Sashe 43
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*** *** ***
ABUJA
Washegari Faruk da wuri ya tashi kawai don ya ga Umminsa. Ai kuwa yana sanya kai a falon Hajiyarsa na sama ya yi tozali da ita tana aikin shara.
Ta dago kanta jin sallamarsa, ta amsa a hankali sannan ta russuna ta gaisheshi.
"Lafiya, kin tashi lafiya?"
Ta amsa da murmushi dauke saman fuskarta.
"Alhamdulillah."
Ya dubi falon sannan ya dubeta.
"Kai Ummi, duk girman falon nan haka kike share shi? Sannu kinji? Karki damu na wani dan lokaci ne."
Ta dubi hanyar dakunan mutanen gidan, (Hajiya tana sashen mijinta)sannan ta dubeshi cikin murya k'arama ta ce.
"Ka yi hakuri ka kyaleni don Allah kaga a falon Hajiya ne, komai zai iya faruwa."
Ya ta6e baki yana mai gyara tsayuwarsa.
"Ke ni na soma gajiya da wannan tsoron naki, me kike tsoro ne alhalin wataran gidana zasu daukoki su kawo? Kalli,(ya dubi jikinsa sannan ya maida dubansa gareta, ko wanka banyi ba na zo kawai domin na ganki ki ji dadi shi ne kike korata, why?"
Maganar ma ta so bata dariya saidai kasancewar ba a nutse ta ke ba yasa bata dara ba, wato don ta ganshi ta ji dadi?
"Na ganka amma don Allah ka bar..."
Jin motsin murda kofar dakin kwanan su Ikram ne yasa ta saurin juyawa ta cigaba da shara. Ihsan din ce ta fito daga ita sai riga iyaka gwuiwa da dogon wando (cotton) na bacci. Kanta ko hula babu, Faruk ya juyo yana dubanta. Ta karemishi kallo daga shi sai dogon wando na bacci da singilet, yana tsaye hannuwansa cikin aljihun wandon, ya kauda kansa daga gareta, ta fito cike da mamakin abinda ya kawoshi da safe bayan ta riga tasan baya fitowa sai ya yi wanka ya shirya, ta kai dubanta ga Ummi, shara take yi abinta, babu wani abu da ta gani wanda zai sa ta tsargu cewar akwai wata a k'asa, saidai zuciyarta ta kasa nutsuwa akan ganin da ta yi mishi tsaye kuma shi kadai tare da Ummi.
A sanyaye ta gaisheshi, ya gyada kai, daga haka ya juya ya fice. Ta bishi da kallo kafin ta dubi Ummi wacce ta yi kamar batasan wainar da suke toyawa ba. Karasawa ta yi ta tsaya a gabanta tana mai take tsintsiyar, Ummi abin ya bata haushi, ji ta ke kamar ta tureta ta fadi k'as. Saidai a fili bata nuna komai ba, ta dago ta dubeta fuskarta ba walwala babu kuma fushi. Ihsan ta watsamata kallon tsana don ta lura yarinyar kamar ta k'ara gogewa a yan kwanakin da ta yi a Abuja.
"Tun yaushe Yaya Faruk ya shigo?"
Abin ya so bawa Ummi dariya, ta barwa cikinta.
"Yana zuwa kika fito falon."
Ihsan ta dan yi sakato tana dubanta kamar dai bata yarda ba don jikinta ya bata akwai wani abun, sai kuma ta ja tsaki.
"Koma dai menene, mutum ya kiyaye yasan matsayinsa."
Ummi ta dan rausaya kai.
"To me ya kawo wannan maganar kuma?"
Cike da mamaki Ihsan ta dubeta.
"Eh lallai, har anzo ga6ar da zan fadi magana ki tuhumeni akanta? Lallai wuyanki ya soma kauri."
'Tukunna ma dai Ihsan, matukar zaki cigaba da gasamin magana za kico karo da fin haka.'
A fili kuwa ta ce. "Allah Ya baki hakuri."
