Sashe 89
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Suna zaune a falo da Hajiya dake lissafe-lissafenta na kaya hannunta rike da biro da dan(Memo) na lissafi, yayinda Ummi ke gefe tana karyawa, zuwa yanzu ta soma sakin jiki da Hajiyar. Sallama ya yi ciki-ciki, suka amsa, Hajiya bata dubeshi ba dalilin batason 6ata a k'irgenta. Ummi ta saci kallonsa, fuskar babu digon walwala, ta daure ta gaisheshi, ya amsa ganin Hajiya na wurin. Ta mike ta janyo tebur gabansa da niyyar hadamishi kari.
"No barshi, sai anjima zan karya."
Ta kada kai kawai ta koma mazauninta, Hajiya ba tare da ta dubeshi ba ta ce.
"A'a, kodai ba ka tare da yunwa ne? Wannan lokacin nasan kana karyawa Sadaukina, maza Ummi gama ki hadomishi."
Ta amsa da toh. Ya yamutse fuska yana duban Hajiya.
"Wai kwanab biyun nan wa ke gyaramin daki ne? Toilet dina k'arni. Ko kusa gyaran bai yi."
"Samira ce." Cewar Hajiya tana dubanshi. Ya dan muskuta.
"Daga yau ta daina bana bukata, sam bata iya aiki yanda ya kamata ba."
Hajiya ta dubi Ummi, kamar ta ce wani abu sai kawai ta share da fadin
"Allah Ya kyauta." Daga haka ta bi bayan wayar da aka kirata har ta yanke bata daga ba. Shi kuwa kwantar da kanshi ya yi jikin kujera ya lumshe idanunsa, shi kadai yasan me ya ke ji a zuciyarsa. Har Ummi ta gama ta hadamishi abin kari bai dago ba balle ya kalleta, itama dauriya kawai ta ke yi hakanan tana jin kunyar kanta bata son Hajiya ta fahimci akwai abinda ya hadasu, saidai tuni ta dagosu shiru kawai ta yi ta zubamusu ido.
Kai tsaye kicin ta sauka ta maida kofi da filet sannan ta yi hanyar sashensa, gyara ta hau yi, saida ta kammala ta tabbatar komai ya yi kyau sannan ta koma ga bandaki ta hau wankewa, saida ta kammala ta goge sannan ta fito rike da tsummokaran a bokiti, ta dubi ko'ina ta ga ya yi kyau sannan ta rufe kofar. Allah Ya taimaketa har ta zagaya wajen garden basu hadu ba, zama ta yi da niyyar wanke tsummokaran, sai kuma ta dakata cikin tunani, Allah Sarkin bayinSa kenan, kamar bata taka matsayin 'yar aiki ba kafin zuwan wannan lokaci da ta ke matsayi na Matar Dan Gida.
Acan kuwa Faruk koda ya hau samansa ya tarar da komai tsaf ya yi mamaki sosai da sosai, kamshi daddad'a kawai ke tashi, da sauri ya karasa ga dakinsa, nan ma an gyare tas hakanan bandaki wanda ke kamshi babu wannan k'arnin.
"To wa ya gyara?" Ya tambayi kansa, ya fito ya nufi barandarsa don ganin nan dinma ko an gyara, shima(tiles) din kamar ba'a ta6a takawa ba.
Kamar ance ya dubi ciki garden, ya hangota tana faman wanke tsummokarai, ya kasa gaskata idanunsa, sai kuma ya ga ta mike tana matsewa gami da shanyawa. Ji ya yi kamar ana k'ara kwararo mishi sonta, ga wani tausayinta da ya ji ya dirar masa, ina laifin ma ta yi gyaran kawai banda wannan wanke-wanken? Ya soma ja baya yana girgiza kai.
"No Ummina, matsayinki ya zarce haka gareni."
Kawai sai ya juya ya fita zuciyarsa na yi mishi babu dadi, ganinta ya ke yi kamar Ummin baya, wacce ta ke yiwa kanta kallon wata marar gata.
Ita kuwa tana tunane-tunanenta akan rayuwa har ta gama shanya, ta sanya hannu da zummar zubar da ruwan, sai ganin mutum ta yi tsaye, ta dubeshi shima din ita ya ke duba, ya kar6e bokitin ya ajiye, a kunyace ta sunkuyar da kanta. Ta kasa cewa uffan.
