Sashe 85
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
102
Bayan Ummi ta kammala karyawa, ko mikewa daga wajen ba ta yi ba, Dada ta mik'omata wani abu a kofi, ta dubi kofin, tasan daman tun zuwanta tana bata nonon saniya tana sha, saidai wannan karon wani abu ta gani cikinsa mai kama da lalle, ta dago kai tana dan yamutse fuska ta dubeta.
"Menene wannan Dada?"
"Kar6i ki shanye sai na gayamaki." Ba musu ta kar6a ta shanye tas gami da saurin korawa da ruwa don dacin bakinta ya kau. Murmushi Dada ta yi sannan ta mik'amata wani kullin itatuwa a farar leda. Ummi ta kar6a tana dubanta.
"Maganin sanyi ne, da zarar kin dawo kafin biki, za ki dunga sha kina tsarki da shi, mahadinshi jar kanwa, wannan da ki ke gani ba'a wasa da shi, sakacin iyayenku kenan, sai a yita dabkawa mata kayan gyara amma ba a basu maganin sanyi. Sai ki ga bayan aure anzo anata faman zaryar zuwa asibiti."
Ita dai Ummi a kunyace ta ajiye ledar a gefe, Dada ta dauka tana cigaba da fadin.
"Ki dage wajen kula da jikinki, ko yanzu ai ke kanki kin ji chanji ba kamar yanda ki ka zo garinnan ba."
Ummi ta yi shiru, kwarai kuwa da gaskiyar Dada, don kuwa tun zuwanta kullum da abinda za ta bata ta sha, daga ta ce maganin basir sai kuwa na ciwon jiki. Ita dai hakanan ta ke sha batare da tasan wani abu na maganin ba.
Misalin bakwai na safe, Faruk ya yi mata text ya shaidamata tahowar direban tun biyar na Asuba, alokacin tana zaune Dada ta kira wata makwafciyarsu tana tsantsara mata kananun kitso, ga kunshi ana yi mata. Sun kwashi awanni uku suna yi kafin a kammala kitson, sannan ta wanke lallen, kowa ya ga kitson da kafarta sai ya tanka, wannan yasa ta rufe gashinta mai laushi da bak'i. Kafar kuwa ta makamishi safa. Ta yi wanka ta hade cikin wata doguwar rigar abaya mai ru6i biyu, bak'i da ruwan k'asa, wanda ya fiddo (shape) dinta, daga gefen hannuwan kuma sai aka yi shi mai fadi kamar buba. Ta yane kanta da mayafinsa.
Wajen karfe goma sha biyu da mintuna, Babanta ya kirawota, ya yi mata nasiha sosai akan ta kula ta kuma bi mijinta sau da k'afa a karshe ya sallameta bayan ya sanarmata cewa an damk'awa Dada sadakinta zata bata, nauyi ya hana Ummi cewa komai ta tashi ta wuce.
Shigarta ciki babu jimawa ta ji yaran gidan na ihun mota ta zo. Gabanta ta ji ya soma bugu, haka kawai ta ji kamar za ta kara yin nesa da yan uwanta.
"To Hasiya, tashi ki yi sallah za ku kama hanya. Shiru ta yi domin yau da asuba jini yazo mata. Shirunta ya fahimtar da Dada, kawai sai wuce ta dauki jakar kayanta ta mikawa Aliyu d'a na biyu wajen Baffa Haruna wanda baifi sa'an Adnan ba.
Ummi ta soma sharar hawaye, tana nan zaune har zuwa lokacin da aka ce ta fito su wuce. Nan ta rike Dada tana hawaye, Dada dakyar ta iya daurewa ta cireta daga jikinta.
"To mene na kukan kuma? Kiyi hakuri kinji, ai ba'a rabu ba. Rike wannan, sadakinki ne." Ta girgiza kai.
"Ki yimin abinda ki ka ga ya dace."
Daga haka ta zira takalminta mai tudu ta janyo jakarta bak'a wacce da ita ta zo sannan ta fito Dada na rike da ita.
Haka dai da kuka Ummi ta rabu da gidannan, mahaifinta shi kansa saida ya ji kamar ya yi kukan, Baffa na gaba ita da Abida suna baya.
Wayar direban ta yi kara, nan ya ke sanarwa da mai kiran cewa sun taho, ya yi musu adduar isowa lafiya sannan sukayi sallama. Ya dubi Baffa yana dan dariya.
"Yalla6ai ne." Baffa ya yi murmushi kawai. Direban kuwa dan surutu, sai ya hadu da Baffa shima ba kanwar lasa ba, tun Ummi na jinsu har ta yi matashi da cinyar Abida bacci mai nauyi ya dauketa.
Basu suka isa Abuja ba sai karfe bakwai da wasu mintuna, shima don sun yi tsaye-tsaye ne yin sallah da sauransu.
Tunda aka shigi garin Abuja Ummi ta ji kamar ta ruga aguje ta koma Gombe, da wane ido zata kalli Hajiya? Wai shikenan fa itama ta zama suruka a gidan.
Bayan isarsu kofar gidan, ya yi hon, da sauri Maigadi ya budemusu suka shiga yana dagamusu hannu. Ta rike hannun Abida. Abida wacce ta suma a kallon gida, ta dubeta, ganin yanda duk ta firgice yasa ta fadin.
"Ki yi ta addua." Sai lokacin ta tuna ta shiga yi, a harabar gidan babu kowa har zuwa lokacin da suka fito sai lokacin kuma suka Gen. Ahmad ya shigo dawowarsa kenan daga masallaci, a bayansa kuwa Haidar Danzaki ne sai ko Faruk Danzaki.
Ummi sai sunne kanta ta ke yi, Baffa ya karasa ya mikawa Daddy hannu suka yi musabaha, yana tambayar yanda suka iso. Su Ummi suka russuna suka gaishesu, sannan suka shiga ciki. Faruk ya tsunduma a kallonta baya ko kifta idanu, saida Haidar ya dan mintsileshi a kafada sannan ya dafa wajen yana 'yar kara kadan. Dariya suka yi.
"Control yourself mana."
Murmushi kawai ya yi kafin ya russuna yana gaida Baffa, sannan sukayi ciki.
Da Binta Ummi ta soma karo, suka rungume juna suna murna, harda hawayenta don Ummi kam akwai arhar kuka.
Binta ta dubeta.
"Kinga yanda ki ka koma kuwa? Ranki ya dade."
Dariya sukayi, lokacin da ta share hawayenta. Saukowar Hajiya daga sama ne yasa ta sunkuyar da kai a kunyace. Hajiya wacce ta kasa 6oye farincikinta ta karaso tana duban Abida.
"Sannunku da zuwa, diyata kunya ta shiga tsakaninmu kuma?"
Ta karashe tana mai rikota, dariya Abida da Binta sukayi.
Ta ja su zuwa sama, dakin Ummi suka sauka, saida sukayi wanka suka chanja kaya sannan Abida dake zaune saman darduma ta idar da sallah ta dubeta.
"Kai Ummi ki godewa Allah, na tayaki murna wallahi. Irin wannan karramakin da su ke yi? Ga uwa uba kuma suna da arziki? Kinyi sa'a sosai, sai naga ma haduwar gidan ta zarce yanda nake kissimawa."
Murmushi kawai Ummi ke yi lokacin da ta ke kokarin jona matacciyar wayarta a chaji. Tana sanye da doguwar riga(cotton) wacce da kadan ta wuce gwuiwa tana da botila a gaban rigar mai dogon hannu sai ta dora zani akai. Kanta rufe da hula, aka kwankwasa kofar da sallama, suka amsa sannan Binta ta shigo. Suka kara gaisawa da Abida kafin ta fadi sakon Hajiya na su fito su ci abinci.
Kamar ta tambayi Binta ina Ikram, sai kawai ta share.
Ta yafa mayafi suka fita itama Abida da lullu6inta.
A saman katuwar ledar cin abinci aka jera komai, Hajiya Babba ta yi musu bismillah, Ummi da kanta ta zuzzubamusu a ranta ta ji sanyin rashin ganin Faruk awajen don kunya ta ke ji.
Bayan sun kammala ta tattara, Hajiya na fadin ta barshi saidai bata saurara ba, ta yi k'asa, Abida ke fadin.
"To Hajiya ai an zama daya."
Saukarta yasa ta gwammace bata sauko din ba don kuwa Haidar ne da gogan zaune suna cin abinci. Dole ba yanda ta iya ta karasa saukowa, ta dan durkusa ta gaida Haidar, ya amsa fuska a sake.
"Sannu Amarya ya hanya?" Ta kasa dubansu, ciki-ciki ta amsa da Alhamdulillah.
Faruk ya bi le66anta da kallo don kuwa maganar bata fito sosai ba, murmushi ya yi sannan ya kauda kansa ya cigaba da cin abincinsa hankali kwance.
Ta mike ta karasa kicin, suka fito tare da Binta suka koma sama, nan suka iske Hajiya Babba da Abida suna ta hira, suka tattara suka koma kasa.
A kicin dinne Ummi ta samu danar tambayar Binta dake faman binta da kallo.
"Wai ina Ikram?"
Dariya Binta ta yi.
"Wallahi tana dawowa daga makaranta ta hada jaka ta gudu gidan Yaya Haidar, saidai fakewa ta yi da cewa zata taimakawa Intisar da ayyuka tunda cikinta ya soma tsufa, har shi Yaya Haidar din ke cewa ta barshi tunda ba tun yau ba yaso zuwannata ta k'i. Yanzu dai ta tafi can, nasan kuma karya ta ke yi wallahi saboda bakin cikin za ki zo matsayin matar Yalla6ai ne."
Murmushi mai ciwo Ummi ta yi, tasan daman da wuya Ikram ta chanja.
Saida ta lek'a ta ga sun bar falon sannan ta fito daga kicin ta haye sama. Babu kowa a falon wannan karon, Hajiya Babba ta yi wurin mijinta, Abida kuwa ta shiga daki, tana shirin murda kofa ta shige daki ta ji sallamar Faruk a bayanta. A rude ta juyo ta tabbatar shi dinne. Ya zubamata idanu yana sanye da riga da wando fari da ja.
"Waalaikumussalam."
Ta amsa a hankali.
Ya karaso daf da ita gami da sanya hannu ya dago ha6anta.
"Ki sameni wajen pool...please."
Ya karashe a tausashe. Ta gyada kai cikin rawar jiki, ya saketa sannan ya juya ya fice, ta bishi da kallo. Bata koma ciki ba sai kawai ta bi bayansa jiki ba kwari. Haidar ya wuce, ta gama waige-waigenta kamar mara gaskiya kafin ta murda kofar ta shiga. Kofar na waje baya ganin na ciki saidai na ciki ya ga na waje. Yana zaune yana duban ruwan, shigowarta yasa shi dago kai yana dubanta. Ta yi kasa da kanta tana mai kara gyara zaman mayafinta. Tana kokarin zama a kujerar gefensa ya janyota ta fada saman kafafunsa ba da niyya ba. Ji ta yi gaba daya ta rude, ta shiga kokarin mikewa saidai ya tare dukkan hanya. Take kuka ya tahomata.
"Don Allah ka yi hakuri."
Ya lumshe ido yana shak'ar kamshin turarenta. Ganin haka ta fisge da karfi ta mike gami da ja baya. Jingina kansa ya yi jikin kujera yana dubanta fuska dauke da murmushi.
"Come to me please Ummi."
Ko gezau ba ta yi, come dai ai ko dan kauyen yau da gobe zai san me kalmar ke nufi.
"Ka yi hakuri ka kyaleni na tafi."
Har lokacin bai motsa ba, saida ya kusan mintuna biyu yana dubanta sannan ya janyo kujera ya nunamata.
"Zo ki zauna."
Saida ta tabbatar dagaske ya ke sannan ta karasa ta zauna.
"Kun iso lafiya?"
Kai ta gyada don har lokacin cike ta ke da fargaba.
"Idan ba ki yi magana ba zan sanyaki yin ta dole fa."
"Alhamdulillah." Ta fada da sauri har muryar na hardewa, abin yaso ba shi dariya.
"Na so mu yi hira saidai na lura kamar kina tare da gajiya ko? Tafi ki kwanta, saidai Antinmu na tafiya za ki had'a kayanki ki komo dakina."
Ta zaro ido tana dubansa, shi kuwa ya hade fuska kamar gaske.
Kawai sai ta sunkuyar da kanta ta soma hawaye.
Karamin tsaki ya ja ya durkusa gabanta.
"Why? Komai kuka awajenki ko Ummina?"
Ya fada a sanyaye, bata ankara ba ta ji ya soma lashe hawayen, ta soma girgiza kai kafin ta yi yunkurin tureshi tana fadin.
"Don Allah Yaya Faruk..."
Yasa hannu akan le66anta kafin ya girgiza mata kai.
"Karki hanani please. Idan bakyaso ki daina kuka. Bakisan suna da tsada wurina ba?"
Ya karashe da murmushi saman fuskarsa. Sannan ya mike yana dubanta.
"Tashi na rakaki."
Ta mike da sauri don daman abinda ta ke zuci-zucin ta ji kenan.
Saida suka kai kofa ya riko kugunta ya kai bakinsa daf da kunnenta.
"I LOVE YOU."
Ta lumshe ido, abinda tunda suke bai ta6a furtamata kenan ba, jikinta ya dauki rawa, zata murda kofar, ya kai hannunsa kan nata suka murda tare. Da sauri ta fice.
"Hey!" Ya fada yanda yasan za ta ji, ta tsaya cak batare da ta juyo ba.
"Ba ki ban amsa ba."
Da sauri ta cigaba da tafiya har da gudu-gudunta. Ya bita da kallo yana murmushi sannan ya juya ya nufi samansa yana dan rera waka cike da nishadi.
@RUFAIDA OMAR
102
Bayan Ummi ta kammala karyawa, ko mikewa daga wajen ba ta yi ba, Dada ta mik'omata wani abu a kofi, ta dubi kofin, tasan daman tun zuwanta tana bata nonon saniya tana sha, saidai wannan karon wani abu ta gani cikinsa mai kama da lalle, ta dago kai tana dan yamutse fuska ta dubeta.
"Menene wannan Dada?"
"Kar6i ki shanye sai na gayamaki." Ba musu ta kar6a ta shanye tas gami da saurin korawa da ruwa don dacin bakinta ya kau. Murmushi Dada ta yi sannan ta mik'amata wani kullin itatuwa a farar leda. Ummi ta kar6a tana dubanta.
"Maganin sanyi ne, da zarar kin dawo kafin biki, za ki dunga sha kina tsarki da shi, mahadinshi jar kanwa, wannan da ki ke gani ba'a wasa da shi, sakacin iyayenku kenan, sai a yita dabkawa mata kayan gyara amma ba a basu maganin sanyi. Sai ki ga bayan aure anzo anata faman zaryar zuwa asibiti."
Ita dai Ummi a kunyace ta ajiye ledar a gefe, Dada ta dauka tana cigaba da fadin.
"Ki dage wajen kula da jikinki, ko yanzu ai ke kanki kin ji chanji ba kamar yanda ki ka zo garinnan ba."
Ummi ta yi shiru, kwarai kuwa da gaskiyar Dada, don kuwa tun zuwanta kullum da abinda za ta bata ta sha, daga ta ce maganin basir sai kuwa na ciwon jiki. Ita dai hakanan ta ke sha batare da tasan wani abu na maganin ba.
Misalin bakwai na safe, Faruk ya yi mata text ya shaidamata tahowar direban tun biyar na Asuba, alokacin tana zaune Dada ta kira wata makwafciyarsu tana tsantsara mata kananun kitso, ga kunshi ana yi mata. Sun kwashi awanni uku suna yi kafin a kammala kitson, sannan ta wanke lallen, kowa ya ga kitson da kafarta sai ya tanka, wannan yasa ta rufe gashinta mai laushi da bak'i. Kafar kuwa ta makamishi safa. Ta yi wanka ta hade cikin wata doguwar rigar abaya mai ru6i biyu, bak'i da ruwan k'asa, wanda ya fiddo (shape) dinta, daga gefen hannuwan kuma sai aka yi shi mai fadi kamar buba. Ta yane kanta da mayafinsa.
Wajen karfe goma sha biyu da mintuna, Babanta ya kirawota, ya yi mata nasiha sosai akan ta kula ta kuma bi mijinta sau da k'afa a karshe ya sallameta bayan ya sanarmata cewa an damk'awa Dada sadakinta zata bata, nauyi ya hana Ummi cewa komai ta tashi ta wuce.
Shigarta ciki babu jimawa ta ji yaran gidan na ihun mota ta zo. Gabanta ta ji ya soma bugu, haka kawai ta ji kamar za ta kara yin nesa da yan uwanta.
"To Hasiya, tashi ki yi sallah za ku kama hanya. Shiru ta yi domin yau da asuba jini yazo mata. Shirunta ya fahimtar da Dada, kawai sai wuce ta dauki jakar kayanta ta mikawa Aliyu d'a na biyu wajen Baffa Haruna wanda baifi sa'an Adnan ba.
Ummi ta soma sharar hawaye, tana nan zaune har zuwa lokacin da aka ce ta fito su wuce. Nan ta rike Dada tana hawaye, Dada dakyar ta iya daurewa ta cireta daga jikinta.
"To mene na kukan kuma? Kiyi hakuri kinji, ai ba'a rabu ba. Rike wannan, sadakinki ne." Ta girgiza kai.
"Ki yimin abinda ki ka ga ya dace."
Daga haka ta zira takalminta mai tudu ta janyo jakarta bak'a wacce da ita ta zo sannan ta fito Dada na rike da ita.
Haka dai da kuka Ummi ta rabu da gidannan, mahaifinta shi kansa saida ya ji kamar ya yi kukan, Baffa na gaba ita da Abida suna baya.
Wayar direban ta yi kara, nan ya ke sanarwa da mai kiran cewa sun taho, ya yi musu adduar isowa lafiya sannan sukayi sallama. Ya dubi Baffa yana dan dariya.
"Yalla6ai ne." Baffa ya yi murmushi kawai. Direban kuwa dan surutu, sai ya hadu da Baffa shima ba kanwar lasa ba, tun Ummi na jinsu har ta yi matashi da cinyar Abida bacci mai nauyi ya dauketa.
Basu suka isa Abuja ba sai karfe bakwai da wasu mintuna, shima don sun yi tsaye-tsaye ne yin sallah da sauransu.
Tunda aka shigi garin Abuja Ummi ta ji kamar ta ruga aguje ta koma Gombe, da wane ido zata kalli Hajiya? Wai shikenan fa itama ta zama suruka a gidan.
Bayan isarsu kofar gidan, ya yi hon, da sauri Maigadi ya budemusu suka shiga yana dagamusu hannu. Ta rike hannun Abida. Abida wacce ta suma a kallon gida, ta dubeta, ganin yanda duk ta firgice yasa ta fadin.
"Ki yi ta addua." Sai lokacin ta tuna ta shiga yi, a harabar gidan babu kowa har zuwa lokacin da suka fito sai lokacin kuma suka Gen. Ahmad ya shigo dawowarsa kenan daga masallaci, a bayansa kuwa Haidar Danzaki ne sai ko Faruk Danzaki.
Ummi sai sunne kanta ta ke yi, Baffa ya karasa ya mikawa Daddy hannu suka yi musabaha, yana tambayar yanda suka iso. Su Ummi suka russuna suka gaishesu, sannan suka shiga ciki. Faruk ya tsunduma a kallonta baya ko kifta idanu, saida Haidar ya dan mintsileshi a kafada sannan ya dafa wajen yana 'yar kara kadan. Dariya suka yi.
"Control yourself mana."
Murmushi kawai ya yi kafin ya russuna yana gaida Baffa, sannan sukayi ciki.
Da Binta Ummi ta soma karo, suka rungume juna suna murna, harda hawayenta don Ummi kam akwai arhar kuka.
Binta ta dubeta.
"Kinga yanda ki ka koma kuwa? Ranki ya dade."
Dariya sukayi, lokacin da ta share hawayenta. Saukowar Hajiya daga sama ne yasa ta sunkuyar da kai a kunyace. Hajiya wacce ta kasa 6oye farincikinta ta karaso tana duban Abida.
"Sannunku da zuwa, diyata kunya ta shiga tsakaninmu kuma?"
Ta karashe tana mai rikota, dariya Abida da Binta sukayi.
Ta ja su zuwa sama, dakin Ummi suka sauka, saida sukayi wanka suka chanja kaya sannan Abida dake zaune saman darduma ta idar da sallah ta dubeta.
"Kai Ummi ki godewa Allah, na tayaki murna wallahi. Irin wannan karramakin da su ke yi? Ga uwa uba kuma suna da arziki? Kinyi sa'a sosai, sai naga ma haduwar gidan ta zarce yanda nake kissimawa."
Murmushi kawai Ummi ke yi lokacin da ta ke kokarin jona matacciyar wayarta a chaji. Tana sanye da doguwar riga(cotton) wacce da kadan ta wuce gwuiwa tana da botila a gaban rigar mai dogon hannu sai ta dora zani akai. Kanta rufe da hula, aka kwankwasa kofar da sallama, suka amsa sannan Binta ta shigo. Suka kara gaisawa da Abida kafin ta fadi sakon Hajiya na su fito su ci abinci.
Kamar ta tambayi Binta ina Ikram, sai kawai ta share.
Ta yafa mayafi suka fita itama Abida da lullu6inta.
A saman katuwar ledar cin abinci aka jera komai, Hajiya Babba ta yi musu bismillah, Ummi da kanta ta zuzzubamusu a ranta ta ji sanyin rashin ganin Faruk awajen don kunya ta ke ji.
Bayan sun kammala ta tattara, Hajiya na fadin ta barshi saidai bata saurara ba, ta yi k'asa, Abida ke fadin.
"To Hajiya ai an zama daya."
Saukarta yasa ta gwammace bata sauko din ba don kuwa Haidar ne da gogan zaune suna cin abinci. Dole ba yanda ta iya ta karasa saukowa, ta dan durkusa ta gaida Haidar, ya amsa fuska a sake.
"Sannu Amarya ya hanya?" Ta kasa dubansu, ciki-ciki ta amsa da Alhamdulillah.
Faruk ya bi le66anta da kallo don kuwa maganar bata fito sosai ba, murmushi ya yi sannan ya kauda kansa ya cigaba da cin abincinsa hankali kwance.
Ta mike ta karasa kicin, suka fito tare da Binta suka koma sama, nan suka iske Hajiya Babba da Abida suna ta hira, suka tattara suka koma kasa.
A kicin dinne Ummi ta samu danar tambayar Binta dake faman binta da kallo.
"Wai ina Ikram?"
Dariya Binta ta yi.
"Wallahi tana dawowa daga makaranta ta hada jaka ta gudu gidan Yaya Haidar, saidai fakewa ta yi da cewa zata taimakawa Intisar da ayyuka tunda cikinta ya soma tsufa, har shi Yaya Haidar din ke cewa ta barshi tunda ba tun yau ba yaso zuwannata ta k'i. Yanzu dai ta tafi can, nasan kuma karya ta ke yi wallahi saboda bakin cikin za ki zo matsayin matar Yalla6ai ne."
Murmushi mai ciwo Ummi ta yi, tasan daman da wuya Ikram ta chanja.
Saida ta lek'a ta ga sun bar falon sannan ta fito daga kicin ta haye sama. Babu kowa a falon wannan karon, Hajiya Babba ta yi wurin mijinta, Abida kuwa ta shiga daki, tana shirin murda kofa ta shige daki ta ji sallamar Faruk a bayanta. A rude ta juyo ta tabbatar shi dinne. Ya zubamata idanu yana sanye da riga da wando fari da ja.
"Waalaikumussalam."
Ta amsa a hankali.
Ya karaso daf da ita gami da sanya hannu ya dago ha6anta.
"Ki sameni wajen pool...please."
Ya karashe a tausashe. Ta gyada kai cikin rawar jiki, ya saketa sannan ya juya ya fice, ta bishi da kallo. Bata koma ciki ba sai kawai ta bi bayansa jiki ba kwari. Haidar ya wuce, ta gama waige-waigenta kamar mara gaskiya kafin ta murda kofar ta shiga. Kofar na waje baya ganin na ciki saidai na ciki ya ga na waje. Yana zaune yana duban ruwan, shigowarta yasa shi dago kai yana dubanta. Ta yi kasa da kanta tana mai kara gyara zaman mayafinta. Tana kokarin zama a kujerar gefensa ya janyota ta fada saman kafafunsa ba da niyya ba. Ji ta yi gaba daya ta rude, ta shiga kokarin mikewa saidai ya tare dukkan hanya. Take kuka ya tahomata.
"Don Allah ka yi hakuri."
Ya lumshe ido yana shak'ar kamshin turarenta. Ganin haka ta fisge da karfi ta mike gami da ja baya. Jingina kansa ya yi jikin kujera yana dubanta fuska dauke da murmushi.
"Come to me please Ummi."
Ko gezau ba ta yi, come dai ai ko dan kauyen yau da gobe zai san me kalmar ke nufi.
"Ka yi hakuri ka kyaleni na tafi."
Har lokacin bai motsa ba, saida ya kusan mintuna biyu yana dubanta sannan ya janyo kujera ya nunamata.
"Zo ki zauna."
Saida ta tabbatar dagaske ya ke sannan ta karasa ta zauna.
"Kun iso lafiya?"
Kai ta gyada don har lokacin cike ta ke da fargaba.
"Idan ba ki yi magana ba zan sanyaki yin ta dole fa."
"Alhamdulillah." Ta fada da sauri har muryar na hardewa, abin yaso ba shi dariya.
"Na so mu yi hira saidai na lura kamar kina tare da gajiya ko? Tafi ki kwanta, saidai Antinmu na tafiya za ki had'a kayanki ki komo dakina."
Ta zaro ido tana dubansa, shi kuwa ya hade fuska kamar gaske.
Kawai sai ta sunkuyar da kanta ta soma hawaye.
Karamin tsaki ya ja ya durkusa gabanta.
"Why? Komai kuka awajenki ko Ummina?"
Ya fada a sanyaye, bata ankara ba ta ji ya soma lashe hawayen, ta soma girgiza kai kafin ta yi yunkurin tureshi tana fadin.
"Don Allah Yaya Faruk..."
Yasa hannu akan le66anta kafin ya girgiza mata kai.
"Karki hanani please. Idan bakyaso ki daina kuka. Bakisan suna da tsada wurina ba?"
Ya karashe da murmushi saman fuskarsa. Sannan ya mike yana dubanta.
"Tashi na rakaki."
Ta mike da sauri don daman abinda ta ke zuci-zucin ta ji kenan.
Saida suka kai kofa ya riko kugunta ya kai bakinsa daf da kunnenta.
"I LOVE YOU."
Ta lumshe ido, abinda tunda suke bai ta6a furtamata kenan ba, jikinta ya dauki rawa, zata murda kofar, ya kai hannunsa kan nata suka murda tare. Da sauri ta fice.
"Hey!" Ya fada yanda yasan za ta ji, ta tsaya cak batare da ta juyo ba.
"Ba ki ban amsa ba."
Da sauri ta cigaba da tafiya har da gudu-gudunta. Ya bita da kallo yana murmushi sannan ya juya ya nufi samansa yana dan rera waka cike da nishadi.