Sashe 53
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
68
Dakta daman a fusacen yake, hannun dansa ya rik'e ya bar
falon bayan ya jefi Ummi da mugun kallo wanda batasan ma
yana yi ba don kanta a sunkuye ya ke tana faman kuka da
sheshshek'a. Itama Ikram mara mishi baya ta yi a guje tana
kukan marin da ta sha.
Daddy ya dubi Ummi.
"Tashi ki je Hasiya."
Ummi ta mik'e tana had'a hanya ta fita, tasan daman
lamarin ba mai yiwuwa ba ne sam, tun yanzu ta soma
fuskantar tashin hankali ina kuma ga idan ta koma Kano?
Daddy ya zauna sannan ya dubi Faruk wanda ke tsaye yana
duban hanyar da Ummi ta bi cike da matsanacin 6acin rai,
har lokacin bai daina jin dacin maganganun yan uwansa ba ga
matar da yafi so duk duniya.
"Zo ka zauna."
Cewar Daddy cikin kwantar da murya yana mai mishi nuni da
gefensa. A hankali ya taka ya zauna a k'asa rai a jagule.
Shiru na yan mintuna ya biyo baya kafin Daddy ya soma
magana....Ihsan tsaye a falon Hajiya Babba ta yi tana jin yanda 'yar
hatsaniya ke tashi a sashen Daddy, ji takeyi kamar ta je ta
ga abinda ke faruwa. Tana nan tsaye Dakta ya fito a fusace,
ko lura da ita baiyi ba haka ya fice, bata kai ga cewa komai
ba Ikram ma ta sanyo kai, hawaye sha6e-sha6e saman
fuskarta, a guje ta yi saman Hajiya, baki sake ta dubi
saman, tana shirin maramata baya Ummi ta fito itama cikin
shigar da ta mugun kad'a hanjin cikin Ihsan, gabanta ya hau
duka da sauri-sauri. Suka dubi juna ido cikin ido kafin kuma
a sanyaye Ummi ta soma tafiya, har ta bar wajen bata iya ce
mata uffan ba, ta dafe kirji wanda ta ke ji kamar zai fad'o.
"Me Ummi kuma ta ke yi a sashen Daddy, da kuma shiga
irin haka?"
Ganin babu mai amsamata ne yasa a karshe ta yanke
shawarar bin bayan 'yar uwata tasan ko menene zata ji.
Daddy ya dubi Faruk cikin kwantar da murya ya soma
magana.
"Tun tashinka ban ta6a kamaka da laifi na k'arya ko
yaudara da makamancinsa ba Faruk, hakazalika ka kasance
mutum wanda bai 6oye abinda zuciyarsa ke so."
Daddy ya danyi shiru sannan ya cigaba da magana.
"Ni ba k'aramin mutum bane, ba alfahari ba, Allah Ya
azurtani da yara masu d'abi'u kyawawa hakazalika masu
iyakar kokari wajen kiyaye dukkan wasu dokoki na
Ubangijinsu, wannan karon sai aka samu akasi, zuciyata ta
kasa nutsuwa da za6inka na matar aure, ina ganin kamar da
wata manufa ta daban ka ke son auren wannan baiwar Allah
da idan a batu na dukiya ne da jin dadin rayuwa, to kai din
kana sama da ita, ina so ka gayamin tsakani da Allah, wane
irin so ka ke ji ga yarinyar nan? Bazan lamunci tozarta DAN
ADAM ba, don kowanne akwai darajarsa ta musamman, bazan
lamunci ka aureta daga baya azo a samu matsala ba. Ka
fadamin gaskiyar abinda ka ke ji game da ita."
Faruk ji ya yi kamar ya d'aga Daddy ya cillashi sama yana
ca6e don dad'i. Ya dan saki fuska.
"Tsakani da Allah nake sonta Daddy, asalima kaunarta ta
samo asali ne daga tausayinta da nake ji, wallahi ba ni da
haramtacciyar nufi akanta."
Daddy ya yi murmushi gami da dafa kan Faruk.
"Tun da kake a rayuwa, ka ta6a zuwar min da wata buk'ata
na k'i?"
Hakoransa a bayyane yana murmushi ya girgiza kai.
"Aa Daddy."
"To wannan ma bazan k'i ba, matuk'ar na yi bincike akan
yarinyar na samu kyakkyawan magana, baka da matsala. Ni
mai aura maka Hasiya ne."
"Da SHARADI.!"
Suka tsinci muryar Hajiya daga bayansu, Faruk a rud'e ya
ke dubanta, ta karaso idanunta na zubda ruwan hawaye ta
zauna saman kujera.
"Ki ka ce me?" Daddy ya fada da mamaki yana kallonta.
Ihsan ta iske Ikram a daki tana kuka da sheshshek'a, wai yau
Yayansu Faruk mai hakuri shine ya mareta akan wata banza
yar aiki Ummi? Wannan abu da cin rai ya ke.
"Ke wai meke faruwa? Tashi ko sanardani don Allah, ni
gaba daya na shiga rud'ani wallahi, naga Ummi da wani shiga
mai ban mamaki."
Ikram ta mik'e zaune tana dubanta cikin dacin rai.
"Za ki ganta da fin wannan ma wallahi muddin ba ki bud'e
baki kin fayyacewa iyayenmu yanda ki ke ji game da Yaya
Faruk ba, a yau Yaya Faruk ya kawo Ummi gaban su Daddy
matsayin wacce ya ke so da aure. Har akanta ya mareni."
Ihsan daskarewa ta yi tana duban Ikram, ji take kamar jinin
jikinta baya gudana yanda ya dace, kamar wata sokuwa ta
bude baki ta na kallonta. Ikram ta fayyacemata duk yanda
akayi tun daga farko har zuwa marin da akayimata da rikicin
Dakta da Faruk.
Hawaye ne kawai ke kwararowa daga saman fuskar Ihsan ta
kasa kata6us. Abin ne ta ke masa kallon mafarki. Ummi dai
'yar aiki, Ummin da ta ke ganin ta fita a komai na rayuwa,
ta fita kudi da ilimi kai harma da yawan dangi kuma
wadatattu da sauransu. Faruk matashi abin so da shaawa ga
duk wata mace mai lafiya, matashi irinsa da ko 'yar
shugaban k'asa ko wani basaraken, bata isa ta yi mishi kallo
daya ta kauda kai batare da ta yabawa tsarin halittarsa ba,
mata nawa ne ke son dace da samunsa? Su nawa ke rububi da
fatan inama ace suna da damar da zaisa ya kasance a
matsayin mijin aurensu?
Ta girgiza kai tana sheshshek'a tana mai cigaba da sak'e-
sak'en zuci.
Abin kaico, ya buge a auren 'yar aikin gidansu, wacce zai
iya samun dubu da suka fita komai ya aura. Abin kunya ne
da takaici ace wai suna takara akan namiji daya tilo ita
da'yar aikin gidansu, wannan kam raini ne da kaskanci
agareta, wannan zubewar k'ima da ajinta ne a idanun
kawayenta da duk wanda yasan irin mutuwar son da ta ke
yiwa Faruk. Ikram kasa zaman dakin ta yi ta fito falo don ta
ji da nata zuciyar dake mata wani irin daci, ga kuma tausayin
Ihsan din da ta ke ji. Wasu lokutan so baima san kan wanda ya
dace ya fad'a ba, ba don zargi babu kyau ba da sai ta ce
anya kuwa ba wani siddabarun Ummi ta yi ga yayannata ba?
Idan ba haka ba, ina shi ina wata Ummi? Ko diri da kyawun
fuskarta ne ya d'ebeshi? Ta jefawa zuciyarta tambayar, sai
kuma ta girgiza kai. Kayya da kamar wuya, idan don hakan
ne kadai akwai wadanda suka ketare Ummin masu kaunarsa
amman bai za6esu ba.
Hajiya ta share hawayenta don daga daki ta ji dukka abinda
ke gudana, hankalinta ya tashi jin wai yau yaranta sun samu
sa6ani akan zancen auren Faruk. Ga kuma a gefe da ta ke
tsoron abinda zai rushen k'akk'arfan zumuncinsu da
kanwarta Madina. Ba zata ta6a amincewa hakan ya afku ba,
don Ummi kuwa, kwarai yarinya ce mai hankali, ta cancanci
zama matar d'anta don a halayya bata ta6a kamata da wani
dabi'a mai muni ba, hakanan bata ta6a cin amanarta ba,
daidai da Madina ta sha yaba hankalin yarinyar. Ta dubi
mijinta kafin ta maida dubanta ga Faruk wanda ya sunkuyar
da kansa cike da jin wani mugun tashin hankali. Yana
fargabar abinda zai fito daga bakin Mahaifiyartasa. Baya
fatan ace itama bata goyi baya ba, to amma a maganarta, ta
nuna goyon bayanta saidai ta ce da sharad'i.
"Kwarai kuwa Abban Ridwan, akwai sharad'i. Na amince ya
auri Ummi, amma ina so itama Ihsan ya aureta!"
Gaban Faruk ya bada sauti mai k'arfi, ya juyo a razane
yana duban Hajiya, fuskarta a daure wanda hakan ya nuna
babu alamun wasa a zancenta.
"Ita Ihsan din ce ta ce tana sona?"
"Na tabbatar kasan tana sonka Sadauki."
Daddy ya yi shiru. Faruk ya girgiza kai a gigice.
"Ni bana son..."
"Kaga, tashi ka tafi zan nemeka."
Cewar Daddy, Faruk ya mik'e ransa babu dadi ya fita, bai
ta6a sha'awar zama da mata biyu ba, ta ya ya Hajiya za ta
k'ak'aba mishi Ihsan alhalin tasan bai ta6a sonta ba?
Asalima bai ta6a soyayya da wata diya mace ba sai Ummi.
Hankalinsa ya koma ga Ummi, a wane ta ke ciki ne? Kai
tsaye ya nufi wajenta don bincikawa.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
71
Dakta daman a fusacen yake, hannun dansa ya rik'e ya bar
falon bayan ya jefi Ummi da mugun kallo wanda batasan ma
yana yi ba don kanta a sunkuye ya ke tana faman kuka da
sheshshek'a. Itama Ikram mara mishi baya ta yi a guje tana
kukan marin da ta sha.
Daddy ya dubi Ummi.
"Tashi ki je Hasiya."
Ummi ta mik'e tana had'a hanya ta fita, tasan daman
lamarin ba mai yiwuwa ba ne sam, tun yanzu ta soma
fuskantar tashin hankali ina kuma ga idan ta koma Kano?
Daddy ya zauna sannan ya dubi Faruk wanda ke tsaye yana
duban hanyar da Ummi ta bi cike da matsanacin 6acin rai,
har lokacin bai daina jin dacin maganganun yan uwansa ba ga
matar da yafi so duk duniya.
"Zo ka zauna."
Cewar Daddy cikin kwantar da murya yana mai mishi nuni da
gefensa. A hankali ya taka ya zauna a k'asa rai a jagule.
Shiru na yan mintuna ya biyo baya kafin Daddy ya soma
magana....Ihsan tsaye a falon Hajiya Babba ta yi tana jin yanda 'yar
hatsaniya ke tashi a sashen Daddy, ji takeyi kamar ta je ta
ga abinda ke faruwa. Tana nan tsaye Dakta ya fito a fusace,
ko lura da ita baiyi ba haka ya fice, bata kai ga cewa komai
ba Ikram ma ta sanyo kai, hawaye sha6e-sha6e saman
fuskarta, a guje ta yi saman Hajiya, baki sake ta dubi
saman, tana shirin maramata baya Ummi ta fito itama cikin
shigar da ta mugun kad'a hanjin cikin Ihsan, gabanta ya hau
duka da sauri-sauri. Suka dubi juna ido cikin ido kafin kuma
a sanyaye Ummi ta soma tafiya, har ta bar wajen bata iya ce
mata uffan ba, ta dafe kirji wanda ta ke ji kamar zai fad'o.
"Me Ummi kuma ta ke yi a sashen Daddy, da kuma shiga
irin haka?"
Ganin babu mai amsamata ne yasa a karshe ta yanke
shawarar bin bayan 'yar uwata tasan ko menene zata ji.
Daddy ya dubi Faruk cikin kwantar da murya ya soma
magana.
"Tun tashinka ban ta6a kamaka da laifi na k'arya ko
yaudara da makamancinsa ba Faruk, hakazalika ka kasance
mutum wanda bai 6oye abinda zuciyarsa ke so."
Daddy ya danyi shiru sannan ya cigaba da magana.
"Ni ba k'aramin mutum bane, ba alfahari ba, Allah Ya
azurtani da yara masu d'abi'u kyawawa hakazalika masu
iyakar kokari wajen kiyaye dukkan wasu dokoki na
Ubangijinsu, wannan karon sai aka samu akasi, zuciyata ta
kasa nutsuwa da za6inka na matar aure, ina ganin kamar da
wata manufa ta daban ka ke son auren wannan baiwar Allah
da idan a batu na dukiya ne da jin dadin rayuwa, to kai din
kana sama da ita, ina so ka gayamin tsakani da Allah, wane
irin so ka ke ji ga yarinyar nan? Bazan lamunci tozarta DAN
ADAM ba, don kowanne akwai darajarsa ta musamman, bazan
lamunci ka aureta daga baya azo a samu matsala ba. Ka
fadamin gaskiyar abinda ka ke ji game da ita."
Faruk ji ya yi kamar ya d'aga Daddy ya cillashi sama yana
ca6e don dad'i. Ya dan saki fuska.
"Tsakani da Allah nake sonta Daddy, asalima kaunarta ta
samo asali ne daga tausayinta da nake ji, wallahi ba ni da
haramtacciyar nufi akanta."
Daddy ya yi murmushi gami da dafa kan Faruk.
"Tun da kake a rayuwa, ka ta6a zuwar min da wata buk'ata
na k'i?"
Hakoransa a bayyane yana murmushi ya girgiza kai.
"Aa Daddy."
"To wannan ma bazan k'i ba, matuk'ar na yi bincike akan
yarinyar na samu kyakkyawan magana, baka da matsala. Ni
mai aura maka Hasiya ne."
"Da SHARADI.!"
Suka tsinci muryar Hajiya daga bayansu, Faruk a rud'e ya
ke dubanta, ta karaso idanunta na zubda ruwan hawaye ta
zauna saman kujera.
"Ki ka ce me?" Daddy ya fada da mamaki yana kallonta.
Ihsan ta iske Ikram a daki tana kuka da sheshshek'a, wai yau
Yayansu Faruk mai hakuri shine ya mareta akan wata banza
yar aiki Ummi? Wannan abu da cin rai ya ke.
"Ke wai meke faruwa? Tashi ko sanardani don Allah, ni
gaba daya na shiga rud'ani wallahi, naga Ummi da wani shiga
mai ban mamaki."
Ikram ta mik'e zaune tana dubanta cikin dacin rai.
"Za ki ganta da fin wannan ma wallahi muddin ba ki bud'e
baki kin fayyacewa iyayenmu yanda ki ke ji game da Yaya
Faruk ba, a yau Yaya Faruk ya kawo Ummi gaban su Daddy
matsayin wacce ya ke so da aure. Har akanta ya mareni."
Ihsan daskarewa ta yi tana duban Ikram, ji take kamar jinin
jikinta baya gudana yanda ya dace, kamar wata sokuwa ta
bude baki ta na kallonta. Ikram ta fayyacemata duk yanda
akayi tun daga farko har zuwa marin da akayimata da rikicin
Dakta da Faruk.
Hawaye ne kawai ke kwararowa daga saman fuskar Ihsan ta
kasa kata6us. Abin ne ta ke masa kallon mafarki. Ummi dai
'yar aiki, Ummin da ta ke ganin ta fita a komai na rayuwa,
ta fita kudi da ilimi kai harma da yawan dangi kuma
wadatattu da sauransu. Faruk matashi abin so da shaawa ga
duk wata mace mai lafiya, matashi irinsa da ko 'yar
shugaban k'asa ko wani basaraken, bata isa ta yi mishi kallo
daya ta kauda kai batare da ta yabawa tsarin halittarsa ba,
mata nawa ne ke son dace da samunsa? Su nawa ke rububi da
fatan inama ace suna da damar da zaisa ya kasance a
matsayin mijin aurensu?
Ta girgiza kai tana sheshshek'a tana mai cigaba da sak'e-
sak'en zuci.
Abin kaico, ya buge a auren 'yar aikin gidansu, wacce zai
iya samun dubu da suka fita komai ya aura. Abin kunya ne
da takaici ace wai suna takara akan namiji daya tilo ita
da'yar aikin gidansu, wannan kam raini ne da kaskanci
agareta, wannan zubewar k'ima da ajinta ne a idanun
kawayenta da duk wanda yasan irin mutuwar son da ta ke
yiwa Faruk. Ikram kasa zaman dakin ta yi ta fito falo don ta
ji da nata zuciyar dake mata wani irin daci, ga kuma tausayin
Ihsan din da ta ke ji. Wasu lokutan so baima san kan wanda ya
dace ya fad'a ba, ba don zargi babu kyau ba da sai ta ce
anya kuwa ba wani siddabarun Ummi ta yi ga yayannata ba?
Idan ba haka ba, ina shi ina wata Ummi? Ko diri da kyawun
fuskarta ne ya d'ebeshi? Ta jefawa zuciyarta tambayar, sai
kuma ta girgiza kai. Kayya da kamar wuya, idan don hakan
ne kadai akwai wadanda suka ketare Ummin masu kaunarsa
amman bai za6esu ba.
Hajiya ta share hawayenta don daga daki ta ji dukka abinda
ke gudana, hankalinta ya tashi jin wai yau yaranta sun samu
sa6ani akan zancen auren Faruk. Ga kuma a gefe da ta ke
tsoron abinda zai rushen k'akk'arfan zumuncinsu da
kanwarta Madina. Ba zata ta6a amincewa hakan ya afku ba,
don Ummi kuwa, kwarai yarinya ce mai hankali, ta cancanci
zama matar d'anta don a halayya bata ta6a kamata da wani
dabi'a mai muni ba, hakanan bata ta6a cin amanarta ba,
daidai da Madina ta sha yaba hankalin yarinyar. Ta dubi
mijinta kafin ta maida dubanta ga Faruk wanda ya sunkuyar
da kansa cike da jin wani mugun tashin hankali. Yana
fargabar abinda zai fito daga bakin Mahaifiyartasa. Baya
fatan ace itama bata goyi baya ba, to amma a maganarta, ta
nuna goyon bayanta saidai ta ce da sharad'i.
"Kwarai kuwa Abban Ridwan, akwai sharad'i. Na amince ya
auri Ummi, amma ina so itama Ihsan ya aureta!"
Gaban Faruk ya bada sauti mai k'arfi, ya juyo a razane
yana duban Hajiya, fuskarta a daure wanda hakan ya nuna
babu alamun wasa a zancenta.
"Ita Ihsan din ce ta ce tana sona?"
"Na tabbatar kasan tana sonka Sadauki."
Daddy ya yi shiru. Faruk ya girgiza kai a gigice.
"Ni bana son..."
"Kaga, tashi ka tafi zan nemeka."
Cewar Daddy, Faruk ya mik'e ransa babu dadi ya fita, bai
ta6a sha'awar zama da mata biyu ba, ta ya ya Hajiya za ta
k'ak'aba mishi Ihsan alhalin tasan bai ta6a sonta ba?
Asalima bai ta6a soyayya da wata diya mace ba sai Ummi.
Hankalinsa ya koma ga Ummi, a wane ta ke ciki ne? Kai
tsaye ya nufi wajenta don bincikawa.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
71