Sashe 107
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Congratulations, you are two months pregnant."
Sunkuyar da kanta ta yi, ta fahimci me ya ke nufi, wato dai tana da ciki wata biyu. Faruk mikewa ya yi ya karasa ya rungume Yayansa suna dariya.
"Congratulations my lil, Hajiyarmu zata yi farinciki da jin hakan."
Sukayi dariya. Tunda Ummi ta sauke kanta bata k'ara dagoshi ba har zuwa sadda Faruk ya dawo ya zauna gami da lalubo hannunta yasa cikin nasa, idanu ta lumshe ta saci dubansa, shima ita ya ke kallo. A hankali bakinsa ya motsa.
"I love you." Ta fahimci hakan ya fada, ta kauda kanta tana murmushi gami da damke hannunsa alamun ta amsa. Hankalin Ridwan ba ya kansu, ya gama rubuta magunguna kafin ya mikowa Faruk.
"Sai a kula banda yawan aikace-aikace. Yau za ka shiga Gida ne?"
"Ai can na nufa ma."
Sukayi dariya, Ummi hankalinta ya tashi, kamar ta ce mishi kar su je, tasan kawai kunya zai sanyata gaban su Hajiya.
Ai kuwa suna fita ta hau rok'onsa akan kada su je, baice uffan ba banda murmushi. Saida suka je din, Ikram ta tarbesu kamar ta hadiyesu don yanzu bil hakki tana kaunar Ummi, soyayyar Gidado ya shafeta.
Hajiya ta yi murnar jin cewar Ummi na dauke da juna biyu, don Faruk da bakinsa ya fadamata, ta hau yi mata gargadi akan ta kula za'a samo mata mai tayata hidima, ta nuna a barshi saidai Hajiya ta dage sai anyi hakan. Faruk bai ce uffan ba don da ta raayinsa shi kansa bazai so ba saidai yana tuna maganar Dakta da ya ce ta dunga hutawa ya amince.
Da Magriba tana dakin Ikram sunyi sallah suka yi zaman hira, anan Ikram ke labartamata yanda sosai yanzu Gidado ke damuwa da ita har idan ya ji shiru bata hau online ba zai damu ya kirata a waya.
"Ikon Allah." Shine kawai abinda Ummi ta ce, duk kuwa da cewar ta yi mata murnar hakan saidai kasan ranta tana tsoron abinda zai je ya dawo idan Hafsa ta samu labari. Ko da wane ido za ta dubeta?
A hakikanin gaskiya ko a baya idan Gidado bai jin wani abu game da Ikram to a yanzun yana ji, don ita kanta Ummin ta fahimta ta yanda duk sadda sukayi waya sai ya yi maganar Ikram, wataran ya ce suna hira wataran ya dunga yabon halin kirkinta . A bakinsa ne ma ta ji cewar suna chatting Abubakar ne ya bashi lambarta. Ko Abubakar din da kullum suke waya bai sanarmata ba.
"Ya karatun? Kina ganewa sosai ko?"
Ikram ta fada gami da katse shirun.
Murmushi Ummi ta yi.
"Ina fahimta."
"Allah Ya taimaka, ga Azumi ma ance nan da sati biyu ko?"
Ta gyada kai.
"Hakane, abin ba wuya, kamar yau ne muke lissafi da Anti Amina ta ke cemin bayan Azumi bikinta, yanzu har ga azumin ya zo."
Dariya Ikram ta yi.
"Kina ban dariya idan kina ce mata Anti, sa"arki ce fa."
Dariya itama Ummin ta yi kadan.
"Ta cancanta, ita ta mayemin gurbin uwa kuma Yaya a gurina alokacin da bani da kowa cikin DAN ADAM dake son ya ra6eni, alokacin da kowa ya gujeni. Ita ke cemin na yi wancan mai kyau ne, kada na yi wannan babu kyau, ta zama Malama agareni tun ban kai ga soma zama a aji ba. Kinga kuwa ta cancanta na kirata da Antina."