"Kinyi min gyara, na gani kuma na ji dadi, Allah Ya yi miki albarka."
"Amin, nagode." Ta amsa jiki a sanyaye ganin ba digon walwala a fuskarsa har lokacin.
"Don Allah Yaya Faruk ka yafemin na..."
"Ki dunga barwa ita Samirar ta dunga wanke wadannan." Ya yi nuni da tsummokaran, fuskarsa a daure ya juya ya tafi. Ta bishi da kallo idanunta cike da kwalla, wannan fushinnasa yana cin ranta kwarai, saidai me za ta yi mishi ya huce?
Misalin karfe sha daya Dakta da iyalinsa suka diro gidan, Jidda har daki ta biyota lokacin tana goge kayan Islamiyyarta, ta dan yi yak'e sadda gabanta ke bugu da sauri-sauri, tasan yau kam zaman gidan zai mata zafi saboda su da basu kaunar su bud'i ido su ganta.
"Anti Jidda sannu da zuwa, ina kwana."
Jidda wacce ta yi sakato tana dubanta da mamakin chanjawarta ta hau jinjina kai.
"Lallai kan mage ya waye, Ummin ce kuwa?" Ba kunya ba tsoron Allah ta furta a fili.
Ummi ta na murmushi ta maida kanta ga gugarta batare da ta ce komai ba.
Jidda ta ta6e baki sannan ta karewa dakin kallo kafin ta fice. Rufe kofarta ne yasa ta duban kofar, ga mamaki sai ta ji ta daure don ko kwallar bata yi ba, inda sabo kuma ai ta soma sabawa da wannan cin fuskar nasu. Fatanta lokacin makaranta ya yi ta wuce tun kafin su taru gaba dayansu abin ya zame mata da yawa, ga fushin Faruk gareta, sannan ga cin fuska daga su Jidda.
Faruk ya dubi Jidda, kwarai ya ji furucinta saidai ya basar ya cigaba da hirarsa da Dakta.
Ta iso garesu ta zauna gefen mijinta.
"Matarka ta yi k'iba ta kara kyau."
Ta fada tana duban Faruk, idan dutse zaiyi magana to ya yi gareta, ya cigaba da jan Dakta da hira. Jidda ta yi dariya kawai don tasan halin Faruk, koda zata wuni tana magana tunda kamar ransa a 6ace ya ke to fa bazai amsa mata ba.
Wajen karfe biyu saura sai ga Haidar da Intisar banda Ikram wacce daga can zata wuce makaranta, kamar hadin baki shima Babban Yaya ya iso alokacin da Fadila, Ummi na jin hayaniyarsu saidai bata ko lek'o falon ba, asalima alwala ta yi sannan ta shiga shirin tafiya makaranta. Turo kofar da akayi ne yasa ta waigowa, Intisar ce, ta shigo da murmushi saman fuskarta.
"Aa, Amarya Ummi sannu."
Ta gaisheta itama fuska a dan sake ganin ita dinma ba wani sabo suka yi ba amman bata bita da kallon banza ba irin na wadancan.
Ta karasa shigowa ciki tana fama da cikinta wanda ya doshi wata biyar saidai yana da girma.
"Makaranta za ki kenan? Ikram ma can muka barota a gida zata wuce, tare za ku yo nan."
"Toh." Ta fada cikin rashin sabo.
Daga haka ta fita itama ta cigaba da shirinta, saida ta yi sallar Azhar sannan ta dauki jakarta ta fito. Duk suna falon, yaransu suna gida saboda Islamiyya sai an tashi zasu yo nan.
Duk suka dubeta, ta yi kasa da kanta tana karanto adduoi cikin ranta, haka ta karasa ta durkusa ta gaishesu, duk suka amsa.
"Amaryar Lil, Allah Yasa alheri." Cewar Dakta, bata amsa ba banda kasa da ta yi da kanta tana murmushi kadan. Hajiya ta dubeta.
"Ki tsaya fa ki ci abinci kan ki wuce."
"Toh."
