Sashe 74
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"Wayyo Allah!!" Ta yi furucin da karfi tana mai mikewa zaune a firgice. Malam Balarabe ya tashi a tsorace yana duban Saude. Sai uban gumi ta ke had'awa duk kuwa da cewar garin ya danyi sanyi.
"Lafiya Saude?"
Ya tambaya cike da fargaba.
Saude dake dafe da kirjinta tana numfarfashi, ta dubeshi, sai lokacin ta dawo hayyacinta. Ta yi tsai da ido tana dubansa domin kuwa tsoro ya ke bata, gani ta ke yi kamar mafarkinta gaskiya ne, wai Malam Balarabe ne da daukarta ya jefa a rijiya bayan ya bata kyakkyawan mari har biyu a gefensa kuwa Hasiya kishiyarta ce tsaye tana faman kyakyatar dariya.
"Addua ya kamata ki dunga yi idan kinyi mafarki ba wai ihu ba. Duk kin tsorata ni."
Daga haka ya ja guntun tsaki ya juyamata baya, ta bishi da kallo cikin zubda ruwan hawaye sannan itama ta kwanta rigingine tana goge fuska.
'Meke shirin faruwa? Kada fa asirinmu ya tonu.'
Ta ke maganar a zuciyarta, ta kudurta komawa wajen Bokanya gobe don ta k'ara bincika mata lamarin. Dakyar ta samu ta koma bacci a wannan daren.
*** *** ***
ABUJA
Mutan Abuja da karfe biyu suka kama hanyar Ringim, wannan zuwa na musamman ne, Hajiya da Gen. Ahmad ne sai ko Babban Yaya da Ridwan sai kuma uban gayyar Faruk da Ummi da Yaha wacce suna shigowa Ringim ta soma rarraba ido na son nuna inda za su sha kwana. Haidar kadai ne bai samu zuwa ba.
Ummi gabanta sai bugu ya ke da sauri-sauri, ga mararta da ta k'ulle, tana cike da tsoron irin cin kashin da za'a yiwa bayin Allahn da suka san daraja ta dan Adam. Wane irin tarba zata samu daga mahaifinnata? Sam, bata da masaniya. Hajiya Babba ta lura da yanayin da ta shiga, ta ji ta bata tausayi don kuwa ta ji daga bakin Yaha irin wahalar da ta sha a hannun ubannata da matarsa, ta dan dafa hannunta, wannan yasa Ummin dubanta. Murmushi na karfafa gwuiwa ta sakarmata.
"Ki kwantar da hankalinki Ummi, ki yi ta addu'a, babu abinda yafi karfin Ubangijinmu."
Ta jinjina kai tana dan murmushi. Daga haka ta cigaba da addu'o'inta har Yaha ta nuna layin da zasu shiga.
Saude ce tsaye rik'e da k'ugu tana faman jan tsaki, a zaune saman kujerar falon, Habiba ce tana faman kai lomar dan wake. Mariya na waje suna wasa da yara.
"Ki yiwa Allah ki taso mu wuce, wai menene haka?"
Habiba ta dauki dunkulen dan wake guda ta jefa a bakinta tana mai dubanta cikin yanayi na santi.
"Ai kwarankwatsa sai na gama, wa ya ce ki yi dan wake alhalin kinsan bana ganinsa na kyale balle kuma da yanzun ma babu abinda na saka a cikina, na fadamiki fa daga kasuwa na fito."
Ta k'ara sud'e man wanda ya hade da yaji sannan ta cigaba da magana.
"Na fadamiki ki saka ranki a inuwa, ko makamancin tunaninki bazai afku ba, idan yar banza ta takura mana sai ma mu saka Yaha ta maido diyarta ta mu kasheta mu kashe banza."
Saude wacce ta gaji da tsayuwa ta zauna sai lokacin ta dan numfasa.
"Anya hakan ma bai fi ba?"
Kafin Habiba ta samu abin cewa, sallamar Malam Balarabe ta karad'e kunnuwansu. Suka dubi juna da mamaki kafin kuma Saude ta yi wuf ta fito.
Ya ajiye ledar hannunsa a gefe.
"Malam lafiya yau ka dawo da wuri?"
Ya dauki buta jikinsa duk a sanyaye ya nufi hanyar bandaki yana fadin.
"Ina zuwa."
Ganin yanda ya ke magana a sanyaye ya kad'a yan hanjin cikinta duk kuwa da cewa tasan halittarsa can daman ba mai zafi bane, idan har kaga bacin ransa to ba karamin kai shi bango ka yi ba.