Ikram ta gyada kai, ita kam yanzu Ummi na burgeta, mutum ba zai san tana da shiga rai ba sai ya zauna da ita, daman bata tsaneta ba tun a baya sai sadda Faruk ya ce zai aureta har ya mareta akanta ga kuma taya Ihsan kishi.
"Lallai ta cancanta har ta wuce cancantar ma. Ni kuma nan gaba ina fatan zama yayarki."
Ta karashe da gwalo, Ummi ta gane, wato ta zama matar Gidado.
Sukayi dariya lokaci guda.
"Dagaske nake, kinsan kuwa Hajiya da Daddy sunce saidai nima na karasa jami'a a gidan mijina, da zarar mun gama jarabawarnan ta karshe sai aure."
Ta jinjina maganar.
"Kice tare za mu sha bikinku da su Ihsan."
Dariya Ikram ta yi sai kuma ta maida fuskarta kalar damuwa.
"Allah Yasa mu auri wanda yafi alheri garemu."
"Amin."
Sai bayan isha'i sannan suka bar gidan zuwa gidansu. Nan kuwa aka shiga rainon ciki babu wasa, yarinya karama aka kawomata, batafi shekaru goma sha hudu ba. Farkon kawota Ummi idanu ta zubamata tana kallonta cike da tausayawa sannan ta dubi wacce ke tare da ita wacce aka kira da mahaifiyarta da ko kusa bata ga kama ba.
"Yanzu Baba wannan aiki zata dunga yi?"
"Eh, aiki kowanne da ki ke so ki sanyata, babu wanda ba zata iya yi gareki ba."
Ta k'ara duban yarinyar wacce ta yi wani firi-firi da idanu. Tausayinta ya kamata.
"Shikenan."
Jin haka matar ta hau washe baki tana gyara mayafi zata mike.
"To bari na koma tunda naga gidan, ke kuma Batula ki kula, kada inji kar in soma gani kin sa6awa uwar dakinki kinji ko? Hajiya don Allah ki dunga kula yarinyar akwai shegen munafunci."
Ummi da ke jin kamar ta makureta ta ce.
"Wane irin munafunci kuma?"
"Um, kada ta dunga yi miki la6e wai, to shikenan ai, sai anjima, Allah Ya kara arziki."
Ta karashe cikin basar da wancan maganar. Ummi ta bata dubu biyu ta hau mota. Nan ta hau zuba godiya ta fice.
Ta maida hankali ga yarinyar da aka kira da Batula.
"Sannu Batula, inaso ki saki jiki da ni, ki rikeni tamkar yayarki, ni bazan cutar da ke ba, zan kuma rikeki bisa amana kinji ko?"
Cikin mamaki mai tsanani da rashin gaskatawa ta gyada kai don gani ta ke kamar wani salo ne na cutarwa, gida na uku kenan da aka kawota, wadancan biyun duk guduwa ta yi saboda matsi da takura.
"Fadamin gaskiya Batul, mene alak'arki da wannan matar? Dagaske itace ta haifeki?"
Ta girgiza kai cikin raunin zuciya kiris take jira ta fashe da kuka.
"A'a, kanwar mamana ce uwa daya uba daya da ta rasu."
Runtse idanu Ummi ta yi ranta na suya.
"Meyasa ta ke kawo ki aikatau?"
"Babana ne ya aureta bayan rasuwar Mamana, ba da son ransa ta ke kawoni gidan aiki ba, ko yau da zamu taho da kuka muka rabu da shi. Kullum saita dakeni, komai ni nake yi mata."
Hawaye Ummi ta shiga fitarwa, DAN ADAM kenan, ace 'yar yayarki ki ke yiwa rikon sakainar kashi? Duniya abin tsoro.
Ummi ta tabbatar mata zata riketa bisa amana, ta bata kyakkyawan muhalli ta sanyata a makaranta. Ita da kanta ta wankemata kanta bayan ta tsefemata kitso, suna yi suna hira Batul na kara bata labarin kauyensu Maraba.
