Sashe 4
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
"Assalamu Alaikum." Cewar Yaha alokacin da ta murd'a k'ofar falon ta sanya k'afa. Wata dattijuwa wacce ke zaune, wata budurwa mai kimanin shekaru sha shida. Tana zaune a k'asan lallausan kafet tana daddanna mata k'afa. Ta nutsu sosai, kamar kace arr! Ta arce.
Ummi dai kallonsu take, daga yanayin yanda ta ga Hajiyar na dubanta, ta sha jinin jikinta, da alama dai matar ba ta da mutunci don kuwa fuskarnan nata babu ko alamun fara'a.
"Ranki ya dad'e baya goya marayu, barkanki da hutawa."
Hajiya tayi wani murmushi, da alama ta ji dadin wannan kirari na Yaha. Ummi dai kallon ikon Allah take, yanayin shigarta da komai ma, sun isa shaidar tana cikin rayuwar daula. Wani kallo da Yaha ta watsa mata ne ya sanya ta ba shiri russunawa sosai gami da rankwafar da kanta ta gaisheta. Hajiyar bata ko amsa ba, saidai ta k'ura mata ido tana k'are mata kallo. Can kuma ta yamutse fuska ta rausaya kai gami da maida dubanta ga Yaha.
"Wannan ce?"
Yaha ta washe baki tana jinjina kai.
"Kwarai kuwa ranki ya dad'e uwar gida ran gida, itace, sunanta Hasiya amma Ummi ake kiranta."
Ummi dai sai zazzare ido take kamar shege a rabon gado, Hajiya Madina tayi murmushi, ko babu komai takan ji dadin wannan kirari da Yaha ke mata.
"Tayi sosai, na tabbatar, zata iya dukkan ayyukan da na na bata. Ince dai bata da son jiki?"
Yaha har lokacin bakinta ya k'i rufuwa don ji take kamar ta shid'e don dad'i domin kuwa ta sha kawowa Hajiya Madina yara, basu yi mata ba.
Ta janye k'afafunta, gami da kallon budurwar batare da tace uffan ba, ta mik'e ta wuce don ko Hajiya batayi magana ba, ta karanceta, wato dai ta basu guri.
Bayan komawarta ciki ne, Hajiya Madina ta dubi Yaha.
"Yahanasu, ina fatan kin shaida mata cewar banason wasa, ba kuma na son son jiki. Dukkan wasu ayyuka da na sanyata, inaso ta kammala su alokacin da ya kamata. Ba kuma na son k'azanta, ta kula sosai don kuwa naga yanayinta, da alama k'azamar ce."
Ummi ta sunkuyar da kai tana sosa gashin kanta wanda amosani ya bi ya takura mata, idan ma ance da kwarkwata lallai babu musu don bata da gatan da Saude zata wanke mata kai.
"Kiyi hakuri, na tabbatar ba zaki samu wannan matsalar ba. Sau daya aka gwada mata yanda zata gyara jikinta, na tabbatar babu wata matsala da zata biyo baya."
Hajiya Madina ta jinjina kai alokaci guda ta yamutse.
"Yauwa, don kinsan banason abinda wadancan shirmammun zasu samu damar zagina. Ko kusa banason wani mishkila ya fito daga d'akina."
Dariya Yaha tayi, ta gane Hajiya Madina tana nufin kishiyoyinta, Hajiya Rakiya da Hajiya Munira.
"Ai kin wuce nan Hajiyata, baya goya marayu. Kar kiji komai, yarinya ce mai kaifin basira. Zata bi dukkan umarninki batare da kin 6ata rai ba.
Kwarai, ta ji dadin kalaman Yaha. Daga nan ta mike da nufin zuwa gabatar da sallar la'asar, bayan ta umarci budurwar nan da ta ambata da Amina, da ta nunawa Ummi wajen kwanansu.
Amina a gaggauce ta bi umarnin Hajiya. Suka wuce tarr har Yaha wacce zata d'auro alwalar sallah itama. Ummi ta dubi d'akin, katifa d'aya ce sai filo, a gefe kuma jakar kaya ne. Sai kofa daya wacce ta ga Yaha ta shiga ciki, wannan ya tabbatarwa Ummi, bandaki ne. An malale dakin da ledar tsakar daki. Fentin dakin mai wani kyalkyali ne, fari da ruwan hoda, saidai babu komai na more rayuwa ciki.
Acan kusa da jakar kayanta, ta ajiyewa Ummi nata da murmushi saman fuskarta ta dubi Ummi, haka kawai ta tsinci kanta da murna sosai, ko babu komai ta samu abokiyar hira.
"Nan zaki dunga kwana."
Ummi ta mayarmata da martanin murmushin, saidai har lokacin bata saki jiki ba don kuwa ko k'arar k'ofa ta ji sai ta firgita. Ta riga da ta saba da hakan.
Yaba ta fito ta shimfida dardumar dakin ta tayar da sallah. Itama Ummi ta shiga, saidai tayi turus don kuwa bata saba da bandakin yan gayu har haka ba.
"Bari na nuna maki yanda zakiyi."
Cewar Amina daga bayanta, wannan yasa Ummi matsawa, ta shigo.
Nan ta gwada mata komai, Ummi tayi godiya cikin muryarta sassanya sannan ta shiga ta d'an kara k'ofar don ta tsorata, bata so ta rufe ta kasa bud'e kanta.
Bayan tayi alwala, irin yanda ta saba ganin mutane nayi don kuwa ko alfarmar zuwa makarantar islamiyya, Ummi bata samu ba. Tayi yanda ta iya sannan ta fito ta tayar da sallar. Tasan ana yin sallah raka'a hud'u a lokacin nan hakan yasa ta soma babu wani karatun kirki don babu abinda ta iya. Ta idar ta zauna tana motsa baki sannan ta yi jugum tana kalle-kalle.
Bayan Yaha ta kammala suka fita, Ramma ta basu abinci, nan suka ci sannan Hajiya ta sallami Yaha ta tafi da abin arziki
DAN ADAM
06
Maigidan, sunansa Alhaji Muhammad Modibbo. Shi d'an asalin garin Adamawa ne, bafulatani ne. Hajiya Madina 'yar uwarsa ce, saidai ita mahaifinta anan Kano ya rayu, anan ya tara zuri"arsa. Soyayya ta kullu tsakaninsu har ta kaisu ga aure lokacin shi Alhaji Muhammaf ya dawo Kano da karatu ya kuma kama aiki anan. Yana da mata biyu bayan ita, Hajiya Binta itace wacce kika gani rannan, sannan amaryarsa Hajiya Lubna, ita 'yar Maiduguri ce, yanzun ma da baki ganta ba, taje biki can Maiduguri da yaranta su hud'u gaba d'aya.
Hajiya Madina tana da yara takwas kamar yanda na fadamaki, ita kuwa Hajiya Binta yaranta shida. Iklima itace babbar budurwar 'yarta sannan Hanif, Sadiya, Nafisa, Usman da Jabir.
Ummi dai kallonsu take, daga yanayin yanda ta ga Hajiyar na dubanta, ta sha jinin jikinta, da alama dai matar ba ta da mutunci don kuwa fuskarnan nata babu ko alamun fara'a.
"Ranki ya dad'e baya goya marayu, barkanki da hutawa."
Hajiya tayi wani murmushi, da alama ta ji dadin wannan kirari na Yaha. Ummi dai kallon ikon Allah take, yanayin shigarta da komai ma, sun isa shaidar tana cikin rayuwar daula. Wani kallo da Yaha ta watsa mata ne ya sanya ta ba shiri russunawa sosai gami da rankwafar da kanta ta gaisheta. Hajiyar bata ko amsa ba, saidai ta k'ura mata ido tana k'are mata kallo. Can kuma ta yamutse fuska ta rausaya kai gami da maida dubanta ga Yaha.
"Wannan ce?"
Yaha ta washe baki tana jinjina kai.
"Kwarai kuwa ranki ya dad'e uwar gida ran gida, itace, sunanta Hasiya amma Ummi ake kiranta."
Ummi dai sai zazzare ido take kamar shege a rabon gado, Hajiya Madina tayi murmushi, ko babu komai takan ji dadin wannan kirari da Yaha ke mata.
"Tayi sosai, na tabbatar, zata iya dukkan ayyukan da na na bata. Ince dai bata da son jiki?"
Yaha har lokacin bakinta ya k'i rufuwa don ji take kamar ta shid'e don dad'i domin kuwa ta sha kawowa Hajiya Madina yara, basu yi mata ba.
Ta janye k'afafunta, gami da kallon budurwar batare da tace uffan ba, ta mik'e ta wuce don ko Hajiya batayi magana ba, ta karanceta, wato dai ta basu guri.
Bayan komawarta ciki ne, Hajiya Madina ta dubi Yaha.
"Yahanasu, ina fatan kin shaida mata cewar banason wasa, ba kuma na son son jiki. Dukkan wasu ayyuka da na sanyata, inaso ta kammala su alokacin da ya kamata. Ba kuma na son k'azanta, ta kula sosai don kuwa naga yanayinta, da alama k'azamar ce."
Ummi ta sunkuyar da kai tana sosa gashin kanta wanda amosani ya bi ya takura mata, idan ma ance da kwarkwata lallai babu musu don bata da gatan da Saude zata wanke mata kai.
"Kiyi hakuri, na tabbatar ba zaki samu wannan matsalar ba. Sau daya aka gwada mata yanda zata gyara jikinta, na tabbatar babu wata matsala da zata biyo baya."
Hajiya Madina ta jinjina kai alokaci guda ta yamutse.
"Yauwa, don kinsan banason abinda wadancan shirmammun zasu samu damar zagina. Ko kusa banason wani mishkila ya fito daga d'akina."
Dariya Yaha tayi, ta gane Hajiya Madina tana nufin kishiyoyinta, Hajiya Rakiya da Hajiya Munira.
"Ai kin wuce nan Hajiyata, baya goya marayu. Kar kiji komai, yarinya ce mai kaifin basira. Zata bi dukkan umarninki batare da kin 6ata rai ba.
Kwarai, ta ji dadin kalaman Yaha. Daga nan ta mike da nufin zuwa gabatar da sallar la'asar, bayan ta umarci budurwar nan da ta ambata da Amina, da ta nunawa Ummi wajen kwanansu.
Amina a gaggauce ta bi umarnin Hajiya. Suka wuce tarr har Yaha wacce zata d'auro alwalar sallah itama. Ummi ta dubi d'akin, katifa d'aya ce sai filo, a gefe kuma jakar kaya ne. Sai kofa daya wacce ta ga Yaha ta shiga ciki, wannan ya tabbatarwa Ummi, bandaki ne. An malale dakin da ledar tsakar daki. Fentin dakin mai wani kyalkyali ne, fari da ruwan hoda, saidai babu komai na more rayuwa ciki.
Acan kusa da jakar kayanta, ta ajiyewa Ummi nata da murmushi saman fuskarta ta dubi Ummi, haka kawai ta tsinci kanta da murna sosai, ko babu komai ta samu abokiyar hira.
"Nan zaki dunga kwana."
Ummi ta mayarmata da martanin murmushin, saidai har lokacin bata saki jiki ba don kuwa ko k'arar k'ofa ta ji sai ta firgita. Ta riga da ta saba da hakan.
Yaba ta fito ta shimfida dardumar dakin ta tayar da sallah. Itama Ummi ta shiga, saidai tayi turus don kuwa bata saba da bandakin yan gayu har haka ba.
"Bari na nuna maki yanda zakiyi."
Cewar Amina daga bayanta, wannan yasa Ummi matsawa, ta shigo.
Nan ta gwada mata komai, Ummi tayi godiya cikin muryarta sassanya sannan ta shiga ta d'an kara k'ofar don ta tsorata, bata so ta rufe ta kasa bud'e kanta.
Bayan tayi alwala, irin yanda ta saba ganin mutane nayi don kuwa ko alfarmar zuwa makarantar islamiyya, Ummi bata samu ba. Tayi yanda ta iya sannan ta fito ta tayar da sallar. Tasan ana yin sallah raka'a hud'u a lokacin nan hakan yasa ta soma babu wani karatun kirki don babu abinda ta iya. Ta idar ta zauna tana motsa baki sannan ta yi jugum tana kalle-kalle.
Bayan Yaha ta kammala suka fita, Ramma ta basu abinci, nan suka ci sannan Hajiya ta sallami Yaha ta tafi da abin arziki
DAN ADAM
06
Maigidan, sunansa Alhaji Muhammad Modibbo. Shi d'an asalin garin Adamawa ne, bafulatani ne. Hajiya Madina 'yar uwarsa ce, saidai ita mahaifinta anan Kano ya rayu, anan ya tara zuri"arsa. Soyayya ta kullu tsakaninsu har ta kaisu ga aure lokacin shi Alhaji Muhammaf ya dawo Kano da karatu ya kuma kama aiki anan. Yana da mata biyu bayan ita, Hajiya Binta itace wacce kika gani rannan, sannan amaryarsa Hajiya Lubna, ita 'yar Maiduguri ce, yanzun ma da baki ganta ba, taje biki can Maiduguri da yaranta su hud'u gaba d'aya.
Hajiya Madina tana da yara takwas kamar yanda na fadamaki, ita kuwa Hajiya Binta yaranta shida. Iklima itace babbar budurwar 'yarta sannan Hanif, Sadiya, Nafisa, Usman da Jabir.