Wawan tsaki ta ja ta yi gaba ta zauna saman kujera gami da kunna talabijin, daman abinda ya fito da ita kenan, kallon wani(series)na 'yan Philippines wanda bata samun kallo da dare sai karfe takwas na safe suke maimaicin sati duk ranar lahadi.
Ummi murmushi kawai ta yi sannan ta cigaba da shararta zuciyarta wasai.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
59
Ta daure ta 6oye razanar da ta yi, ta amsa mata. Karasowa ta yi tana mai zaro ido.
"Ke Ummi yau asirinki dai ya tonu, ashe kema 'yar hannu ce, naga ma kusan kin fi Sa'ade sa'a don kuwa ke kamun babban goro kikayi."
Ummi da ta rasa meke mata dadi a duniya ta cigaba da kallonta tana ji kamar ta saki fitsari.
"Me..me..kike so ki ce?"
Binta ta yi dariya kadan lokacin da ta zauna tana mai sa hannu ta janyo ledar.
"Eh lallai dole ki rude, ki kwantar da hankalinki ki ci arziki, ai ni idan har za ki dunga yagamin abinda kika samo to fa kar kiji komai don ba ko da matsala da ni. Ki bi sannu dai da mutan gidan da su Bala(mai kula da shukoki), su ne abin ji."
Ta fiddo meatpie ta gutsira. Ummi dai banda innalillahi babu abinda take fada a ranta, Binta ta ganota saidai ta to musu mugun fassara, to daman ina zata aminta cewar soyayya na tafi tsakani da Allah, namiji kamar Faruk zaiyi mata?
"Wallahi babu makamanciyar abinda ki ke zargi tsakanina da Yaya Faruk."
Binta tana taunar meatpie ta watsamata harara.
"Wai kina zaton ban ganku sadda ku ka shiga wajen wanka ba? Haba Ummi, wannan ba abin rufemin bane, nifa makwafciyarki ce, idan ban rufamiki asiri ba wa zai rufa? Tun yaushe ya soma nemanki?"
Ran Ummi idan ya yi dubu to ya 6aci don jin wannan mummunan zaton da Binta ta yi mata.
"Ina miki rantsuwa da Allah abinda kike tsammani tsakanina da Yaya Faruk ba haka bane."
Binta ta yi sakato.
"To menene? A banza zai kawowa 'yar aiki kayayyaki har haka batare da cewa yana da buk'ata akanki ba? Haba Ummi, ko kunnuwana sun kai dubu bafa zan yarda da abinda ki ke fad'a ba. Kedai ki saki jiki kawai arziki ne ya zo miki, idan ma kin ci sa'a nan gaba ya daga darajarki a gidannan."
Ummi ta runtse ido, ta fahimci Binta ta yi nisa cikin zargin abinda ba haka ba. Bai kuma kamata ta barta da wannan bahagon tunanin ba.
"Tsaya ki ji gaskiyar magana, amma don Allah ki rufamin sirrina."
Binta ta tsaya tana dubanta.
"Karki damu, ki saki jiki ki sanarmin, wallahi zan bar zancen a tsakaninmu."
Ummi ta kwashe abinda ke faruwa ta sanarmata. Binta wacce ta daskare awajen ta kasa ko kwakkwarar magana, mamaki ne ya cikata kwarai dagaske, ba don ya ganewa idanunta ba da sai ta iya karyata Ummi nan take, saidai kuma har zuciyarta ta aminta da hakan. Ta cigaba da karewa Ummi kallo, ba k'arya tana da kyawun gani a yaba kuma a so, amma abin mamakin, akwai fiye da ita masu son Faruk saidai wai ace basu isheshi kallo ba sai ita?
Ummi duk ta k'ara tsorata ganin irin kallon da Binta ke bin ta da shi, ga dukkan alamu bata yarda da zancenta ba ne. Wannan yasa ta kara riko hannunta.