Cikin kayanta ta dauko wanda ya yi mata kadan ta bata ta sanya kasancewar yarinyar akwai tsawo nan suka zauna das a jikinta.
Koda Faruk ya dawo, ya yi mamaki, bai gane ko wacece ba ganin tana zaune a kasa suna hira da Ummi suna dariya. Batul ta gaisheshi ta yi ciki, ya zauna yana duban Ummi wacce ta tashi ta tarbeshi.
"Ummina wacece wannan?"
Da murmushi ta amsa.
"Itace wacce Hajiya ta turo zata tayani aikace-aikace."
Ya jinjina kai.
"Naga kamar wata kanwarki kunata hira ai."
Murmushin ta kara yi.
"Kanwartawa ce ma. Tausayi take ban."
Nan ta labarta mishi labarinta, shi kansa ya yi mamaki.
"Allah kenan, DAN ADAM babu mai iya masa sai Allahn da Ya halicceshi, Allah Ya datar da mu."
"Amin."
Tun daga wannan ranar Ummi ta riki Batul bisa amana, har makaranta an sanyata na Arabi.
Haka har azumi ya zo, nan ma komai tare sukeyi, cikin azumin ne kuma Intisar ta haihu diyarta mace. Kowa ya yi murna da hakan, ranar suna aka sanya sunan Hajiya Mama, wato Sadiya. Hajiya Mama ta ji dadin wannan karar da sukayi gareta.
Anci suna an kare lafiya kowa na yaba yanda Faruk ke nan nan da Ummi ko gaban mutane ne ba ya iya 6oye son da ya ke mata.
A ranar sunan ma ganin yanda Ummi ke yiwa Batul saida su Jidda suka tofa.
"Wai wannan inace 'yar aikinki ce ki ke mata haka?"
Murmushi ta yi.
"Ni ina mata kallon mutum mai daraja."
"Don kema a baya yar aikin ce ko?"
Cewar Fadila.
Abin ya ta6a zuciyar Intisar da su Ikram, Ummi kuwa ko a jikinta ta soma bata amsa.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
126
Sunkuyar da kanta ta yi, ta fahimci me ya ke nufi, wato dai tana da ciki wata biyu. Faruk mikewa ya yi ya karasa ya rungume Yayansa suna dariya.
"Congratulations my lil, Hajiyarmu zata yi farinciki da jin hakan."
Sukayi dariya. Tunda Ummi ta sauke kanta bata k'ara dagoshi ba har zuwa sadda Faruk ya dawo ya zauna gami da lalubo hannunta yasa cikin nasa, idanu ta lumshe ta saci dubansa, shima ita ya ke kallo. A hankali bakinsa ya motsa.
"I love you." Ta fahimci hakan ya fada, ta kauda kanta tana murmushi gami da damke hannunsa alamun ta amsa. Hankalin Ridwan ba ya kansu, ya gama rubuta magunguna kafin ya mikowa Faruk.
"Sai a kula banda yawan aikace-aikace. Yau za ka shiga Gida ne?"
"Ai can na nufa ma."
Sukayi dariya, Ummi hankalinta ya tashi, kamar ta ce mishi kar su je, tasan kawai kunya zai sanyata gaban su Hajiya.
Ai kuwa suna fita ta hau rok'onsa akan kada su je, baice uffan ba banda murmushi. Saida suka je din, Ikram ta tarbesu kamar ta hadiyesu don yanzu bil hakki tana kaunar Ummi, soyayyar Gidado ya shafeta.
Hajiya ta yi murnar jin cewar Ummi na dauke da juna biyu, don Faruk da bakinsa ya fadamata, ta hau yi mata gargadi akan ta kula za'a samo mata mai tayata hidima, ta nuna a barshi saidai Hajiya ta dage sai anyi hakan. Faruk bai ce uffan ba don da ta raayinsa shi kansa bazai so ba saidai yana tuna maganar Dakta da ya ce ta dunga hutawa ya amince.
