammala."
"Toh."
Daga haka Amina ta mik'a wani d'an (Corridor) ita kuwa ta nufi dakinsu.
Har ta idar da sallar Amina bata dawo ba, nan kuma ta zauna ta soma gyangyadi don kuwa ba karamin gajiya tayi ba. Ta kwanta saman katifar dake shimfide ta mutum d'aya, wani dadi taji ya ratsata, yayinda iskar fanka ke kad'ata.
"Ashe nima zan kwana saman katifa wataran?"
Ta fad"a a fili. Tana nan kwance ta ji shigowar Amina. Da sauri kuma ta mik'e zaune tana mutsistsika ido.
"Har kin soma bacci wai? Taso mu ci abinci."
Ta mike ta bi bayanta, falon wayam, kadan-kadan ta dunga jiyo sautin dariya da hirarrakinsu daga can cikin da batasan iyaka zurfi da yanayinsa ba.
Amina ta kammala kwashe komai ta wanke na wankewa, tayi mamakin yanda bata nemi tayinta ba. Suka zauna suka ci tuwo da miya sukayi nak, a karshe suka sha ragowar romon kifi wanda duk an jagwalgwalashi da k'ayoyi, haka suka dan tsinci na tsinta suka zubda sauran.
Bayan sun kammala, Amina ta rufe kicin din bayan ta kashe fitila, ta rage fitilun falon sannan suka shige dakinsu suma.
"Bazasu dawo falon ba?" Cewar Ummi.
Ta gyada mata kai. "Ai kuma shikenan, acan babban falon Hajiya suka fi zama, matukar kinga sun shige, toh sai kuma wata safiyar, don daga nan kowa makwancinsa yake nufa."
Ummi ta jinjina kai kawai.
DAN ADAM
@Rufaida Omar
05
Bayan shigarsu Amina ta dubeta.
"Idan kika bi shawarwarin da zan baki, toh lallai zaki zauna da kowa lafiya a gidannan. Yanzu na lura kina tattare da gajiya, ki kwanta ki huta, gobe ma yi maganar idan Allah Ya kaimu da rai da lafiya. Kinji ko?"
Ta gyada kanta tana murmushi, haka kawai ta ji tana kaunar Amina.
"Toh Anti." Antin da ta kirata da shi ya sanyaya ranta sosai, itama ta ji tana kaunarta kamar yar uwarta ta jini. Tana mamakin uwar da ta haifi yarinya kyakkyawa har haka, ta juma iya barinta ta fito aikatau. Kodayake, rayuwa ce ke sanyawa wani lokacin, ba don rai yana so ba. Ita ta ta6a zaton zatayi wani aikatau? Ko a mafarki a'a.
Ta barwa Ummi katifa; ita kuwa tayi amfani da bargo ta shimfida a gefenta ta kwanta. Ummi na jin sadda take zuba ruwan addu'o'i, abin ya bata sha'awa. Daga nan bacci ya kwasheta batare da ta shirya ba.
■●♣♣♣♣♣▪▲♥♥♥★★★★★