Sashe 55
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
70
ABUJA
Misalin takwas na safe, Ummi ta kammala gyara sashen Hajiya duk jikinta a dar-dar, burinta ta yi ta kammala ta bar wajen kafin wani ya risk'eta, saidai cikin rashin sa'a tana murnar har ta kammala za ta tafi ba wanda ya fito, Ihsan ta fito falon tare da Ikram. Daman tun jiya suke dakonta. Tsayawa ta yi kyam tana kallonsu, fuskarta alamu na rashin gaskiya ya bayyana, ta numfasa dakyar tana mai hadiyar yawu, suka k'araso har inda ta ke, idanunsu k'arara ya nuna alamun 6acin rai, babu ma kamar Ihsan wacce bacci 6arawo ne kadai ya saceta shima cike da mafarke-mafarke.
"Ina kwana..."
Bata kai ga k'arasawa ba ta ji an dauketa da wani zazzafan mari, ta rik'e kuncinta lokaci guda kuma ta saki bokitin hannunta tana duban Ikram fuskarta cike da tsananin damuwa, tuni hawaye sun soma sauka a fuskarta.
"Kinyi kad'an a mareni saboda ke ba kasa tararki na rama wallahi! Ke din banza! Sa'arki daya ma jiya a gaban wadanda suke da daraja aka mareni, da tun jiya na huce. To saidai mu din an koyamana tsayawa iyakar matsayinmu bamu saba ketarewa ba, ke kuwa da alama ba ki samu wannan tarbiyyar ba tunda har ya kasance kinyi tsaurin idon kai kanki inda aka fi karfinki. Banza mai kwadayi."
Ikram ce ke wadannan kalaman tana mai jifanta da wani banzan kallo, ba ta ce uffan ba, ta sa hannu zata dauki bokitin Ihsan ta buge hannun da k'afarta.
"Aiki kuma a gidannan ya k'are miki, sannan ki sa a ranki muddin yau muka isa Kano zamanki a gidanmu ya k'are, sai naga ta inda zaki auri Yaya Faruk din. Banza kawai!"
Ummi da ta kasa dagowa daga durkushen da ta yi, ta runtse idonta cikin jin zafin wannan abu.
"Meke faruwa ne?"
Suka tsinci muryar Hajiya, da sauri suka nutsu kamar ba su ba.
"Bakomai Hajiya, k'arewa Matar Yaya kallo mukeyi."
Cewar Ikram tana dariya ta raini. Hajiya ta daure fuska.
"Ku bar wajen nan tun ban sa6amuku ba."
Suka juya suna gunguni suka koma daki. Hajiya ta zauna saman kujera ta yi shiru tana kallon Ummi dake faman goge ruwan da suka zubar suka 6ata mata guganta, tana yi tana hawaye. Murya na rawa ta gaida Hajiya, Hajiya ta amsa mata. Saida ta kammala sannan ta mik'e da zummar barin wajen, ta dakatar da ita ta hanyar kiranta, jin yanda Hajiya ta kira sunanta da sanyin murya, yasa ta dan ji sauki na rad'ad'i da kuma fargabar da ta cikata. Ta amsa a ladabce tana mai zama a gefe kanta a k'asa.
"Kiyi hakuri Ummi, nasan daman tunda Sadauki ya 6ullo da maganar aurenki, dole irin haka ta faru koma fiye da hakan kafin a samu fahimtar juna. Ni ban ta6a k'in ki a zuciyata ba, haka kuma ina miki kallon mutum kamar kowa mai nata darajar ta daban. Ko yanzu hakurinki yasa kin k'ara samun wani gurbi a zuciyata. Ki sani, ni mai son abinda Sadaukina ke so ne matukar ba abin assha bane don haka kema na yarda da lamarinki da shi. Kar kice kuma zakiyi amfani da wannan damar ki cutar da d'ana, bazan ta6a lamunta ba. Idan kin d'ore a yanda kike yanzun to fa zamu shirya da ke. Sannan Ihsan..."
Sallamar Gogan ya katse Hajiya daga maganarta, suka amsa suna dubansa. Idanunsa shima a kansu da mamaki, musamman ma na ganin yanda abar kaunarsa ke fidda ruwan hawaye saidai bayason cewa wani abu don gaban Hajiya ne, fatansa dai kada Hajiya ce ta sanyata kuka.