Da Magriba tana dakin Ikram sunyi sallah suka yi zaman hira, anan Ikram ke labartamata yanda sosai yanzu Gidado ke damuwa da ita har idan ya ji shiru bata hau online ba zai damu ya kirata a waya.
"Ikon Allah." Shine kawai abinda Ummi ta ce, duk kuwa da cewar ta yi mata murnar hakan saidai kasan ranta tana tsoron abinda zai je ya dawo idan Hafsa ta samu labari. Ko da wane ido za ta dubeta?
A hakikanin gaskiya ko a baya idan Gidado bai jin wani abu game da Ikram to a yanzun yana ji, don ita kanta Ummin ta fahimta ta yanda duk sadda sukayi waya sai ya yi maganar Ikram, wataran ya ce suna hira wataran ya dunga yabon halin kirkinta . A bakinsa ne ma ta ji cewar suna chatting Abubakar ne ya bashi lambarta. Ko Abubakar din da kullum suke waya bai sanarmata ba.
"Ya karatun? Kina ganewa sosai ko?"
Ikram ta fada gami da katse shirun.
Murmushi Ummi ta yi.
"Ina fahimta."
"Allah Ya taimaka, ga Azumi ma ance nan da sati biyu ko?"
Ta gyada kai.
"Hakane, abin ba wuya, kamar yau ne muke lissafi da Anti Amina ta ke cemin bayan Azumi bikinta, yanzu har ga azumin ya zo."
Dariya Ikram ta yi.
"Kina ban dariya idan kina ce mata Anti, sa"arki ce fa."
Dariya itama Ummin ta yi kadan.
"Ta cancanta, ita ta mayemin gurbin uwa kuma Yaya a gurina alokacin da bani da kowa cikin DAN ADAM dake son ya ra6eni, alokacin da kowa ya gujeni. Ita ke cemin na yi wancan mai kyau ne, kada na yi wannan babu kyau, ta zama Malama agareni tun ban kai ga soma zama a aji ba. Kinga kuwa ta cancanta na kirata da Antina."
Ikram ta gyada kai, ita kam yanzu Ummi na burgeta, mutum ba zai san tana da shiga rai ba sai ya zauna da ita, daman bata tsaneta ba tun a baya sai sadda Faruk ya ce zai aureta har ya mareta akanta ga kuma taya Ihsan kishi.
"Lallai ta cancanta har ta wuce cancantar ma. Ni kuma nan gaba ina fatan zama yayarki."
Ta karashe da gwalo, Ummi ta gane, wato ta zama matar Gidado.
Sukayi dariya lokaci guda.
"Dagaske nake, kinsan kuwa Hajiya da Daddy sunce saidai nima na karasa jami'a a gidan mijina, da zarar mun gama jarabawarnan ta karshe sai aure."
Ta jinjina maganar.
"Kice tare za mu sha bikinku da su Ihsan."
Dariya Ikram ta yi sai kuma ta maida fuskarta kalar damuwa.
"Allah Yasa mu auri wanda yafi alheri garemu."
"Amin."
Sai bayan isha'i sannan suka bar gidan zuwa gidansu. Nan kuwa aka shiga rainon ciki babu wasa, yarinya karama aka kawomata, batafi shekaru goma sha hudu ba. Farkon kawota Ummi idanu ta zubamata tana kallonta cike da tausayawa sannan ta dubi wacce ke tare da ita wacce aka kira da mahaifiyarta da ko kusa bata ga kama ba.
"Yanzu Baba wannan aiki zata dunga yi?"
"Eh, aiki kowanne da ki ke so ki sanyata, babu wanda ba zata iya yi gareki ba."
Ta k'ara duban yarinyar wacce ta yi wani firi-firi da idanu. Tausayinta ya kamata.
"Shikenan."
Jin haka matar ta hau washe baki tana gyara mayafi zata mike.
"To bari na koma tunda naga gidan, ke kuma Batula ki kula, kada inji kar in soma gani kin sa6awa uwar dakinki kinji ko? Hajiya don Allah ki dunga kula yarinyar akwai shegen munafunci."
Ummi da ke jin kamar ta makureta ta ce.
"Wane irin munafunci kuma?"
"Um, kada ta dunga yi miki la6e wai, to shikenan ai, sai anjima, Allah Ya kara arziki."
Ta karashe cikin basar da wancan maganar. Ummi ta bata dubu biyu ta hau mota. Nan ta hau zuba godiya ta fice.
Ta maida hankali ga yarinyar da aka kira da Batula.
"Sannu Batula, inaso ki saki jiki da ni, ki rikeni tamkar yayarki, ni bazan cutar da ke ba, zan kuma rikeki bisa amana kinji ko?"
Cikin mamaki mai tsanani da rashin gaskatawa ta gyada kai don gani ta ke kamar wani salo ne na cutarwa, gida na uku kenan da aka kawota, wadancan biyun duk guduwa ta yi saboda matsi da takura.
"Fadamin gaskiya Batul, mene alak'arki da wannan matar? Dagaske itace ta haifeki?"
Ta girgiza kai cikin raunin zuciya kiris take jira ta fashe da kuka.
"A'a, kanwar mamana ce uwa daya uba daya da ta rasu."
Runtse idanu Ummi ta yi ranta na suya.
"Meyasa ta ke kawo ki aikatau?"
"Babana ne ya aureta bayan rasuwar Mamana, ba da son ransa ta ke kawoni gidan aiki ba, ko yau da zamu taho da kuka muka rabu da shi. Kullum saita dakeni, komai ni nake yi mata."
Hawaye Ummi ta shiga fitarwa, DAN ADAM kenan, ace 'yar yayarki ki ke yiwa rikon sakainar kashi? Duniya abin tsoro.
Ummi ta tabbatar mata zata riketa bisa amana, ta bata kyakkyawan muhalli ta sanyata a makaranta. Ita da kanta ta wankemata kanta bayan ta tsefemata kitso, suna yi suna hira Batul na kara bata labarin kauyensu Maraba.
Cikin kayanta ta dauko wanda ya yi mata kadan ta bata ta sanya kasancewar yarinyar akwai tsawo nan suka zauna das a jikinta.
Koda Faruk ya dawo, ya yi mamaki, bai gane ko wacece ba ganin tana zaune a kasa suna hira da Ummi suna dariya. Batul ta gaisheshi ta yi ciki, ya zauna yana duban Ummi wacce ta tashi ta tarbeshi.
"Ummina wacece wannan?"
Da murmushi ta amsa.
"Itace wacce Hajiya ta turo zata tayani aikace-aikace."
Ya jinjina kai.
"Naga kamar wata kanwarki kunata hira ai."
Murmushin ta kara yi.
"Kanwartawa ce ma. Tausayi take ban."
Nan ta labarta mishi labarinta, shi kansa ya yi mamaki.
"Allah kenan, DAN ADAM babu mai iya masa sai Allahn da Ya halicceshi, Allah Ya datar da mu."
"Amin."
Tun daga wannan ranar Ummi ta riki Batul bisa amana, har makaranta an sanyata na Arabi.
Haka har azumi ya zo, nan ma komai tare sukeyi, cikin azumin ne kuma Intisar ta haihu diyarta mace. Kowa ya yi murna da hakan, ranar suna aka sanya sunan Hajiya Mama, wato Sadiya. Hajiya Mama ta ji dadin wannan karar da sukayi gareta.
Anci suna an kare lafiya kowa na yaba yanda Faruk ke nan nan da Ummi ko gaban mutane ne ba ya iya 6oye son da ya ke mata.
A ranar sunan ma ganin yanda Ummi ke yiwa Batul saida su Jidda suka tofa.
"Wai wannan inace 'yar aikinki ce ki ke mata haka?"
Murmushi ta yi.
"Ni ina mata kallon mutum mai daraja."
"Don kema a baya yar aikin ce ko?"
Cewar Fadila.
Abin ya ta6a zuciyar Intisar da su Ikram, Ummi kuwa ko a jikinta ta soma bata amsa.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
126