Habiba ta fito rike da kwanon dan wake a hannunta, cikin muryar rad'a ta ce.
"To bari na koma na cigaba da bawa cikina hakkinsa kafin nan kun kammala."
Ta karashe da dariyar shakiyanci Saude na harararta.
"Malama yanzu zan shigo."
Ita dai Habiba ta sa kai ta fice.
Bayan fitowar Malam Balarabe ya ja kujera yar tsugunno ya zauna gami da zabga uban tagumi. Cikin fargaba ta ce.
"Wai menene? Ko babu kasuwar balangun ne yau naga ko rana bata ida faduwa ba ka taho."
Ya numfasa.
"Haruna(yaronsa) na bari a can na taho, jikin nawa duk babu dadi, haka kawai na tsinci kaina da jin wani sanyin jiki, fatana Allah Yasa alheri ne."
Saude ta yi tsuru da idanu, yau kuma meke shirin faruwa?
Shigowar Mariya a guje ne ya katse tunanin kowannensu.
"Umma! Umma!!"
Suka maida hankali gareta jin yanda ta ke ihun kira, babu wanda gabansa bai fad'i ba acikinsu. Malam Balarabe ne ya riko hannunta.
"Menene 'yar Baba?"
Tana haki tana nuna kofar waje da yatsa, bakinta a washe ta ke fadin.
"Wasu ne suka zo da katuwar mota suna..."
Kafin ta karasa magana suka tsinci sallama mutane, Yaha ce a gaba Hajiya Babba na biye da ita.
Saude ta zaro ido.
"Yaha?" Malam Balarabe ya mike yana mai amsa sallamarsu yana dubansu duban rashin sani don daidai da Yahar bai rike kamanninta ba.
Kafin kuma wani cikinsu ya kara cewa komai, Ummi itama ta sanyo kai da sallamarta wanda dakyar ta iya daurewa ta yi shi don a matukar tsorace take.
Ganinta yasa Malam Balarabe zaro ido ya nunota da yatsa.
"Ha...ha..si..daman ba ki mutu ba?!"
Kawai sai ya zube anan, ihu da salatin Ummi ne ya ankarar da Saude cewa lallai yau ABINDA AKE GUDU ya afku!
Ta kasa koda kwakkwarar motsi tana ganin Ummi ta yi kanshi tana jijjigawa.
Faruk da suke waje, yana jin ihun Ummi baisan sadda ya sanya kai cikin gidan ba su Babban Yaya na biye da shi.
Hajiya Babba ta hangi buta, da sauri ta nufi butar ta dauko, Faruk ne cikin zafin nama ya kar6a ya soma yayyafa mishi, aka ci sa'a ya farfado. Saude jikinta sai kadawa ya ke yi tamkar mazari, ana haka itama Habiba ta shigo don kuwa ta ji hayaniya saidai bata gask'ata ba hakan yasa ta zo ganewa idanunta. Wata budurwa ta gani sanye da tsadaddun kaya durkushe tana kuka sai mazan dake tsaye a wajen.
Malam Balarabe aka kamashi ya zauna gami da jingina da bango.
"Sannu Baba."
Cewar su Babban Yaya, bai amsa ba sai binsu da ya ke yi da kallo kafin ya sauke idanunsa akan Ummi, da sauri ya runtse ido ya soma salati. Duk sai ya basu mamaki, babu kamar Ummi, mamakinta bai wuce na ganin wai mahaifinta ke tsoranta ba.
"Wai Malam lafiya?"
Saude ta yi maganar cikin rawar murya tana mai fatan ace Malam Balarabe ya koresu daga gidan matsayin ya ga fatalwa matarsa.
Ya nuna Ummi.
"Wai Hasiya ce dai ta dawo? Daman ba ta mutu ba?"
Tambayar da ya yi ne yasa hankalin su ya dan kwanta banda na Saude da Habiba wacce jin hakan yasa ta sulale ta koma gidanta, bata yi wata-wata ba ta dauki mayafi sai gidan Bokanya har jikinta na rawa tsabar firgici.
Acan kuwa, Yaha ta amsawa Malam.
"Aa Malam, wannan Hasiyar Ummi ce diyarka diyar marigayiya."
Ya kurawa Ummi idanu kamar yau ya soma ganinta, Ummi! Ummi!! Shi kuwa ina ta shiga kwana biyu ba ya ganinta?
((Ku yi hakuri, rashin chaji ke sa ku ji ni shiruuu..))
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
92
"Lafiya Saude?"
Ya tambaya cike da fargaba.
Saude dake dafe da kirjinta tana numfarfashi, ta dubeshi, sai lokacin ta dawo hayyacinta. Ta yi tsai da ido tana dubansa domin kuwa tsoro ya ke bata, gani ta ke yi kamar mafarkinta gaskiya ne, wai Malam Balarabe ne da daukarta ya jefa a rijiya bayan ya bata kyakkyawan mari har biyu a gefensa kuwa Hasiya kishiyarta ce tsaye tana faman kyakyatar dariya.
"Addua ya kamata ki dunga yi idan kinyi mafarki ba wai ihu ba. Duk kin tsorata ni."
Daga haka ya ja guntun tsaki ya juyamata baya, ta bishi da kallo cikin zubda ruwan hawaye sannan itama ta kwanta rigingine tana goge fuska.
'Meke shirin faruwa? Kada fa asirinmu ya tonu.'
Ta ke maganar a zuciyarta, ta kudurta komawa wajen Bokanya gobe don ta k'ara bincika mata lamarin. Dakyar ta samu ta koma bacci a wannan daren.
*** *** ***
ABUJA
Mutan Abuja da karfe biyu suka kama hanyar Ringim, wannan zuwa na musamman ne, Hajiya da Gen. Ahmad ne sai ko Babban Yaya da Ridwan sai kuma uban gayyar Faruk da Ummi da Yaha wacce suna shigowa Ringim ta soma rarraba ido na son nuna inda za su sha kwana. Haidar kadai ne bai samu zuwa ba.
Ummi gabanta sai bugu ya ke da sauri-sauri, ga mararta da ta k'ulle, tana cike da tsoron irin cin kashin da za'a yiwa bayin Allahn da suka san daraja ta dan Adam. Wane irin tarba zata samu daga mahaifinnata? Sam, bata da masaniya. Hajiya Babba ta lura da yanayin da ta shiga, ta ji ta bata tausayi don kuwa ta ji daga bakin Yaha irin wahalar da ta sha a hannun ubannata da matarsa, ta dan dafa hannunta, wannan yasa Ummin dubanta. Murmushi na karfafa gwuiwa ta sakarmata.
"Ki kwantar da hankalinki Ummi, ki yi ta addu'a, babu abinda yafi karfin Ubangijinmu."
Ta jinjina kai tana dan murmushi. Daga haka ta cigaba da addu'o'inta har Yaha ta nuna layin da zasu shiga.
Saude ce tsaye rik'e da k'ugu tana faman jan tsaki, a zaune saman kujerar falon, Habiba ce tana faman kai lomar dan wake. Mariya na waje suna wasa da yara.
"Ki yiwa Allah ki taso mu wuce, wai menene haka?"
Habiba ta dauki dunkulen dan wake guda ta jefa a bakinta tana mai dubanta cikin yanayi na santi.
"Ai kwarankwatsa sai na gama, wa ya ce ki yi dan wake alhalin kinsan bana ganinsa na kyale balle kuma da yanzun ma babu abinda na saka a cikina, na fadamiki fa daga kasuwa na fito."
Ta k'ara sud'e man wanda ya hade da yaji sannan ta cigaba da magana.
"Na fadamiki ki saka ranki a inuwa, ko makamancin tunaninki bazai afku ba, idan yar banza ta takura mana sai ma mu saka Yaha ta maido diyarta ta mu kasheta mu kashe banza."
Saude wacce ta gaji da tsayuwa ta zauna sai lokacin ta dan numfasa.
"Anya hakan ma bai fi ba?"
Kafin Habiba ta samu abin cewa, sallamar Malam Balarabe ta karad'e kunnuwansu. Suka dubi juna da mamaki kafin kuma Saude ta yi wuf ta fito.
Ya ajiye ledar hannunsa a gefe.
"Malam lafiya yau ka dawo da wuri?"
Ya dauki buta jikinsa duk a sanyaye ya nufi hanyar bandaki yana fadin.
"Ina zuwa."
Ganin yanda ya ke magana a sanyaye ya kad'a yan hanjin cikinta duk kuwa da cewa tasan halittarsa can daman ba mai zafi bane, idan har kaga bacin ransa to ba karamin kai shi bango ka yi ba.
Habiba ta fito rike da kwanon dan wake a hannunta, cikin muryar rad'a ta ce.
"To bari na koma na cigaba da bawa cikina hakkinsa kafin nan kun kammala."
Ta karashe da dariyar shakiyanci Saude na harararta.
"Malama yanzu zan shigo."
Ita dai Habiba ta sa kai ta fice.
Bayan fitowar Malam Balarabe ya ja kujera yar tsugunno ya zauna gami da zabga uban tagumi. Cikin fargaba ta ce.
"Wai menene? Ko babu kasuwar balangun ne yau naga ko rana bata ida faduwa ba ka taho."
Ya numfasa.
"Haruna(yaronsa) na bari a can na taho, jikin nawa duk babu dadi, haka kawai na tsinci kaina da jin wani sanyin jiki, fatana Allah Yasa alheri ne."
Saude ta yi tsuru da idanu, yau kuma meke shirin faruwa?
Shigowar Mariya a guje ne ya katse tunanin kowannensu.
"Umma! Umma!!"
Suka maida hankali gareta jin yanda ta ke ihun kira, babu wanda gabansa bai fad'i ba acikinsu. Malam Balarabe ne ya riko hannunta.
"Menene 'yar Baba?"
Tana haki tana nuna kofar waje da yatsa, bakinta a washe ta ke fadin.
"Wasu ne suka zo da katuwar mota suna..."
Kafin ta karasa magana suka tsinci sallama mutane, Yaha ce a gaba Hajiya Babba na biye da ita.
Saude ta zaro ido.
"Yaha?" Malam Balarabe ya mike yana mai amsa sallamarsu yana dubansu duban rashin sani don daidai da Yahar bai rike kamanninta ba.
Kafin kuma wani cikinsu ya kara cewa komai, Ummi itama ta sanyo kai da sallamarta wanda dakyar ta iya daurewa ta yi shi don a matukar tsorace take.
Ganinta yasa Malam Balarabe zaro ido ya nunota da yatsa.
"Ha...ha..si..daman ba ki mutu ba?!"
Kawai sai ya zube anan, ihu da salatin Ummi ne ya ankarar da Saude cewa lallai yau ABINDA AKE GUDU ya afku!
Ta kasa koda kwakkwarar motsi tana ganin Ummi ta yi kanshi tana jijjigawa.
Faruk da suke waje, yana jin ihun Ummi baisan sadda ya sanya kai cikin gidan ba su Babban Yaya na biye da shi.
Hajiya Babba ta hangi buta, da sauri ta nufi butar ta dauko, Faruk ne cikin zafin nama ya kar6a ya soma yayyafa mishi, aka ci sa'a ya farfado. Saude jikinta sai kadawa ya ke yi tamkar mazari, ana haka itama Habiba ta shigo don kuwa ta ji hayaniya saidai bata gask'ata ba hakan yasa ta zo ganewa idanunta. Wata budurwa ta gani sanye da tsadaddun kaya durkushe tana kuka sai mazan dake tsaye a wajen.
Malam Balarabe aka kamashi ya zauna gami da jingina da bango.
"Sannu Baba."
Cewar su Babban Yaya, bai amsa ba sai binsu da ya ke yi da kallo kafin ya sauke idanunsa akan Ummi, da sauri ya runtse ido ya soma salati. Duk sai ya basu mamaki, babu kamar Ummi, mamakinta bai wuce na ganin wai mahaifinta ke tsoranta ba.
"Wai Malam lafiya?"
Saude ta yi maganar cikin rawar murya tana mai fatan ace Malam Balarabe ya koresu daga gidan matsayin ya ga fatalwa matarsa.
Ya nuna Ummi.
"Wai Hasiya ce dai ta dawo? Daman ba ta mutu ba?"
Tambayar da ya yi ne yasa hankalin su ya dan kwanta banda na Saude da Habiba wacce jin hakan yasa ta sulale ta koma gidanta, bata yi wata-wata ba ta dauki mayafi sai gidan Bokanya har jikinta na rawa tsabar firgici.
Acan kuwa, Yaha ta amsawa Malam.
"Aa Malam, wannan Hasiyar Ummi ce diyarka diyar marigayiya."
Ya kurawa Ummi idanu kamar yau ya soma ganinta, Ummi! Ummi!! Shi kuwa ina ta shiga kwana biyu ba ya ganinta?
((Ku yi hakuri, rashin chaji ke sa ku ji ni shiruuu..))
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
92