Ya karaso cikin shigar kananun kaya wanda ya nuna shaidar ya yi wanka, ya zauna gefen Hajiya yana mai gaisheta, ta amsa fuskarta a dan sake ba kamar jiya ba da ta daure mishi, hakan ya dan sanyamishi nutsuwa. Ummi ta gaisheshi batare da ta dubeshi ba, ya amsa yana bin fuskarta da kallo, yana son ya tambayi dalilin kukanta saidai babu dama.
"Je ki sai na nemeki, kin shirya kayanki?"
Ta gyada kai, Faruk ya yamutsa fuska yana duban Hajiyarsa cikin rashin fahimta, bayan fitar Ummi dauke da bokiti da tsummokarai, ya dubi Hajiya.
"Ina zata?"
"Kano zata koma mana, ko ka manta daga can ta fito?"
Ya daure fuska yana mai kauda kai.
"Idan har a matsayin yar aiki zata je don Allah ayi hakuri Hajiya."
Ya karashe fuskarsa cike da damuwa kwarai. Ta yi shiru tana dubansa, ta gama karantar ba karamin so ya ke yiwa Ummi ba, tasan halin d'anta, wannan magana har cikin zuciyarsa ya ke yinta.
"To yanzu Sadauki za'ayita rike musu ita ne? Karka manta fa kawota akayi Kano aikatau asalinta ba ma'yar garin bace."
Ya lumshe ido kafin ya bude.
"'Yar Ringim ce. Kuyi hakuri har ta cika watanta, idan wacce ta kawota ta zo Kanon, sai aje har Ummin ayiwa mahaifinta bayani don Allah Hajiya. Amma yanzu ba girma kuma ta cigaba da aikatau, a duba wannan lamarin Hajiyata."
Hajiya ta gyada kai cike da gamsuwa.
"Shikenan, na ji zanyi tunani."
Bayan fitarsa daga falon ta rasa ma abin yi, mikewa ta yi ta nufi dakinta. Karshe dai ta yanke hukuncin kiran kanwarta Hajiya Mama, don ita har nauyin Hajiya Madina ta ke d'an ji a yanzu.
Hajiya Mama ta dauka, bayan sun gaisa ta ce. "Sadiya kina jina?"
"Ina jinki Hajiya."
Ta koramata dukkan yanda ake ciki tun daga jiya da Faruk ya zo musu da maganar Ummi har zuwa yanzun da ya ce shi bayason komawarta aikatau Kano. Ta k'ara da fad'in.
"Ki ban shawara Sadiya, kwakwalwata ta cushe, na rasa abinda zanyi, ina kuma jin tsoron Madina ta ji maganarnan daga bakin 'yarta."
Hajiya Mama da ta sandare don mamakin wannan al'mari ta numfasa.
"Allah Mai Iko, wannan shine ana zaton wuta a makera. Karki damu Hajiya, ni banga aibu a aurensa da Ummi ba matukar zai had'a har ita Ihsan din kamar yanda ku ka ce, don bazamu so wannan abu ya kawo matsala a zuri'armu ba. Amma don Allah kamar yanda Genaral ya ce, ku daure kuyi bincike sosai akan Asalin yarinyar nan, Ummi dai a halayya bata da aibu daidai gwargwado yarinyar akwai hakuri da sanin yakamata sannan har gwaje-gwaje ayi ko don gujewa wani abu da zai je ya dawo. Ki kwantar da hankalinki, daman yau zanje saloon, zan fasa idan yaso na sanarwa Alhaji na je gidan Madinan. Allah Ya za6a abinda yafi alheri."
Cike da jin dadin kalamanta Hajiya Babba ta ce.
"Kai da kuwa kinyimin babban taimako wallahi, nagode sosai."
"Haba Hajiya, kina gaba da ni ai kin wuce haka, na tabbatar Madina ba zata kawo matsala ba in sha Allah."
Ta jinjina kai.
"Ina fatan hakan."
