Sashe 46
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummi a rud'e ta k'ara d'agowa gami da lek'awa. Hankali kwance ya ke zanensa banda murmushi babu abinda kake gani a saman fuskarsa. Wasu ruwan hawaye ne suka zubomata, shikenan yau babu ita ba k'ara kwana a gidannan. Da sauri ta juya ta soma harhad'a kayanta don bil hakki ita kadai tasan iyakar rudanin da ta shiga.
Gogan kuwa, ya kwashi tsawon minti goma sha biyar kafin ya kammala ya mik'e tsaye, ganin haka yasa kowannensu mik'ewa, kowace budurwa awajen babu wacce kirjinta bai bugu da sauri-sauri don fargabar fuskar da zasu gani. Haidar ya k'ara tasowa ya iso gareshi, ya kai dubansa ga takardar zanen, ya k'urawa zanen ido, babu abinda kake gani sai manyan idanunta, ya yi alamun nikaf wanda ya rufe gaba daya fuskarta, sai kadan daga siririn hancinta da ya dan fiddo mai dauke da karamin bak'in tabo daga sama. Ya kauda lasufika sannan ya harareshi.
Haka mukayi da kai?"
Faruk da ke kokarin saka kwat dinsa ya daga mishi gira kadan.
"Ina kishin a ganta."
Haidar ya jinjina kai yana dariya sannan ya kara duban hoton sosai.
"Kamar na ta6a ganin mai irin tabon nan, saidai bazan iya tuna a ina ba."
Faruk ya murmusa kafin ya k'ara daukar alk'alami, daga k'asa ya rubuta farkon sunanta.
"H"
Haidar duk iyakar tunaninsa bai ganeta ba, a karshe ya daga kafada kadan gami da maida dubansa ga jama'a wadanda ke jin kamar su tashi su warci hoton su sha kallo. Baice komai ba ya juya zanen ya nuna musu.
"Ga wacce Kanina ya zana, sunanta da harafin H ya soma, ya dai yi mana kwalelan fuskarta inda ya ce yana kishin a ganemishi kyakkyawar fuskarta."
Dariya matasan suka sanya, ita kuwa Ihsan ido ta k'urawa zanen, ta kasa gane ko wacece ita.
"Wace kenan?" Shine tambayar da da yawa daga yanmatan. Ihsan ta dubi Ikram cikin rawar murya don har ta soma kwalla.
"Wa ki ka sani mai farkon suna H?"
Ikram wacce tausayin Ihsan ya mamayeta ta daga kafada kadan.
"Bani da masaniya akan kowacece, Hafsa kadai na sani sai Hadiyya, yanzu duk sunyi aure ma."
Ita kuwa Ummi jin maganar Haidar ne yasa ta tsayawa daga abinda ta soma na watsa kayanta cikin yar jakarta. Ta mike da sauri ta lek'a, saidai bata ganin zanen yanda ya kamata, hakan yasa ta fitowa wajen, a daidai bayan bishiyar dogon yaro ta dan la6e tana hangen zanen. Ta dan sauke ajiyar zuciya duk kuwa da cewar akwai sauran rina a kaba, ta shafi karan hancinta, tabbas bakin a tabon nan yana nan inda ya ke wanda ta samu asanadin wani ciwo da ta ji awajen tun tana yarinya. Gabanta na dukan tara-tara ta zaro ido.
'Yanzu idan aka gane ni da wannan tabon ya zanyi ni Hasiya?' Ta tambayi zuciyarta, tambayar da tasan amsar bai wuce na ta shiga uku ba.
Lokacin da Haidar ya kammala addu'oin fatan alheri shi da budurwar da ya ke so, aka soma mikewa da kadan kadan ana mik'a mishi kyautuka. Ihsan ta so barin wajen don ita kadai tasan yanda ta ke ji, saidai Ikram ta lalla6ata gami da nunamata kada ta sake ta yi wasa da wannan damar, shi kadai ya yi mata saura, haka ta daure ta karasa gami da mik'a mishi kyautar da ta tanada domin shi wanda a ciki sak'on da ta ke son isar mishi ya ke. Ya kar6a yana mai dubanta, ko baa fada ba, idan ka kalli idanunta kasan ta yi kuka. Bai nuna ya gane komai ba, godiya ya yi mata sannan ta bar wajen da saurinta.
Haka kawai sai Ummi ta ji tausayinta, tana son maso wani, son wanda ta ke yi don shi baisan tana yi ba. A sanyaye ta juya ta bar wajen ta koma daki. Bata yi mintuna uku da shiga ba ta ji an murda kofar da sallama an shigo. Ai batasan sadda ta mik'e tsaye ba tsabar kidimewa. Murmushi ya sakarmata sannan ya tura kofar ya rufe. Karasowa ya yi yana dubanta.
"Matsoraciya Ummina."
Ta yi raurau da ido, ya girgiza mata kai.
"Kar fa kice kuka zakimin."
Ta yi k'asa da kanta. Yasa hannu a ha6anta ya dago fuskarta suka dubi juna ido cikin ido. Ta lumshe idonta don ba zata jure kallon kwayar idanunsa ba. Ya saukr hannunsa gami da sakin ajiyar zuciya. Allah kadai yasan irin wutar kaunarta da ke ruruwa a zuciyarta a kowane dak'ik'a.
Hankalinsa ya kai ga kayanta da rabinsu ta sanya a jaka ga wasu a k'asa.
"Menene wannan?"
Ta dubi kayan sannan ta tuna ashe fa guduwa ta yi shirin yi.
"Bakomai, linkesu nake yi."
Ya durkusa gaban kayan ya soma dagasu, duk ba wasu kayan kirki gareta sosai ba, ya girgiza kai kawai ya mike tsaye. Ta dubeshi kadan.
"Domin Allah ka tafi Yaya Faruk, kada a je nemanka."
Ya rungume hannunsa a kirji.
"Wai kuwa Ummi kina kallon kanki a madubi kuwa?"
Bai bari ta yi magana ba yasa hannu ya dauki hodarta dake gefe ya bude gami da juyamata, ta dubi dan madubin na hodar, kafin ta sauke idanunta kasa. Ya numfasa da murmushi saman fuskarsa.
"Shikenan dai."
Shiru ya biyo baya, tana ji Haidar na cigiyarsa ta lasufika akan ya zo sallamar bak'insa. Ta daure ta yi magana.
"Ina tayaka murnar wannan rana, Allah Ya k'aro shekaru masu albarka, Ya taimaki rayuwarka."
"Amin. Allah Ya nunamana na aurenmu haka. Thanks my Ummi, zo muje ki rakani mu sallami bak'inmu."
Ya kai hannu da zummar riko nata, ta ja baya da sauri tana girgiza kai.
"Ke na soma gajiya da 6oyon da muke yi, aurenki fa nakeson yi. Amma dai..."
Ya jinjina kai kawai sannan ya juya ya fita, a kofar sukayi kici6us da Binta ta gaisheshi, fuska a daure ya amsa gami da fadin.
"Ki kiyaye bakinki." Shi ne abinda yace, ta amsa da to cikin sauri, daga nan ya yi gaba. Da sauri ta fad'a dakin wajen Ummi. Ummi na ganin itace ta sauke numfashi don a farko da ta ji maganar da Faruk ya yi duk ta dauka ko da Ikram ya ke. Binta ta kama ha6a bakinta a washe.
"Ke Ummi, abu fa ya soma zafi, anya kuwa nan gaba Yalla6ai bazai daukeki daga sashen yan aiki ya maida cikin gidansu ba, kafin daga baya ya daukeki cancak zuwa gidan aurenku?"
Ummi ta yi dariya, maganar Binta ta karshe ta yi mata dadi. Ita kuwa Binta k'irr ta tsayar da ido tana duban fuskar Ummi kafin ta doka tsalle ta rungumeta tana ihun murna.
"Kece, daman nasan ke ce wallahi."
Ummi ta kwaci kanta tana kokarin rufewa Binta baki.
"Ki rufamin asiri kiyi shiru kada wani ya ji."
Binta tana dariya ta yi mata nuni da tabon dake a saman hancinta.
"Wannan tabon nayi mamakin yanda Yalla6ai ya ganoshi, naga sai an k'ura miki ido ake ganeshi."
"Shiyasa nake gudun ranar da asirina zai tonu."
Guntun tsaki Binta ta ja.
"To menene? Ke saifa kin zama jaruma wallahi. Ni kizo muje kaya aka bani na kai dakin Yalla6ai, ki zo ki tayani kwashe kyaututtukansa."
Girgiza kai ta yi.
"Ki taimakeni ki je ke kadai babu inda zan je."
Dariya Binta ta saka.
"Kekam ban ga irinki a fagen tsoro ba."
Ummi ta bi ta da kallo kawai har ta fice.
Haka shagalin ya k'are kowacce budurwa jiki a sanyaye don ba'a samu shiga ba ta ko'ina.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
63
Misalin tara na daren, falon Hajiya Babba babu kowa sai matasan yaranta da matansu, sai kuma su Ikram.
Fadila ta kar6i hoton zanen daga hannun Jidda tana mai kuramishi ido itama. Jidda ta dubesu.
"Nikam kaina ya k'ulle ai, nayi iyakar yi na na kasa gane wacece wannan wallahi. Kai na karfen baka kyauta mana ba, yanda muka ci burin yau mu ga hoton matarka?"
Ta karashe tana duban Faruk wanda abincinsa ya ke ci babu ko alamun damuwa a fuskarsa.
"Ke dai bari kawai Jidda, ni kaina ya soma sarawa ma don kallon zanen." Cewar Fadila. Sukayi dariya, Hajiya Babba ta mike tana fadin.
"Um, idan dai Sadauki ne kadan daga aikinsa, a komai sai ya bada mamaki."
Daga haka ta barsu suka bita da kallo. Faruk ya dubi Haidar.
"Broda, ina fa da magana da kai."
"Bakasan hanyar gidana ba?"
Ya yi murmushi.
"Sau daya fa na ta6a zuwa gidanka tun kafin tariyarka, kaga kuwa na mance."
"Aa Lil, baka kyauta ba kam." Cewar Dakta.
Babban Yaya na murmushi ya cafe.
"Kuyi mishi uzuri, aikinsa babu hutu sosai."
Haka sukayita hirarsu, a karshe bayan duk sun tafi, Ikram ta mike rike da takardar zanen zuwa dakinsu.
Ihsan na kwance har kanta ya soma sarawa sanadin kukan da ta ci. Ta mike zaune gami da kar6ar takardar.
"Duk iyakar tunani ban gane wacece wannan ba Ikram, saidai na rasa dalilin da yasa jikina ke bani kamar na santa, kuma na ta6a ganin kwayar idanun nan."
Ikram ta jinjina kai.
"Ni kaina nakasa hakura da kallon zanen wallahi, gani nakeyi kamar nasanta."
Ihsan ta ja tsaki gami da wurgi da takardar.
"Me zan amfana da shi a saninta ma? Ni yanzu gaba daya na gaji da zaman Abija, gida zan koma."
Ikram ta dubeta.
"Kada kiyi saurin karaya ina kara baki shawara, ni nasan taimakon da zan miki."
Ihsan ta dubeta cikin rashin fahimta.
"Ban fahimceki ba."
Murmushi Ikram ta yi.
"Kedai ki bani lokaci."
Jin hakan yasa Ihsan ta dan samu nutsuwa.
A daidai gaban motar Haidar suka tsaya, Intisar na ciki tana jira su kammala. Haidar ya dubeshi.
"Ina jinka."
Faruk ya gyara tsayuwa.
"I am serious fa, wacce na zana dagaske ita nake son aure, saidai ni a wajena ban dauki hakan matsala ba kamar yanda ku ma bana tunani za ku k'i farincikina."
Haidar ya daga kafada kadan cikin rashin fahimta.
"Me ya kawo duk wadannan? Yarinyar musulma ce?"
"Eh."
"Tana da asali?"
"Kwarai kuwa."
Murmushi ya yi gami da dafa kafadarsa.
"Idan akwai hakan, a ganina babu wata matsala, gayamin a ina ta ke?"
Faruk na murmushin shima ya shafi sumarsa.
"Zan zo gidanka gobe daga ofis."
"Dayake taka ce zata kawoka ko? Ai yanzun na ga kafarka."
Sukayi dariya sannan sukayi sallama ya shiga motar suka wuce.
*** *** ***
KADUNA
Gogan kuwa, ya kwashi tsawon minti goma sha biyar kafin ya kammala ya mik'e tsaye, ganin haka yasa kowannensu mik'ewa, kowace budurwa awajen babu wacce kirjinta bai bugu da sauri-sauri don fargabar fuskar da zasu gani. Haidar ya k'ara tasowa ya iso gareshi, ya kai dubansa ga takardar zanen, ya k'urawa zanen ido, babu abinda kake gani sai manyan idanunta, ya yi alamun nikaf wanda ya rufe gaba daya fuskarta, sai kadan daga siririn hancinta da ya dan fiddo mai dauke da karamin bak'in tabo daga sama. Ya kauda lasufika sannan ya harareshi.
Haka mukayi da kai?"
Faruk da ke kokarin saka kwat dinsa ya daga mishi gira kadan.
"Ina kishin a ganta."
Haidar ya jinjina kai yana dariya sannan ya kara duban hoton sosai.
"Kamar na ta6a ganin mai irin tabon nan, saidai bazan iya tuna a ina ba."
Faruk ya murmusa kafin ya k'ara daukar alk'alami, daga k'asa ya rubuta farkon sunanta.
"H"
Haidar duk iyakar tunaninsa bai ganeta ba, a karshe ya daga kafada kadan gami da maida dubansa ga jama'a wadanda ke jin kamar su tashi su warci hoton su sha kallo. Baice komai ba ya juya zanen ya nuna musu.
"Ga wacce Kanina ya zana, sunanta da harafin H ya soma, ya dai yi mana kwalelan fuskarta inda ya ce yana kishin a ganemishi kyakkyawar fuskarta."
Dariya matasan suka sanya, ita kuwa Ihsan ido ta k'urawa zanen, ta kasa gane ko wacece ita.
"Wace kenan?" Shine tambayar da da yawa daga yanmatan. Ihsan ta dubi Ikram cikin rawar murya don har ta soma kwalla.
"Wa ki ka sani mai farkon suna H?"
Ikram wacce tausayin Ihsan ya mamayeta ta daga kafada kadan.
"Bani da masaniya akan kowacece, Hafsa kadai na sani sai Hadiyya, yanzu duk sunyi aure ma."
Ita kuwa Ummi jin maganar Haidar ne yasa ta tsayawa daga abinda ta soma na watsa kayanta cikin yar jakarta. Ta mike da sauri ta lek'a, saidai bata ganin zanen yanda ya kamata, hakan yasa ta fitowa wajen, a daidai bayan bishiyar dogon yaro ta dan la6e tana hangen zanen. Ta dan sauke ajiyar zuciya duk kuwa da cewar akwai sauran rina a kaba, ta shafi karan hancinta, tabbas bakin a tabon nan yana nan inda ya ke wanda ta samu asanadin wani ciwo da ta ji awajen tun tana yarinya. Gabanta na dukan tara-tara ta zaro ido.
'Yanzu idan aka gane ni da wannan tabon ya zanyi ni Hasiya?' Ta tambayi zuciyarta, tambayar da tasan amsar bai wuce na ta shiga uku ba.
Lokacin da Haidar ya kammala addu'oin fatan alheri shi da budurwar da ya ke so, aka soma mikewa da kadan kadan ana mik'a mishi kyautuka. Ihsan ta so barin wajen don ita kadai tasan yanda ta ke ji, saidai Ikram ta lalla6ata gami da nunamata kada ta sake ta yi wasa da wannan damar, shi kadai ya yi mata saura, haka ta daure ta karasa gami da mik'a mishi kyautar da ta tanada domin shi wanda a ciki sak'on da ta ke son isar mishi ya ke. Ya kar6a yana mai dubanta, ko baa fada ba, idan ka kalli idanunta kasan ta yi kuka. Bai nuna ya gane komai ba, godiya ya yi mata sannan ta bar wajen da saurinta.
Haka kawai sai Ummi ta ji tausayinta, tana son maso wani, son wanda ta ke yi don shi baisan tana yi ba. A sanyaye ta juya ta bar wajen ta koma daki. Bata yi mintuna uku da shiga ba ta ji an murda kofar da sallama an shigo. Ai batasan sadda ta mik'e tsaye ba tsabar kidimewa. Murmushi ya sakarmata sannan ya tura kofar ya rufe. Karasowa ya yi yana dubanta.
"Matsoraciya Ummina."
Ta yi raurau da ido, ya girgiza mata kai.
"Kar fa kice kuka zakimin."
Ta yi k'asa da kanta. Yasa hannu a ha6anta ya dago fuskarta suka dubi juna ido cikin ido. Ta lumshe idonta don ba zata jure kallon kwayar idanunsa ba. Ya saukr hannunsa gami da sakin ajiyar zuciya. Allah kadai yasan irin wutar kaunarta da ke ruruwa a zuciyarta a kowane dak'ik'a.
Hankalinsa ya kai ga kayanta da rabinsu ta sanya a jaka ga wasu a k'asa.
"Menene wannan?"
Ta dubi kayan sannan ta tuna ashe fa guduwa ta yi shirin yi.
"Bakomai, linkesu nake yi."
Ya durkusa gaban kayan ya soma dagasu, duk ba wasu kayan kirki gareta sosai ba, ya girgiza kai kawai ya mike tsaye. Ta dubeshi kadan.
"Domin Allah ka tafi Yaya Faruk, kada a je nemanka."
Ya rungume hannunsa a kirji.
"Wai kuwa Ummi kina kallon kanki a madubi kuwa?"
Bai bari ta yi magana ba yasa hannu ya dauki hodarta dake gefe ya bude gami da juyamata, ta dubi dan madubin na hodar, kafin ta sauke idanunta kasa. Ya numfasa da murmushi saman fuskarsa.
"Shikenan dai."
Shiru ya biyo baya, tana ji Haidar na cigiyarsa ta lasufika akan ya zo sallamar bak'insa. Ta daure ta yi magana.
"Ina tayaka murnar wannan rana, Allah Ya k'aro shekaru masu albarka, Ya taimaki rayuwarka."
"Amin. Allah Ya nunamana na aurenmu haka. Thanks my Ummi, zo muje ki rakani mu sallami bak'inmu."
Ya kai hannu da zummar riko nata, ta ja baya da sauri tana girgiza kai.
"Ke na soma gajiya da 6oyon da muke yi, aurenki fa nakeson yi. Amma dai..."
Ya jinjina kai kawai sannan ya juya ya fita, a kofar sukayi kici6us da Binta ta gaisheshi, fuska a daure ya amsa gami da fadin.
"Ki kiyaye bakinki." Shi ne abinda yace, ta amsa da to cikin sauri, daga nan ya yi gaba. Da sauri ta fad'a dakin wajen Ummi. Ummi na ganin itace ta sauke numfashi don a farko da ta ji maganar da Faruk ya yi duk ta dauka ko da Ikram ya ke. Binta ta kama ha6a bakinta a washe.
"Ke Ummi, abu fa ya soma zafi, anya kuwa nan gaba Yalla6ai bazai daukeki daga sashen yan aiki ya maida cikin gidansu ba, kafin daga baya ya daukeki cancak zuwa gidan aurenku?"
Ummi ta yi dariya, maganar Binta ta karshe ta yi mata dadi. Ita kuwa Binta k'irr ta tsayar da ido tana duban fuskar Ummi kafin ta doka tsalle ta rungumeta tana ihun murna.
"Kece, daman nasan ke ce wallahi."
Ummi ta kwaci kanta tana kokarin rufewa Binta baki.
"Ki rufamin asiri kiyi shiru kada wani ya ji."
Binta tana dariya ta yi mata nuni da tabon dake a saman hancinta.
"Wannan tabon nayi mamakin yanda Yalla6ai ya ganoshi, naga sai an k'ura miki ido ake ganeshi."
"Shiyasa nake gudun ranar da asirina zai tonu."
Guntun tsaki Binta ta ja.
"To menene? Ke saifa kin zama jaruma wallahi. Ni kizo muje kaya aka bani na kai dakin Yalla6ai, ki zo ki tayani kwashe kyaututtukansa."
Girgiza kai ta yi.
"Ki taimakeni ki je ke kadai babu inda zan je."
Dariya Binta ta saka.
"Kekam ban ga irinki a fagen tsoro ba."
Ummi ta bi ta da kallo kawai har ta fice.
Haka shagalin ya k'are kowacce budurwa jiki a sanyaye don ba'a samu shiga ba ta ko'ina.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
63
Misalin tara na daren, falon Hajiya Babba babu kowa sai matasan yaranta da matansu, sai kuma su Ikram.
Fadila ta kar6i hoton zanen daga hannun Jidda tana mai kuramishi ido itama. Jidda ta dubesu.
"Nikam kaina ya k'ulle ai, nayi iyakar yi na na kasa gane wacece wannan wallahi. Kai na karfen baka kyauta mana ba, yanda muka ci burin yau mu ga hoton matarka?"
Ta karashe tana duban Faruk wanda abincinsa ya ke ci babu ko alamun damuwa a fuskarsa.
"Ke dai bari kawai Jidda, ni kaina ya soma sarawa ma don kallon zanen." Cewar Fadila. Sukayi dariya, Hajiya Babba ta mike tana fadin.
"Um, idan dai Sadauki ne kadan daga aikinsa, a komai sai ya bada mamaki."
Daga haka ta barsu suka bita da kallo. Faruk ya dubi Haidar.
"Broda, ina fa da magana da kai."
"Bakasan hanyar gidana ba?"
Ya yi murmushi.
"Sau daya fa na ta6a zuwa gidanka tun kafin tariyarka, kaga kuwa na mance."
"Aa Lil, baka kyauta ba kam." Cewar Dakta.
Babban Yaya na murmushi ya cafe.
"Kuyi mishi uzuri, aikinsa babu hutu sosai."
Haka sukayita hirarsu, a karshe bayan duk sun tafi, Ikram ta mike rike da takardar zanen zuwa dakinsu.
Ihsan na kwance har kanta ya soma sarawa sanadin kukan da ta ci. Ta mike zaune gami da kar6ar takardar.
"Duk iyakar tunani ban gane wacece wannan ba Ikram, saidai na rasa dalilin da yasa jikina ke bani kamar na santa, kuma na ta6a ganin kwayar idanun nan."
Ikram ta jinjina kai.
"Ni kaina nakasa hakura da kallon zanen wallahi, gani nakeyi kamar nasanta."
Ihsan ta ja tsaki gami da wurgi da takardar.
"Me zan amfana da shi a saninta ma? Ni yanzu gaba daya na gaji da zaman Abija, gida zan koma."
Ikram ta dubeta.
"Kada kiyi saurin karaya ina kara baki shawara, ni nasan taimakon da zan miki."
Ihsan ta dubeta cikin rashin fahimta.
"Ban fahimceki ba."
Murmushi Ikram ta yi.
"Kedai ki bani lokaci."
Jin hakan yasa Ihsan ta dan samu nutsuwa.
A daidai gaban motar Haidar suka tsaya, Intisar na ciki tana jira su kammala. Haidar ya dubeshi.
"Ina jinka."
Faruk ya gyara tsayuwa.
"I am serious fa, wacce na zana dagaske ita nake son aure, saidai ni a wajena ban dauki hakan matsala ba kamar yanda ku ma bana tunani za ku k'i farincikina."
Haidar ya daga kafada kadan cikin rashin fahimta.
"Me ya kawo duk wadannan? Yarinyar musulma ce?"
"Eh."
"Tana da asali?"
"Kwarai kuwa."
Murmushi ya yi gami da dafa kafadarsa.
"Idan akwai hakan, a ganina babu wata matsala, gayamin a ina ta ke?"
Faruk na murmushin shima ya shafi sumarsa.
"Zan zo gidanka gobe daga ofis."
"Dayake taka ce zata kawoka ko? Ai yanzun na ga kafarka."
Sukayi dariya sannan sukayi sallama ya shiga motar suka wuce.
*** *** ***
KADUNA