"Wallahi iyakar gaskiyar kenan, na gayamaki banda wannan babu abinda ke tsakaninmu, na rasa kuma yanda zanyi ya bar shiga harkata."
Binta ta jinjina kai gami da sauke ajiyar zuciya.
"Tab! Babbar magana. Amma kin kusa kiyi wauta wallahi Ummi, da ace ni na samu wannan damar da babu ta yanda zanyi watsi da ita. Aure fa Ummi? Auren ma da matashi irin Yalla6ai Faruk? Gaskiya ki sake tunani, ki cire tsoro kamar yanda yace din ki tabbatar kin ba shi goyon baya. Karki damu ni don na rufamiki wannan asirin to ba komai ba ne wallahi. Idan ma na ce zan tona ai na shiga uku don nasan nima korata zaayi."
Ta karashe da dariya, Ummi kuwa ta murmusa, hankalinta ya kwanta kadan.
Ta dibarmata kusan rabin kayan sannan Binta ta fice zuwa dakinta bayan ta kara jaddada mata akan kada ta sake ta bari wannan dama ta kufcemata. Ummi da to kawai ta bita.
Ihsan tunda ta ji abinda Faruk ya ce wa Dakta hankalinta ya tashi, ji ta ke kamar ta yi tsuntsuwa ta je sashensa ta ganewa idonta ko dagaske ne. Wai ashe dai yana da budurwa wacce ya ke so ta ke zaman jiran gawon shanu? Sam bazai yiwu ba! Sai a yau ta ji tana son bin shawarar Ikram, wato ta sanarwa Faruk yanda ta ke jinsa a ranta. Ta numfasa.
'Shi kadai ne mafita.' Ta ayyana hakan a zuciyarta.
Mintuna biyar da haka, sai ga shi ya shigo falon. Suka dubeshi. Haidar ya ce. "Ina shirin bin sahu na ga 'yar gidan taka sai kuma gakanan."
Faruk wanda tun shigowarsa ya ke murmushi ya zauna a saman kafet kusa da kafafun Babban Yaya, hannu yasa ya dauki ayaba guda cikin wanda suke ci.
"Yanzu Dakta saida ka tonamin?"
"Ana 6oye abin farinciki ne?" Cewar Dakta. Ya girgiza kai yana 'yar dariya.
"Yanzu fa na soma yak'in, ban kai ga cin nasara ba."
Sukayi dariya gaba daya har Ikram, Ihsan ji ta ke yi tamkar ta fashe. Gaba dayansu sun yarda don tunda suke da kaninnasu basu ta6a jin ya yi musu zancen kowace mace ba sai a yau din.
"Dariyar me akeyi?" Fadin Daddy wanda shigowarsa gidan kenan daga waje, ya yi bak'o. Bayan ya karaso ya zauna suka dubeshi. Babban Yaya ne ya soma magana.
"Daddy kaninmu ya samo maka suruka fa."
Da mamaki ya dubi Faruk wanda banda murmushi da taunar ayaba babu abinda ya ke yi.
"Dagaske?"
Faruk bai amsa ba. Daddy ya ji dadi a ransa.
"Kai Masha Allah, na ji dadin wannan lamari. Ai gwara ka soma shirin auren kafin na yi maka na dole."
Aka dara, Daddy ba ruwansa matukar yana da lokaci yakan zauna da iyalinsa suyi hira da dariya. Hajiya Babba ta sauko itama tare da wata budurwa da uwarta ta aiko daukar mata mayafai, bayan ta sallameta ta dawo wajensu, alokacin Ihsan ta sulale ta bar falon don tsabar takaici. Nan itama aka fesamata, murmushi kawai ta yi tare da addu'ar nemawa danta za6in Allah. Daga nan kuma hira ta 6arke, Ikram tuni ta ankara babu Ihsan a falon hakan yasa ta bi bayanta.
A can karshen gadonsu ta risketa ta sanya kanta cikin filo tana kuka har da sheshshek'a. Ta karasa ta zauna a gefenta.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
ABUJA
Washegari Faruk da wuri ya tashi kawai don ya ga Umminsa. Ai kuwa yana sanya kai a falon Hajiyarsa na sama ya yi tozali da ita tana aikin shara.
Ta dago kanta jin sallamarsa, ta amsa a hankali sannan ta russuna ta gaisheshi.
"Lafiya, kin tashi lafiya?"
Ta amsa da murmushi dauke saman fuskarta.
"Alhamdulillah."
Ya dubi falon sannan ya dubeta.
"Kai Ummi, duk girman falon nan haka kike share shi? Sannu kinji? Karki damu na wani dan lokaci ne."
Ta dubi hanyar dakunan mutanen gidan, (Hajiya tana sashen mijinta)sannan ta dubeshi cikin murya k'arama ta ce.
"Ka yi hakuri ka kyaleni don Allah kaga a falon Hajiya ne, komai zai iya faruwa."
Ya ta6e baki yana mai gyara tsayuwarsa.
"Ke ni na soma gajiya da wannan tsoron naki, me kike tsoro ne alhalin wataran gidana zasu daukoki su kawo? Kalli,(ya dubi jikinsa sannan ya maida dubansa gareta, ko wanka banyi ba na zo kawai domin na ganki ki ji dadi shi ne kike korata, why?"
Maganar ma ta so bata dariya saidai kasancewar ba a nutse ta ke ba yasa bata dara ba, wato don ta ganshi ta ji dadi?
"Na ganka amma don Allah ka bar..."
Jin motsin murda kofar dakin kwanan su Ikram ne yasa ta saurin juyawa ta cigaba da shara. Ihsan din ce ta fito daga ita sai riga iyaka gwuiwa da dogon wando (cotton) na bacci. Kanta ko hula babu, Faruk ya juyo yana dubanta. Ta karemishi kallo daga shi sai dogon wando na bacci da singilet, yana tsaye hannuwansa cikin aljihun wandon, ya kauda kansa daga gareta, ta fito cike da mamakin abinda ya kawoshi da safe bayan ta riga tasan baya fitowa sai ya yi wanka ya shirya, ta kai dubanta ga Ummi, shara take yi abinta, babu wani abu da ta gani wanda zai sa ta tsargu cewar akwai wata a k'asa, saidai zuciyarta ta kasa nutsuwa akan ganin da ta yi mishi tsaye kuma shi kadai tare da Ummi.
A sanyaye ta gaisheshi, ya gyada kai, daga haka ya juya ya fice. Ta bishi da kallo kafin ta dubi Ummi wacce ta yi kamar batasan wainar da suke toyawa ba. Karasawa ta yi ta tsaya a gabanta tana mai take tsintsiyar, Ummi abin ya bata haushi, ji ta ke kamar ta tureta ta fadi k'as. Saidai a fili bata nuna komai ba, ta dago ta dubeta fuskarta ba walwala babu kuma fushi. Ihsan ta watsamata kallon tsana don ta lura yarinyar kamar ta k'ara gogewa a yan kwanakin da ta yi a Abuja.
"Tun yaushe Yaya Faruk ya shigo?"
Abin ya so bawa Ummi dariya, ta barwa cikinta.
"Yana zuwa kika fito falon."
Ihsan ta dan yi sakato tana dubanta kamar dai bata yarda ba don jikinta ya bata akwai wani abun, sai kuma ta ja tsaki.
"Koma dai menene, mutum ya kiyaye yasan matsayinsa."
Ummi ta dan rausaya kai.
"To me ya kawo wannan maganar kuma?"
Cike da mamaki Ihsan ta dubeta.
"Eh lallai, har anzo ga6ar da zan fadi magana ki tuhumeni akanta? Lallai wuyanki ya soma kauri."
'Tukunna ma dai Ihsan, matukar zaki cigaba da gasamin magana za kico karo da fin haka.'
A fili kuwa ta ce. "Allah Ya baki hakuri."
Wawan tsaki ta ja ta yi gaba ta zauna saman kujera gami da kunna talabijin, daman abinda ya fito da ita kenan, kallon wani(series)na 'yan Philippines wanda bata samun kallo da dare sai karfe takwas na safe suke maimaicin sati duk ranar lahadi.
Ummi murmushi kawai ta yi sannan ta cigaba da shararta zuciyarta wasai.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
59
Ta daure ta 6oye razanar da ta yi, ta amsa mata. Karasowa ta yi tana mai zaro ido.
"Ke Ummi yau asirinki dai ya tonu, ashe kema 'yar hannu ce, naga ma kusan kin fi Sa'ade sa'a don kuwa ke kamun babban goro kikayi."
Ummi da ta rasa meke mata dadi a duniya ta cigaba da kallonta tana ji kamar ta saki fitsari.
"Me..me..kike so ki ce?"
Binta ta yi dariya kadan lokacin da ta zauna tana mai sa hannu ta janyo ledar.
"Eh lallai dole ki rude, ki kwantar da hankalinki ki ci arziki, ai ni idan har za ki dunga yagamin abinda kika samo to fa kar kiji komai don ba ko da matsala da ni. Ki bi sannu dai da mutan gidan da su Bala(mai kula da shukoki), su ne abin ji."
Ta fiddo meatpie ta gutsira. Ummi dai banda innalillahi babu abinda take fada a ranta, Binta ta ganota saidai ta to musu mugun fassara, to daman ina zata aminta cewar soyayya na tafi tsakani da Allah, namiji kamar Faruk zaiyi mata?
"Wallahi babu makamanciyar abinda ki ke zargi tsakanina da Yaya Faruk."
Binta tana taunar meatpie ta watsamata harara.
"Wai kina zaton ban ganku sadda ku ka shiga wajen wanka ba? Haba Ummi, wannan ba abin rufemin bane, nifa makwafciyarki ce, idan ban rufamiki asiri ba wa zai rufa? Tun yaushe ya soma nemanki?"
Ran Ummi idan ya yi dubu to ya 6aci don jin wannan mummunan zaton da Binta ta yi mata.
"Ina miki rantsuwa da Allah abinda kike tsammani tsakanina da Yaya Faruk ba haka bane."
Binta ta yi sakato.
"To menene? A banza zai kawowa 'yar aiki kayayyaki har haka batare da cewa yana da buk'ata akanki ba? Haba Ummi, ko kunnuwana sun kai dubu bafa zan yarda da abinda ki ke fad'a ba. Kedai ki saki jiki kawai arziki ne ya zo miki, idan ma kin ci sa'a nan gaba ya daga darajarki a gidannan."
Ummi ta runtse ido, ta fahimci Binta ta yi nisa cikin zargin abinda ba haka ba. Bai kuma kamata ta barta da wannan bahagon tunanin ba.
"Tsaya ki ji gaskiyar magana, amma don Allah ki rufamin sirrina."
Binta ta tsaya tana dubanta.
"Karki damu, ki saki jiki ki sanarmin, wallahi zan bar zancen a tsakaninmu."
Ummi ta kwashe abinda ke faruwa ta sanarmata. Binta wacce ta daskare awajen ta kasa ko kwakkwarar magana, mamaki ne ya cikata kwarai dagaske, ba don ya ganewa idanunta ba da sai ta iya karyata Ummi nan take, saidai kuma har zuciyarta ta aminta da hakan. Ta cigaba da karewa Ummi kallo, ba k'arya tana da kyawun gani a yaba kuma a so, amma abin mamakin, akwai fiye da ita masu son Faruk saidai wai ace basu isheshi kallo ba sai ita?
Ummi duk ta k'ara tsorata ganin irin kallon da Binta ke bin ta da shi, ga dukkan alamu bata yarda da zancenta ba ne. Wannan yasa ta kara riko hannunta.