Sannan ta mike daga durkuson da ta yi ta nufi kasa, Jidda kallon kafafunta ta ke yi da suka sha kunshi wanda ya kara haskakata, ta ta6e baki gami da yin kus-kus da Fadila suka dara gami da tafawa.
Mazan suka dubesu kawai suka kauda kai. Faruk kuwa tsam ya mike. Ya dubi yayyunsa.
"Ina zuwa."
Daga haka ya sanya takalmi ya bi bayan Ummi, dariya sukayi, Hajiya kuwa murmushi kawai ta yi. Ta gama gaskatawa Ummi ce farincikin dan nata.
Ita kuwa baiwar Allah, a tsaitsaye ta ci fried rice din loma uku kawai ta yi, Binta na cewa ta k'ara, fadi ta ke a'a saita dawo. Ruwa ta sha sannan ta fito, har zata fita ta ji maganarsa.
"Ki jira na kaiki."
Ta tsaya cak batare da ta waiga ba, ya yi hanyar dakinsa, mukulli ya dauko, tana tsaye sai jin hon dinsa ta yi hakan ya fahimtar da ita cewar ta kofar baya ya zagaya. Ko a motar baice mata uffan ba, suna isa bayan ya tsaya ya dubeta.
"Yau me ya hanaki sanya safa?"
Cikin soma gajiya da wannan fushin na Faruk ta amsa cikin rawar murya.
"Na manta ne wallahi." Ya sa hannu gefensa ya bata wacce ya fito da shi ta sanya sannan ya cire lock ta fita.
"Nagode." Shine abinda ta ce cikin rawar murya sannan ta rufe kofar ta fice.
Tana shiga su Shukra suka tareta.
"Anti Hasiya yau ma Yayanmu ne ya kawoki?"
Tsaki ta ja wanda batasan sadda ya fita ba, ta giftasu ta wuce, suka bita da kallo kawai.
Husna ta lura kamar tana cikin damuwa, ta bi bayanta har kusa da kujerarta ta zauna gami da dafata.
"Lafiya kuwa Hasiya?"
Kamar jira ta ke yi kawai sai ta soma kuka, Husna ta rike kafadarta, ta duba ta ga ana kallonsu.
"Ki yi hakurin danne damuwarki, kinga idanuwa duk a kanki fa."
Jin haka yasa ta share idanunnata, ta daure ta nutsu, ayau ta ji kewar Antinta Amina kwarai, saidai itama Husna ta yarda da ita, tana da hankali, watakil ta samu shawarar da zata iya bata. .....
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
107
"No barshi, sai anjima zan karya."
Ta kada kai kawai ta koma mazauninta, Hajiya ba tare da ta dubeshi ba ta ce.
"A'a, kodai ba ka tare da yunwa ne? Wannan lokacin nasan kana karyawa Sadaukina, maza Ummi gama ki hadomishi."
Ta amsa da toh. Ya yamutse fuska yana duban Hajiya.
"Wai kwanab biyun nan wa ke gyaramin daki ne? Toilet dina k'arni. Ko kusa gyaran bai yi."
"Samira ce." Cewar Hajiya tana dubanshi. Ya dan muskuta.
"Daga yau ta daina bana bukata, sam bata iya aiki yanda ya kamata ba."
Hajiya ta dubi Ummi, kamar ta ce wani abu sai kawai ta share da fadin
"Allah Ya kyauta." Daga haka ta bi bayan wayar da aka kirata har ta yanke bata daga ba. Shi kuwa kwantar da kanshi ya yi jikin kujera ya lumshe idanunsa, shi kadai yasan me ya ke ji a zuciyarsa. Har Ummi ta gama ta hadamishi abin kari bai dago ba balle ya kalleta, itama dauriya kawai ta ke yi hakanan tana jin kunyar kanta bata son Hajiya ta fahimci akwai abinda ya hadasu, saidai tuni ta dagosu shiru kawai ta yi ta zubamusu ido.
Kai tsaye kicin ta sauka ta maida kofi da filet sannan ta yi hanyar sashensa, gyara ta hau yi, saida ta kammala ta tabbatar komai ya yi kyau sannan ta koma ga bandaki ta hau wankewa, saida ta kammala ta goge sannan ta fito rike da tsummokaran a bokiti, ta dubi ko'ina ta ga ya yi kyau sannan ta rufe kofar. Allah Ya taimaketa har ta zagaya wajen garden basu hadu ba, zama ta yi da niyyar wanke tsummokaran, sai kuma ta dakata cikin tunani, Allah Sarkin bayinSa kenan, kamar bata taka matsayin 'yar aiki ba kafin zuwan wannan lokaci da ta ke matsayi na Matar Dan Gida.
Acan kuwa Faruk koda ya hau samansa ya tarar da komai tsaf ya yi mamaki sosai da sosai, kamshi daddad'a kawai ke tashi, da sauri ya karasa ga dakinsa, nan ma an gyare tas hakanan bandaki wanda ke kamshi babu wannan k'arnin.
"To wa ya gyara?" Ya tambayi kansa, ya fito ya nufi barandarsa don ganin nan dinma ko an gyara, shima(tiles) din kamar ba'a ta6a takawa ba.
Kamar ance ya dubi ciki garden, ya hangota tana faman wanke tsummokarai, ya kasa gaskata idanunsa, sai kuma ya ga ta mike tana matsewa gami da shanyawa. Ji ya yi kamar ana k'ara kwararo mishi sonta, ga wani tausayinta da ya ji ya dirar masa, ina laifin ma ta yi gyaran kawai banda wannan wanke-wanken? Ya soma ja baya yana girgiza kai.
"No Ummina, matsayinki ya zarce haka gareni."
Kawai sai ya juya ya fita zuciyarsa na yi mishi babu dadi, ganinta ya ke yi kamar Ummin baya, wacce ta ke yiwa kanta kallon wata marar gata.
Ita kuwa tana tunane-tunanenta akan rayuwa har ta gama shanya, ta sanya hannu da zummar zubar da ruwan, sai ganin mutum ta yi tsaye, ta dubeshi shima din ita ya ke duba, ya kar6e bokitin ya ajiye, a kunyace ta sunkuyar da kanta. Ta kasa cewa uffan.
"Kinyi min gyara, na gani kuma na ji dadi, Allah Ya yi miki albarka."
"Amin, nagode." Ta amsa jiki a sanyaye ganin ba digon walwala a fuskarsa har lokacin.
"Don Allah Yaya Faruk ka yafemin na..."
"Ki dunga barwa ita Samirar ta dunga wanke wadannan." Ya yi nuni da tsummokaran, fuskarsa a daure ya juya ya tafi. Ta bishi da kallo idanunta cike da kwalla, wannan fushinnasa yana cin ranta kwarai, saidai me za ta yi mishi ya huce?
Misalin karfe sha daya Dakta da iyalinsa suka diro gidan, Jidda har daki ta biyota lokacin tana goge kayan Islamiyyarta, ta dan yi yak'e sadda gabanta ke bugu da sauri-sauri, tasan yau kam zaman gidan zai mata zafi saboda su da basu kaunar su bud'i ido su ganta.
"Anti Jidda sannu da zuwa, ina kwana."
Jidda wacce ta yi sakato tana dubanta da mamakin chanjawarta ta hau jinjina kai.
"Lallai kan mage ya waye, Ummin ce kuwa?" Ba kunya ba tsoron Allah ta furta a fili.
Ummi ta na murmushi ta maida kanta ga gugarta batare da ta ce komai ba.
Jidda ta ta6e baki sannan ta karewa dakin kallo kafin ta fice. Rufe kofarta ne yasa ta duban kofar, ga mamaki sai ta ji ta daure don ko kwallar bata yi ba, inda sabo kuma ai ta soma sabawa da wannan cin fuskar nasu. Fatanta lokacin makaranta ya yi ta wuce tun kafin su taru gaba dayansu abin ya zame mata da yawa, ga fushin Faruk gareta, sannan ga cin fuska daga su Jidda.
Faruk ya dubi Jidda, kwarai ya ji furucinta saidai ya basar ya cigaba da hirarsa da Dakta.
Ta iso garesu ta zauna gefen mijinta.
"Matarka ta yi k'iba ta kara kyau."
Ta fada tana duban Faruk, idan dutse zaiyi magana to ya yi gareta, ya cigaba da jan Dakta da hira. Jidda ta yi dariya kawai don tasan halin Faruk, koda zata wuni tana magana tunda kamar ransa a 6ace ya ke to fa bazai amsa mata ba.
Wajen karfe biyu saura sai ga Haidar da Intisar banda Ikram wacce daga can zata wuce makaranta, kamar hadin baki shima Babban Yaya ya iso alokacin da Fadila, Ummi na jin hayaniyarsu saidai bata ko lek'o falon ba, asalima alwala ta yi sannan ta shiga shirin tafiya makaranta. Turo kofar da akayi ne yasa ta waigowa, Intisar ce, ta shigo da murmushi saman fuskarta.
"Aa, Amarya Ummi sannu."
Ta gaisheta itama fuska a dan sake ganin ita dinma ba wani sabo suka yi ba amman bata bita da kallon banza ba irin na wadancan.
Ta karasa shigowa ciki tana fama da cikinta wanda ya doshi wata biyar saidai yana da girma.
"Makaranta za ki kenan? Ikram ma can muka barota a gida zata wuce, tare za ku yo nan."
"Toh." Ta fada cikin rashin sabo.
Daga haka ta fita itama ta cigaba da shirinta, saida ta yi sallar Azhar sannan ta dauki jakarta ta fito. Duk suna falon, yaransu suna gida saboda Islamiyya sai an tashi zasu yo nan.
Duk suka dubeta, ta yi kasa da kanta tana karanto adduoi cikin ranta, haka ta karasa ta durkusa ta gaishesu, duk suka amsa.
"Amaryar Lil, Allah Yasa alheri." Cewar Dakta, bata amsa ba banda kasa da ta yi da kanta tana murmushi kadan. Hajiya ta dubeta.
"Ki tsaya fa ki ci abinci kan ki wuce."
"Toh."
Sannan ta mike daga durkuson da ta yi ta nufi kasa, Jidda kallon kafafunta ta ke yi da suka sha kunshi wanda ya kara haskakata, ta ta6e baki gami da yin kus-kus da Fadila suka dara gami da tafawa.
Mazan suka dubesu kawai suka kauda kai. Faruk kuwa tsam ya mike. Ya dubi yayyunsa.
"Ina zuwa."
Daga haka ya sanya takalmi ya bi bayan Ummi, dariya sukayi, Hajiya kuwa murmushi kawai ta yi. Ta gama gaskatawa Ummi ce farincikin dan nata.
Ita kuwa baiwar Allah, a tsaitsaye ta ci fried rice din loma uku kawai ta yi, Binta na cewa ta k'ara, fadi ta ke a'a saita dawo. Ruwa ta sha sannan ta fito, har zata fita ta ji maganarsa.
"Ki jira na kaiki."
Ta tsaya cak batare da ta waiga ba, ya yi hanyar dakinsa, mukulli ya dauko, tana tsaye sai jin hon dinsa ta yi hakan ya fahimtar da ita cewar ta kofar baya ya zagaya. Ko a motar baice mata uffan ba, suna isa bayan ya tsaya ya dubeta.
"Yau me ya hanaki sanya safa?"
Cikin soma gajiya da wannan fushin na Faruk ta amsa cikin rawar murya.
"Na manta ne wallahi." Ya sa hannu gefensa ya bata wacce ya fito da shi ta sanya sannan ya cire lock ta fita.
"Nagode." Shine abinda ta ce cikin rawar murya sannan ta rufe kofar ta fice.
Tana shiga su Shukra suka tareta.
"Anti Hasiya yau ma Yayanmu ne ya kawoki?"
Tsaki ta ja wanda batasan sadda ya fita ba, ta giftasu ta wuce, suka bita da kallo kawai.
Husna ta lura kamar tana cikin damuwa, ta bi bayanta har kusa da kujerarta ta zauna gami da dafata.
"Lafiya kuwa Hasiya?"
Kamar jira ta ke yi kawai sai ta soma kuka, Husna ta rike kafadarta, ta duba ta ga ana kallonsu.
"Ki yi hakurin danne damuwarki, kinga idanuwa duk a kanki fa."
Jin haka yasa ta share idanunnata, ta daure ta nutsu, ayau ta ji kewar Antinta Amina kwarai, saidai itama Husna ta yarda da ita, tana da hankali, watakil ta samu shawarar da zata iya bata. .....
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
107