A karshe sukayi sallama da zummar duk yanda akayi zata sanarmata.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
73
ABUJA
Misalin takwas na safe, Ummi ta kammala gyara sashen Hajiya duk jikinta a dar-dar, burinta ta yi ta kammala ta bar wajen kafin wani ya risk'eta, saidai cikin rashin sa'a tana murnar har ta kammala za ta tafi ba wanda ya fito, Ihsan ta fito falon tare da Ikram. Daman tun jiya suke dakonta. Tsayawa ta yi kyam tana kallonsu, fuskarta alamu na rashin gaskiya ya bayyana, ta numfasa dakyar tana mai hadiyar yawu, suka k'araso har inda ta ke, idanunsu k'arara ya nuna alamun 6acin rai, babu ma kamar Ihsan wacce bacci 6arawo ne kadai ya saceta shima cike da mafarke-mafarke.
"Ina kwana..."
Bata kai ga k'arasawa ba ta ji an dauketa da wani zazzafan mari, ta rik'e kuncinta lokaci guda kuma ta saki bokitin hannunta tana duban Ikram fuskarta cike da tsananin damuwa, tuni hawaye sun soma sauka a fuskarta.
"Kinyi kad'an a mareni saboda ke ba kasa tararki na rama wallahi! Ke din banza! Sa'arki daya ma jiya a gaban wadanda suke da daraja aka mareni, da tun jiya na huce. To saidai mu din an koyamana tsayawa iyakar matsayinmu bamu saba ketarewa ba, ke kuwa da alama ba ki samu wannan tarbiyyar ba tunda har ya kasance kinyi tsaurin idon kai kanki inda aka fi karfinki. Banza mai kwadayi."
Ikram ce ke wadannan kalaman tana mai jifanta da wani banzan kallo, ba ta ce uffan ba, ta sa hannu zata dauki bokitin Ihsan ta buge hannun da k'afarta.
"Aiki kuma a gidannan ya k'are miki, sannan ki sa a ranki muddin yau muka isa Kano zamanki a gidanmu ya k'are, sai naga ta inda zaki auri Yaya Faruk din. Banza kawai!"
Ummi da ta kasa dagowa daga durkushen da ta yi, ta runtse idonta cikin jin zafin wannan abu.
"Meke faruwa ne?"
Suka tsinci muryar Hajiya, da sauri suka nutsu kamar ba su ba.
"Bakomai Hajiya, k'arewa Matar Yaya kallo mukeyi."
Cewar Ikram tana dariya ta raini. Hajiya ta daure fuska.
"Ku bar wajen nan tun ban sa6amuku ba."
Suka juya suna gunguni suka koma daki. Hajiya ta zauna saman kujera ta yi shiru tana kallon Ummi dake faman goge ruwan da suka zubar suka 6ata mata guganta, tana yi tana hawaye. Murya na rawa ta gaida Hajiya, Hajiya ta amsa mata. Saida ta kammala sannan ta mik'e da zummar barin wajen, ta dakatar da ita ta hanyar kiranta, jin yanda Hajiya ta kira sunanta da sanyin murya, yasa ta dan ji sauki na rad'ad'i da kuma fargabar da ta cikata. Ta amsa a ladabce tana mai zama a gefe kanta a k'asa.
"Kiyi hakuri Ummi, nasan daman tunda Sadauki ya 6ullo da maganar aurenki, dole irin haka ta faru koma fiye da hakan kafin a samu fahimtar juna. Ni ban ta6a k'in ki a zuciyata ba, haka kuma ina miki kallon mutum kamar kowa mai nata darajar ta daban. Ko yanzu hakurinki yasa kin k'ara samun wani gurbi a zuciyata. Ki sani, ni mai son abinda Sadaukina ke so ne matukar ba abin assha bane don haka kema na yarda da lamarinki da shi. Kar kice kuma zakiyi amfani da wannan damar ki cutar da d'ana, bazan ta6a lamunta ba. Idan kin d'ore a yanda kike yanzun to fa zamu shirya da ke. Sannan Ihsan..."
Sallamar Gogan ya katse Hajiya daga maganarta, suka amsa suna dubansa. Idanunsa shima a kansu da mamaki, musamman ma na ganin yanda abar kaunarsa ke fidda ruwan hawaye saidai bayason cewa wani abu don gaban Hajiya ne, fatansa dai kada Hajiya ce ta sanyata kuka.
Ya karaso cikin shigar kananun kaya wanda ya nuna shaidar ya yi wanka, ya zauna gefen Hajiya yana mai gaisheta, ta amsa fuskarta a dan sake ba kamar jiya ba da ta daure mishi, hakan ya dan sanyamishi nutsuwa. Ummi ta gaisheshi batare da ta dubeshi ba, ya amsa yana bin fuskarta da kallo, yana son ya tambayi dalilin kukanta saidai babu dama.
"Je ki sai na nemeki, kin shirya kayanki?"
Ta gyada kai, Faruk ya yamutsa fuska yana duban Hajiyarsa cikin rashin fahimta, bayan fitar Ummi dauke da bokiti da tsummokarai, ya dubi Hajiya.
"Ina zata?"
"Kano zata koma mana, ko ka manta daga can ta fito?"
Ya daure fuska yana mai kauda kai.
"Idan har a matsayin yar aiki zata je don Allah ayi hakuri Hajiya."
Ya karashe fuskarsa cike da damuwa kwarai. Ta yi shiru tana dubansa, ta gama karantar ba karamin so ya ke yiwa Ummi ba, tasan halin d'anta, wannan magana har cikin zuciyarsa ya ke yinta.
"To yanzu Sadauki za'ayita rike musu ita ne? Karka manta fa kawota akayi Kano aikatau asalinta ba ma'yar garin bace."
Ya lumshe ido kafin ya bude.
"'Yar Ringim ce. Kuyi hakuri har ta cika watanta, idan wacce ta kawota ta zo Kanon, sai aje har Ummin ayiwa mahaifinta bayani don Allah Hajiya. Amma yanzu ba girma kuma ta cigaba da aikatau, a duba wannan lamarin Hajiyata."
Hajiya ta gyada kai cike da gamsuwa.
"Shikenan, na ji zanyi tunani."
Bayan fitarsa daga falon ta rasa ma abin yi, mikewa ta yi ta nufi dakinta. Karshe dai ta yanke hukuncin kiran kanwarta Hajiya Mama, don ita har nauyin Hajiya Madina ta ke d'an ji a yanzu.
Hajiya Mama ta dauka, bayan sun gaisa ta ce. "Sadiya kina jina?"
"Ina jinki Hajiya."
Ta koramata dukkan yanda ake ciki tun daga jiya da Faruk ya zo musu da maganar Ummi har zuwa yanzun da ya ce shi bayason komawarta aikatau Kano. Ta k'ara da fad'in.
"Ki ban shawara Sadiya, kwakwalwata ta cushe, na rasa abinda zanyi, ina kuma jin tsoron Madina ta ji maganarnan daga bakin 'yarta."
Hajiya Mama da ta sandare don mamakin wannan al'mari ta numfasa.
"Allah Mai Iko, wannan shine ana zaton wuta a makera. Karki damu Hajiya, ni banga aibu a aurensa da Ummi ba matukar zai had'a har ita Ihsan din kamar yanda ku ka ce, don bazamu so wannan abu ya kawo matsala a zuri'armu ba. Amma don Allah kamar yanda Genaral ya ce, ku daure kuyi bincike sosai akan Asalin yarinyar nan, Ummi dai a halayya bata da aibu daidai gwargwado yarinyar akwai hakuri da sanin yakamata sannan har gwaje-gwaje ayi ko don gujewa wani abu da zai je ya dawo. Ki kwantar da hankalinki, daman yau zanje saloon, zan fasa idan yaso na sanarwa Alhaji na je gidan Madinan. Allah Ya za6a abinda yafi alheri."
Cike da jin dadin kalamanta Hajiya Babba ta ce.
"Kai da kuwa kinyimin babban taimako wallahi, nagode sosai."
"Haba Hajiya, kina gaba da ni ai kin wuce haka, na tabbatar Madina ba zata kawo matsala ba in sha Allah."
Ta jinjina kai.
"Ina fatan hakan."
A karshe sukayi sallama da zummar duk yanda akayi zata sanarmata.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
73