"Wallahi iyakar gaskiyar kenan, na gayamaki banda wannan babu abinda ke tsakaninmu, na rasa kuma yanda zanyi ya bar shiga harkata."
Binta ta jinjina kai gami da sauke ajiyar zuciya.
"Tab! Babbar magana. Amma kin kusa kiyi wauta wallahi Ummi, da ace ni na samu wannan damar da babu ta yanda zanyi watsi da ita. Aure fa Ummi? Auren ma da matashi irin Yalla6ai Faruk? Gaskiya ki sake tunani, ki cire tsoro kamar yanda yace din ki tabbatar kin ba shi goyon baya. Karki damu ni don na rufamiki wannan asirin to ba komai ba ne wallahi. Idan ma na ce zan tona ai na shiga uku don nasan nima korata zaayi."
Ta karashe da dariya, Ummi kuwa ta murmusa, hankalinta ya kwanta kadan.
Ta dibarmata kusan rabin kayan sannan Binta ta fice zuwa dakinta bayan ta kara jaddada mata akan kada ta sake ta bari wannan dama ta kufcemata. Ummi da to kawai ta bita.
Ihsan tunda ta ji abinda Faruk ya ce wa Dakta hankalinta ya tashi, ji ta ke kamar ta yi tsuntsuwa ta je sashensa ta ganewa idonta ko dagaske ne. Wai ashe dai yana da budurwa wacce ya ke so ta ke zaman jiran gawon shanu? Sam bazai yiwu ba! Sai a yau ta ji tana son bin shawarar Ikram, wato ta sanarwa Faruk yanda ta ke jinsa a ranta. Ta numfasa.
'Shi kadai ne mafita.' Ta ayyana hakan a zuciyarta.
Mintuna biyar da haka, sai ga shi ya shigo falon. Suka dubeshi. Haidar ya ce. "Ina shirin bin sahu na ga 'yar gidan taka sai kuma gakanan."
Faruk wanda tun shigowarsa ya ke murmushi ya zauna a saman kafet kusa da kafafun Babban Yaya, hannu yasa ya dauki ayaba guda cikin wanda suke ci.
"Yanzu Dakta saida ka tonamin?"
"Ana 6oye abin farinciki ne?" Cewar Dakta. Ya girgiza kai yana 'yar dariya.
"Yanzu fa na soma yak'in, ban kai ga cin nasara ba."
Sukayi dariya gaba daya har Ikram, Ihsan ji ta ke yi tamkar ta fashe. Gaba dayansu sun yarda don tunda suke da kaninnasu basu ta6a jin ya yi musu zancen kowace mace ba sai a yau din.
"Dariyar me akeyi?" Fadin Daddy wanda shigowarsa gidan kenan daga waje, ya yi bak'o. Bayan ya karaso ya zauna suka dubeshi. Babban Yaya ne ya soma magana.
"Daddy kaninmu ya samo maka suruka fa."
Da mamaki ya dubi Faruk wanda banda murmushi da taunar ayaba babu abinda ya ke yi.
"Dagaske?"
Faruk bai amsa ba. Daddy ya ji dadi a ransa.
"Kai Masha Allah, na ji dadin wannan lamari. Ai gwara ka soma shirin auren kafin na yi maka na dole."
Aka dara, Daddy ba ruwansa matukar yana da lokaci yakan zauna da iyalinsa suyi hira da dariya. Hajiya Babba ta sauko itama tare da wata budurwa da uwarta ta aiko daukar mata mayafai, bayan ta sallameta ta dawo wajensu, alokacin Ihsan ta sulale ta bar falon don tsabar takaici. Nan itama aka fesamata, murmushi kawai ta yi tare da addu'ar nemawa danta za6in Allah. Daga nan kuma hira ta 6arke, Ikram tuni ta ankara babu Ihsan a falon hakan yasa ta bi bayanta.
A can karshen gadonsu ta risketa ta sanya kanta cikin filo tana kuka har da sheshshek'a. Ta karasa ta zauna a gefenta.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR