Sashe 47
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Munira tana zaune ta kurawa talabijin ido, saidai gaba daya hankalinta baya tare da kallon, Tasleem da Haris sai wasa da keke sukeyi ko kusa basu da wata matsala. Babban damuwarta bai wuce na auren da Deen ya sanarmata zaiyi ba da macen da sai su share awanni uku cikin dare suna waya, har yau batasan wacece ba saidai babu irin cin kashin da bata gani daga gurinsa tun soma soyayyarsa da yarinyar. Tunaninta ya katse sa'ilin da wayarta ta dauki k'ara. Ganin lambar yar uwarta Atika mai aure a Ringim yasa ta rage k'arar talabijin gami da dauka. Bayan sallama ko gaisawa Atika bata bari sunyi ba ta soma magana.
"Wai kuwa Munira kinsan abinda ke shirin samunki kuwa?"
Munira ta kara gyara zamanta kafin ta saki murmushi mai ciwo.
"Na sani Yaya, to ya zanyi? Aure kaddara ce ai, shi ya sani."
Atika ta saka salati.
"Ikon Allah, oh ni Fatima, ba dai kema sun shanyeki kamar yanda suka shanye Deenin ba? Wallahi na tausayawa rayuwarki Munira, cab!"
Munira ta ji gabanta na dukan tara-tara. Daman ya lafiyar giwa....
"Yaya wai me kikeson cewa? Ko kina da labarin wacce zai aura ne? Ni wallahi nan da kike gani ko sunanta bazan iya kawomiki ba don a Yanzu bai daukeni wata abar ba yanzu ballantana ya sanarmin."
"To wallahi Munira bacci bai ganmu ba, tashi tsaye ya dace muyi da addu'a, Deeni ba kowace zai aura ba face Dijar Baba Yahuza."
Jin zancen ta yi tamkar saukar aradu, wani salati ta saka da karfi kafin kuma ta yi wurgi da wayar ta zube anan ta hau kuka.
A guje yaranta suka yo kanta tare da Asiya mai tayata aiki.
"Lafiya Hajiya?"
Ta kasa barwa cikinta, ta sanarwa Asiya matsalar da ta ke ciki yanzun. Asiya ita kanta hankalinta ya tashi ainun, daman ta zargi hakan tsakanin Dija da Oga, ita take ganin yanayin muamalarsu a gidan. Ta yi ta bawa Munira hakuri, karshe dai ganin yaranta sun shiga damuwa ta mike ta dauki wayarta da ke faman ruri ta yi daki. Atika ce, nan ta shiga bata baki da nunamata addua kadai ce mafita
"Yaya ai ni na hakura da zama da Deen ma."
"Me kenan kikayi idan kinyi hakan Munira? Ashe ma ta ci galaba kenan, kada ki soma wannan bahagon tunanin."
Daga haka sukayi sallama. Munira ta cigaba da kuka har ta gode Allah, lallai DAN ADAM butulu ne, kayi mishi alheri ya sakamaka da sharri, ko a mafarki bata ta6a hangen haka ga Dija ba, bata ta6a kawowa zata ci amanarta har haka ba. Wannan rayuwa da me ta yi kama?
Ta jima cikin wannan hali har dawowar Deen daga wurin aiki bata iya komai ba. Daman ba wani nemanta ya ke yi ba yanzun, taso zuwa ta sameshi saidai kuma ta ga rashin alfanun hakan. Wannan yasa ta zuba ido ganin yanda lamuran zasu cigaba da kasancewa, mik'awa Allah lamarin shi yafi kamar dai yanda Yayarta ta ce.
*** *** ***
ABUJA
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
64
ABUJA
Intisar sanye cikin riga doguwa 'yar kanti, ta ci kwalliyarta daidai misali ta fito daga kicin dauke da kwanukan abinci ta jera saman tebur inda Haidar da Faruk ke zaune. Ta gaida Faruk ya amsa shima ya gaisheta. Abin ma ya basu dariya.
"Ba dariya, matar yaya ta ke ai."
Haidar ya harareshi da wasa.
"Sai yanzu ka sani?"
Dariya kawai ya yi, Intisar dai bata saba irin wasan da Faruk ba don bai fiye sakarmusu ba, murmushi kawai ta danyi. Bayan ta gama(serving) dinsu ta bar wajen. Saida suka kammala ci sannan suka wuce masallaci bayan dawowarsu ne suka zauna a falon Haidar. Haidar ya dora kafa daya kan daya.
"Ina sauraronka."
Faruk ya mik'a mishi waya. Haidar ya kar6a yana kallo, ido waje kuma ya ke kallonsa.
"Wannan kamar Ummi yar aikin Mami."
Faruk cikin jin zafin yar aikin da ya kirata ya jinjina kai.
"Yes itace, a wurina ba 'yar aiki bace, budurwar da nake shirin aure ce, ita kuma nake son ta zama surukarku."
"Kasan abinda ka ke cewa kuwa?"
"Kwarai kuwa, Ummi nake so da aure."
Haidar ya dan yi jim kafin ya girgiza kai cikin sauyin yanayi,
"Bazai yiwu ba."
"Saboda ita ba mutum ba ce?"
Faruk ya jefamishi tambayar rai a 6ace.
Haidar ya dafa kafadarsa.
"Cool down mana, ba nufina wai wani abin daban ba, saidai matsayinku ya bambanta, wannan abu ba mai yiwuwa bane, ka chanja tunani Faruk, da kamar wuya su Daddy su yarjemaka."
Faruk ya murtuk'e fuska.
"Haka kake gani?"
Haidar da mamaki ya ke kallonsa.
"Kai baka gani?"
Ya girgiza kai gami da kwantar da kai jikin kujera.
"Ban ta6a hangen hakan ba, ban kuma sani ba ko don na riga na yi nisa a kaunarta ne yasa ban gano ba? Ni yanzu kai na zo ka ban shawarar wanda ya dace na soma tunkara tsakanin Hajiyarmu da Daddy?"
Haidar ya shafi goshinsa yana kara duban hoton Ummi sannan ya dubi Faruk.
"Ka sanarwa dukkansu alokaci guda. Ni a raayina, banga aibu a auren Ummi ba, na lura yarinya ce nutsastsiya sannan tana da kyawun hali da na fuska. Matsalar dai iyayenmu, idan sun amince shikenan, bansan raayin Babban Yaya da Dakta ba."
Faruk ya dan ta6e baki.
"Nifa zan zauna da ita. Shawara kawai daman na zo nema awajenka, ka kuma tayani adduar samun nasara akansu."
Haidar ya gyada kai yana dan murmushi.
"In sha Allahu, mai Ummi, zan tayaka. Amma wacece H din da ka zana?"
Faruk ya dan dara gami da kashe ido daya.
"Hasiya, real name dinta ne. Sunan mum dinta ta ci, amman ta rasu yanzu."
"Kai Nawan." Cewar Haidar gami da ba shi hannu suka cafke kamar wasu abokai.
"Wato komai nata ka sani? Duk ta yaya?"
Faruk ya gutsira mishi labarin Ummi, ya dora da fadin.
"Tausayinta ne ya soma rinjayar zuciyata har na soma jin sonta a raina."
Shi kansa Haidar ya tausayamata.
"Allah Sarki, rayuwa kenan, kowa da inda Allah Ya ajiyeshi, babu wanda yafi wani a wajenSa sai wanda yafi tsoronShi. Allah dai Ya datar da mu."
"Ameen broda. Ni bari na k'arasa, waya nakeson zuwa na siyo."
"Na wa kenan?"
Murmushi Faruk ya yi, Haidar ya dafa kafadarsa yana tayashi murmushin.
"Lallai na yarda da Dakta ke cewa irinku da bakwa soyayya idan kun tashi yi to zakuyi mai ban mamaki."
Abin ma sai ya bawa Faruk dariya, har wajen mota ya rakashi sannan sukayi sallama da zummar duk yanda Faruk sukayi da iyayen zai sanarmishi.
Hajiya Babba ta ajiye wayarta a gefe bayan ta gama amsawa ta dubi Ikram wacce ke zaman jiranta ta kammala.
"Ina jinki."
Ikram ta yi gyaran murya ta soma magana.
"Hajiya daman akan Ihsan ne."
Cike da mamaki ta dubeta.
"Meyafaru da Ihsan din? Ko ta gaji da mu ne?"
"A'a, daman..." (Ta kwashe tun farkon sadda Ihsan ta soma son Faruk har zuwa jiya da ta shiryamishi party na taya murnar ranar haihuwa.
Hajiya Babba bayan gama sauraronta ta numfasa fuskarta dauke da damuwa.
"Tun ba yau ba nasan yarinyarnan tana son Sadauki, saidai banga alamun Sadauki yana sonta ba."
Ikram itama ta jinjina kai, tasan gaskiya ne.
"Amma Hajiya bakya ganin a haka ya aureta idan yaso son ya shiga a hankali?"
"Kina ganin zai yarda? Banason abinda za'a zo zumunci ya lalace, matukar akayi aure ba da son ran daya ba to shakka babu zai shafi zumuncinmu abinda bazan ta6a fatan naga ranarsa ba kenan."
Ikram ta yi mamakin abinda Hajiyarsu ta ce, duk da tasan gaskiya ne, amma ai ya dace ta duba alak'a. Ita shaida ce akan yanda Hajiya ke tsananin kaunar dannata, batasan 6acin ransa tun yana karami kamar yanda ta samu labari daga yayyunsu. Ta bude baki zatayi magana Hajiya ta dagamata hannu.
"Ya isa hakanan, sai naji ta bakinsa, banason yi mishi katsalanda a lamari irin haka. Musamman lamari irin wannan na aure."
Jiki a sanyaye Ikram ta mike zata fita daga dakin, ta dakatar da ita.
"Maganar ta tsaya iyaka nan, ban yarje miki sanarwa Ihsan ba."
Ikram da ta rasa bakin magana, kai kawai ta gyada sannan ta fice har lokacin mamakin Hajiyarsu bai saketa ba, ko babu komai naka ai naka ne, saidai batasan hukuncin da zata yanke ba.
Mintuna k'alilan da yin hakan, Faruk ya dawo gidan a gajiye, kai tsaye sashensa ya nufa ya yi wanka ya sanya doguwar jallabiya ruwan madara da wando kafin ya dauki wayar da ya siyowa Ummi na kamfanin HTC ya sanyata a chaji. A karshe ya nufi sashen Daddy.
Acan ya iske Hajiya, suka gaisa kafin su shiga hira da iyayennasa. Can Daddy ya dubeshi.
"Son shekarunka talatin a duniya, ya ci ace zuwa yanzu ka soma tunanin aure."
"Ai ina jin ya samu matar aure, bai kai da fad'amana wacece ba ko Sadaukina?"
Murmushi ya yi yana mai shafar sumar kansa.
"A ina take?" Fadin Daddy kenan yana mai gyara zamansa don yasan dagasken ne don dannasu koda wasa bai ta6a zancen kowace mace ba.
"Ba ta yi nisa da mu ba sosai Daddy."
Hajiya da Daddy suka dubi juna, kafin su dubeshi.
"Ko 'yar gidan Alhaji Hamza? (Makwafcinsu)"
Ya yamutsa fuska.
"A'a, asalima ita ba 'yar garin nan bace."
"Wacece kenan?" Hajiya ta tambaya.
Ya yi shiru can kuma ya sunkuyar da kai.
"Zan kawomuku ita ku ganta cikin satinnan In sha Allah."
Suka gyada kai lokaci guda.
"Allah Ya kaimu." Fadin Daddy. Faruk da Hajiya suka amsa da amin, ita kuwa Hajiya ta soma tunanin kodai Ihsan ce?
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
"Wai kuwa Munira kinsan abinda ke shirin samunki kuwa?"
Munira ta kara gyara zamanta kafin ta saki murmushi mai ciwo.
"Na sani Yaya, to ya zanyi? Aure kaddara ce ai, shi ya sani."
Atika ta saka salati.
"Ikon Allah, oh ni Fatima, ba dai kema sun shanyeki kamar yanda suka shanye Deenin ba? Wallahi na tausayawa rayuwarki Munira, cab!"
Munira ta ji gabanta na dukan tara-tara. Daman ya lafiyar giwa....
"Yaya wai me kikeson cewa? Ko kina da labarin wacce zai aura ne? Ni wallahi nan da kike gani ko sunanta bazan iya kawomiki ba don a Yanzu bai daukeni wata abar ba yanzu ballantana ya sanarmin."
"To wallahi Munira bacci bai ganmu ba, tashi tsaye ya dace muyi da addu'a, Deeni ba kowace zai aura ba face Dijar Baba Yahuza."
Jin zancen ta yi tamkar saukar aradu, wani salati ta saka da karfi kafin kuma ta yi wurgi da wayar ta zube anan ta hau kuka.
A guje yaranta suka yo kanta tare da Asiya mai tayata aiki.
"Lafiya Hajiya?"
Ta kasa barwa cikinta, ta sanarwa Asiya matsalar da ta ke ciki yanzun. Asiya ita kanta hankalinta ya tashi ainun, daman ta zargi hakan tsakanin Dija da Oga, ita take ganin yanayin muamalarsu a gidan. Ta yi ta bawa Munira hakuri, karshe dai ganin yaranta sun shiga damuwa ta mike ta dauki wayarta da ke faman ruri ta yi daki. Atika ce, nan ta shiga bata baki da nunamata addua kadai ce mafita
"Yaya ai ni na hakura da zama da Deen ma."
"Me kenan kikayi idan kinyi hakan Munira? Ashe ma ta ci galaba kenan, kada ki soma wannan bahagon tunanin."
Daga haka sukayi sallama. Munira ta cigaba da kuka har ta gode Allah, lallai DAN ADAM butulu ne, kayi mishi alheri ya sakamaka da sharri, ko a mafarki bata ta6a hangen haka ga Dija ba, bata ta6a kawowa zata ci amanarta har haka ba. Wannan rayuwa da me ta yi kama?
Ta jima cikin wannan hali har dawowar Deen daga wurin aiki bata iya komai ba. Daman ba wani nemanta ya ke yi ba yanzun, taso zuwa ta sameshi saidai kuma ta ga rashin alfanun hakan. Wannan yasa ta zuba ido ganin yanda lamuran zasu cigaba da kasancewa, mik'awa Allah lamarin shi yafi kamar dai yanda Yayarta ta ce.
*** *** ***
ABUJA
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
64
ABUJA
Intisar sanye cikin riga doguwa 'yar kanti, ta ci kwalliyarta daidai misali ta fito daga kicin dauke da kwanukan abinci ta jera saman tebur inda Haidar da Faruk ke zaune. Ta gaida Faruk ya amsa shima ya gaisheta. Abin ma ya basu dariya.
"Ba dariya, matar yaya ta ke ai."
Haidar ya harareshi da wasa.
"Sai yanzu ka sani?"
Dariya kawai ya yi, Intisar dai bata saba irin wasan da Faruk ba don bai fiye sakarmusu ba, murmushi kawai ta danyi. Bayan ta gama(serving) dinsu ta bar wajen. Saida suka kammala ci sannan suka wuce masallaci bayan dawowarsu ne suka zauna a falon Haidar. Haidar ya dora kafa daya kan daya.
"Ina sauraronka."
Faruk ya mik'a mishi waya. Haidar ya kar6a yana kallo, ido waje kuma ya ke kallonsa.
"Wannan kamar Ummi yar aikin Mami."
Faruk cikin jin zafin yar aikin da ya kirata ya jinjina kai.
"Yes itace, a wurina ba 'yar aiki bace, budurwar da nake shirin aure ce, ita kuma nake son ta zama surukarku."
"Kasan abinda ka ke cewa kuwa?"
"Kwarai kuwa, Ummi nake so da aure."
Haidar ya dan yi jim kafin ya girgiza kai cikin sauyin yanayi,
"Bazai yiwu ba."
"Saboda ita ba mutum ba ce?"
Faruk ya jefamishi tambayar rai a 6ace.
Haidar ya dafa kafadarsa.
"Cool down mana, ba nufina wai wani abin daban ba, saidai matsayinku ya bambanta, wannan abu ba mai yiwuwa bane, ka chanja tunani Faruk, da kamar wuya su Daddy su yarjemaka."
Faruk ya murtuk'e fuska.
"Haka kake gani?"
Haidar da mamaki ya ke kallonsa.
"Kai baka gani?"
Ya girgiza kai gami da kwantar da kai jikin kujera.
"Ban ta6a hangen hakan ba, ban kuma sani ba ko don na riga na yi nisa a kaunarta ne yasa ban gano ba? Ni yanzu kai na zo ka ban shawarar wanda ya dace na soma tunkara tsakanin Hajiyarmu da Daddy?"
Haidar ya shafi goshinsa yana kara duban hoton Ummi sannan ya dubi Faruk.
"Ka sanarwa dukkansu alokaci guda. Ni a raayina, banga aibu a auren Ummi ba, na lura yarinya ce nutsastsiya sannan tana da kyawun hali da na fuska. Matsalar dai iyayenmu, idan sun amince shikenan, bansan raayin Babban Yaya da Dakta ba."
Faruk ya dan ta6e baki.
"Nifa zan zauna da ita. Shawara kawai daman na zo nema awajenka, ka kuma tayani adduar samun nasara akansu."
Haidar ya gyada kai yana dan murmushi.
"In sha Allahu, mai Ummi, zan tayaka. Amma wacece H din da ka zana?"
Faruk ya dan dara gami da kashe ido daya.
"Hasiya, real name dinta ne. Sunan mum dinta ta ci, amman ta rasu yanzu."
"Kai Nawan." Cewar Haidar gami da ba shi hannu suka cafke kamar wasu abokai.
"Wato komai nata ka sani? Duk ta yaya?"
Faruk ya gutsira mishi labarin Ummi, ya dora da fadin.
"Tausayinta ne ya soma rinjayar zuciyata har na soma jin sonta a raina."
Shi kansa Haidar ya tausayamata.
"Allah Sarki, rayuwa kenan, kowa da inda Allah Ya ajiyeshi, babu wanda yafi wani a wajenSa sai wanda yafi tsoronShi. Allah dai Ya datar da mu."
"Ameen broda. Ni bari na k'arasa, waya nakeson zuwa na siyo."
"Na wa kenan?"
Murmushi Faruk ya yi, Haidar ya dafa kafadarsa yana tayashi murmushin.
"Lallai na yarda da Dakta ke cewa irinku da bakwa soyayya idan kun tashi yi to zakuyi mai ban mamaki."
Abin ma sai ya bawa Faruk dariya, har wajen mota ya rakashi sannan sukayi sallama da zummar duk yanda Faruk sukayi da iyayen zai sanarmishi.
Hajiya Babba ta ajiye wayarta a gefe bayan ta gama amsawa ta dubi Ikram wacce ke zaman jiranta ta kammala.
"Ina jinki."
Ikram ta yi gyaran murya ta soma magana.
"Hajiya daman akan Ihsan ne."
Cike da mamaki ta dubeta.
"Meyafaru da Ihsan din? Ko ta gaji da mu ne?"
"A'a, daman..." (Ta kwashe tun farkon sadda Ihsan ta soma son Faruk har zuwa jiya da ta shiryamishi party na taya murnar ranar haihuwa.
Hajiya Babba bayan gama sauraronta ta numfasa fuskarta dauke da damuwa.
"Tun ba yau ba nasan yarinyarnan tana son Sadauki, saidai banga alamun Sadauki yana sonta ba."
Ikram itama ta jinjina kai, tasan gaskiya ne.
"Amma Hajiya bakya ganin a haka ya aureta idan yaso son ya shiga a hankali?"
"Kina ganin zai yarda? Banason abinda za'a zo zumunci ya lalace, matukar akayi aure ba da son ran daya ba to shakka babu zai shafi zumuncinmu abinda bazan ta6a fatan naga ranarsa ba kenan."
Ikram ta yi mamakin abinda Hajiyarsu ta ce, duk da tasan gaskiya ne, amma ai ya dace ta duba alak'a. Ita shaida ce akan yanda Hajiya ke tsananin kaunar dannata, batasan 6acin ransa tun yana karami kamar yanda ta samu labari daga yayyunsu. Ta bude baki zatayi magana Hajiya ta dagamata hannu.
"Ya isa hakanan, sai naji ta bakinsa, banason yi mishi katsalanda a lamari irin haka. Musamman lamari irin wannan na aure."
Jiki a sanyaye Ikram ta mike zata fita daga dakin, ta dakatar da ita.
"Maganar ta tsaya iyaka nan, ban yarje miki sanarwa Ihsan ba."
Ikram da ta rasa bakin magana, kai kawai ta gyada sannan ta fice har lokacin mamakin Hajiyarsu bai saketa ba, ko babu komai naka ai naka ne, saidai batasan hukuncin da zata yanke ba.
Mintuna k'alilan da yin hakan, Faruk ya dawo gidan a gajiye, kai tsaye sashensa ya nufa ya yi wanka ya sanya doguwar jallabiya ruwan madara da wando kafin ya dauki wayar da ya siyowa Ummi na kamfanin HTC ya sanyata a chaji. A karshe ya nufi sashen Daddy.
Acan ya iske Hajiya, suka gaisa kafin su shiga hira da iyayennasa. Can Daddy ya dubeshi.
"Son shekarunka talatin a duniya, ya ci ace zuwa yanzu ka soma tunanin aure."
"Ai ina jin ya samu matar aure, bai kai da fad'amana wacece ba ko Sadaukina?"
Murmushi ya yi yana mai shafar sumar kansa.
"A ina take?" Fadin Daddy kenan yana mai gyara zamansa don yasan dagasken ne don dannasu koda wasa bai ta6a zancen kowace mace ba.
"Ba ta yi nisa da mu ba sosai Daddy."
Hajiya da Daddy suka dubi juna, kafin su dubeshi.
"Ko 'yar gidan Alhaji Hamza? (Makwafcinsu)"
Ya yamutsa fuska.
"A'a, asalima ita ba 'yar garin nan bace."
"Wacece kenan?" Hajiya ta tambaya.
Ya yi shiru can kuma ya sunkuyar da kai.
"Zan kawomuku ita ku ganta cikin satinnan In sha Allah."
Suka gyada kai lokaci guda.
"Allah Ya kaimu." Fadin Daddy. Faruk da Hajiya suka amsa da amin, ita kuwa Hajiya ta soma tunanin kodai Ihsan ce?
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR