Sashe 49
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A fili kuwa don ta kwantar mata da hankali. Ta nunamata bawani abu bane, ya dace ta koyi jarumta tun daga yanzu. Ta k'ara bata shawarar tashi tsaye da addua, inda ta tabbatar mata itama zata tayata. Ummi ta yi godiya sannan ta jawo ledar suka bude. Wani hadadden Atamfa (pink) ne mai turuwa, a wani 6angaren mai dan haske-haske, anyi dinkin riga da zani, koda Ummi ta daga rigar ta girgiza kai.
"Anya rigar nan zata yimin?"
"Tsaf ma kuwa, tashi ki gwada kedai."
Ba musu ta gwada, ai kam ba karamin kyau ya yi mata ba. Ta cire suka cigaba da duba ledar, harda dan kunne da sark'a fashion mai kyau da agogo, harda turare kala uku da kayan kwalliya, abin bai tsaya anan ba har dasu takalmi fari kalar mayafin da ya sanyomata. Binta banda washe baki babu abinda takeyi, ita kuwa mai abin jikinta sanyi ya k'ara yi. Wayar ta k'ara dagawa tana juyawa.
"Kai Ummi ki godewa Allah, kin samu mijin da ya iya kula da matarsa wallahi."
Murmushi Ummi ta yi.
"Kai Binta, har ya zama mijina?"
"Haka nake miki fata 'yar kanwata, nidai nasan gudunmuwar da zan baki a wannan lokacin idan ya zo."
Dariya kawai Ummi ta yi gami da girgiza kai, a ranta fatan hakan ya ksance takeyi.
Sun dan jima tare da Binta kafin ta mik'e ta yi mata sallama don ta soma hamma na jin bacci. Bayan fitarta ta maida kayan cikin ledar ta yi gefe da su.
Alwala ta d'auro ta gabatar da nafila, ta jima tana addu'o'i kafin ta shafa ta koma makwancinta. Wayar ta k'urawa ido tana jujjuyawa, ta yi nisa cikin tunani wayar ta dauki k'ara.
'Hubbyna.' Shine sunan da ya fito, wani ajiyar zuciya ta saki gami da yin murmushi. Kafin ta dauka kamar yanda ya koyamata yacce zata yi.
Sallama ta soma yi mishi ya amsa.
"Ba ki yi bacci ba, meyasa?"
Ta ji daddadan muryarsa har cikin jini da bargonta.
"Bakomai." Shiru ya dan biyo baya can kuma ya yi magana.
"Ina fatan ba kuka kikayi ba?"
Da mamaki karara akan fuskarta ta girgiza kai.
"Ni..ni banyi kuka ba."
Ya yi murmushi mai sauti.
"Ni kuma jikina ya bani kinyi kuka Ummina, amman dai shikenan. Ya kika ga kayan, sunyi miki ko a chanja?"
'Ni na isa nace basuyi ba?' Ta fada a zuciyarta batare da sanin ya fito fili ba.
"Har kin yi yawa indai awajen Umar Faruk ne. Ni ban ajiyeki nan kusa ba fa. Amma yanzu duk bazaki gane hakan ba sai bayan aurenmu."
Ta lumshe ido tana mai jin wani kaunarsa sabuwa fil a cikin ranta.
"Inama hakan zata faru Yaya Faruk."
Furucin ya yi mishi dadi, ya fahimci ta soma sakin jiki da shi.
"Zai faru in sha Allahu Ummina, ki kwantar da hankalinki har zuwa ranar da Umarul Faruk zai mantar da ke dukkan bakkan ciki da iznin Allah, ranar da zamu kasance mata da miji abin so da alfahari. Matukar ni ne mijinki, bazan k'ara barin ki cikin hali na damuwa ba. Watakil sai kin gaji da ni, don daga ranar da na aureki, na daina zuwa aiki."
Dariya sosai ya bata, sai gashi ta shiga yinta kwarai. Ya lumshe ido gami da k'ara rungume daya daga cikin kananun filon dake saman gadonsa. Shi kadai yasan yanda ya ke jin dariyarta. Ta tsaida dariyar cike da jin kunya. Murya kamar na wanda baya son magana ya ce.
"Naso ace kina gabana kike dariyar nan Ummi, yana daga cikin abinda ban ta6a gani ba daga gareki, kuma zanso na ganin."
Ta sunkuyar da kanta tamkar yana ganinta ta hau wasa da igiyar hular t-shirt din dake jikinta.
"Saida safe Yaya Faruk, bacci nake ji."
"Ko na zo?"
Ta zaro ido kamar yanda ganinta, ya yi 'yar dariya.
"Matsoraciyata, na tabbatar kin tsorata. Shikenan saida safe, kiyi mana adduar fa."
"To."
Daga haka sukayi sallama. Ta bi wayar da kallo tana murmushi. A karshe ta ajiyeta gefe, mikewa ta yi ta yi nafila sannan ta karanta istihara tana kallo a takarda kafin ta shafa ta kwanta.
WASHEGARI....!!!!
Cikin ikon Allah ta tashi da jin kwarin gwuiwa a zuciya da gangar jiki, kaso sitti na damuwarta ya ragu.
Bayan Magriba ya shigo gidan, kai tsaye sashensa ya soma nufa. Bayan ya yi wanka ya nemi Ummi a waya, tana zaune tana harhad'a kayanta sanin da ta yi cewar gobe Asabar kuma a ranar Hajiya ta sanarmata shine na komawarta Kano, wayar ta katseta. Hannu tasa ta dauka, tasan ko waye mai kiran, gabanta na dukan tara-tara ta dauka da sallama. Ya amsa sannan ta gaisheshi.
"Ki shirya Ummi, na dawo ina sama, da zarar na kammala abinda nakeyi zan sauko mu je."
Ji ta yi kamar ta saki fitsari, ta daure ta gyada kai don bakinta ya yi mata nauyi. Shaf ta mance ma waya ce suke yi.
"Ummi, meyafaru kuma?"
Ya tambaya a sanyaye. Sai lokacin ta dan samu ta yi magana.
"Bakomai, zan shirya."
Ya yi murmushi mai sauti.
"Ko kefa."
Daga nan sukayi sallama. Ta yi k'uri tana duban wayar kafin kuma ta ajiyeta.
"Allah ka saukaka mana." Ta fada a fili, tana mai amsawa kanta.
Shigowar Binta ya katseta, ta amsa sallamarta. Binta ta k'araso.
"Naga fa Yalla6ai ya dawo."
Ummi ta yi murmushin karfin hali.
"Munyi waya yanzu, yana nan kan bakansa, yanzun ma cewa ya yi na shirya."
Binta ta jinjina kai.
"Sai ki tashi, hakanan za ki je kedai kiyita addua a ranki."
Ta saka kayan, Binta ta gyaramata fuskarta, ta yi mata daurin dankwali mai hawa-hawa irin na zamani. Ta taimaka mata da sanya dan kunne da sark'an. Sai kuma ta saki baki tana kallonta.
"Masha Allah, wallahi Ummi na k'ara ganin abinda Yalla6ai ya hango wajenki, Ummi bakiyi kalar 'yan aiki ba."
Ummi ta girgiza kai bata iya cewa komai ba don a yanzun ita kadai tasan yanayin da ta ke ciki.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
65
Mik'ewa ya yi ya koma daki ta bishi da kallo cikin jin wani shauki na kaunarsa.
'Kaico, Yaya Faruk an kusa rabamu.'
Ta fad'a a ranta, jikinta yana bata cewa komai ya zo karshe, watakil harda zamanta cikin zuri'ar tasu gaba d'aya, tasan maganar Antinta ya kusa tabbata wanda ta ce.
'Karki manta matsayinmu awajen mutanen nan, mu 'yan aiki ne, ba su daukemu komai ba face wannan Ummi. Bar ganin suna mana dariya, duk sadda muka bari wasu lamura suka afku ranar zasu tunamana cewar mu kaskantu ne awajensu, ranar zasu tunamana matsayinmu na marasa galihu.'
Hannunsa ta ji saman fatar fuskarta yana sharemata ruwan hawaye. Ta dubeshi, fuskarsa kai ka rantse bai ta6a dariya ba.
"Kinaso muyi fad'a kenan, na tsani nayita nanata magana d'aya. Karki so ki ji yanda nakejin zuciyata idan kina kuka, amma ke naga kamar kin fison damuwata."
Karo na biyu da ta ji tana son fadamishi damuwarta.
"Kayi hakuri Yaya Faruk, saidai gani nakeyi kamar an kusa yimin katanga da kai."
Ya zubamata ido baice uffan ba, hannunsa tuni ya sauke daga saman fuskarta. Can kuma ya soma magana.
"Fata nagari lamiri, ki saka a ranki in sha Allah babu wani abu da zai yanke alak'armu har ya zuwa aurenmu da rayuwar auren. Banaso kina kawo komai a ranki. Yau idan da dama, kada ki rage bacci ki tashi mu yiwa junanmu addua akan Allah Ya za6amana abinda yafi alheri. Kin iya karanta istihara?"
Ta girgiza kai.
"Ban iyaba, saidai ina da Hisnul muslim."
Ya gyada kai.
"Ki yi adduar istihara a yau Ummi, in sha Allah zamu ga daidai a lamuranmu. Ga wannan."
Ya mik'amata wata leda, ta sa hannu ta kar6a.
"Shi nakeso ki saka gobe idan na kiraki a waya, kinji?"
Ta gyada kai.
"Yauwa."
Daga nan ya sallameta ya yi mata rakiya har suka sauka daga matattakala sannan ya tsaya ta wuce.
"Zan kiraki." Ya fada da muryar rad'a. Ta dubeshi ta murmusa ya yi mata alamun (kiss) da baki, a kunyace ta wuce da sauri. Daga haka ya koma sama.
Bayan ya kammala dukkan wasu ayyuka, ya soma duba kyaututtukan da yan uwa da abokan arziki suka ba shi, sai a yau ya samu wannan damar. Turaruka sunfi komai yawa, agogo kuwa kusan biyar ya samu, wasu kuwa kayan kwalam ne har da katina kala-kala. Hankalinsa ya kai ga na Ihsan, yasa hannu ya dauka ya bude. Kamshi ya soma ziyartar hancinsa....!
Wani hadadden agogo ne sai kuma zobe na azurfa. Murmushi ya yi sadda ta ci karo da kati mai dauke da kalaman so. Ya bude ya karanta.
"My friends told me that falling in love would be the most beautiful feeling in the world. After I fell in love with you, I realized that even the most beautiful feeling in the world would look ugly against your love. Frm Ihsan Modibbo."
Ya ta6e baki kadan, ya cigaba da daga sauran katinan, duk kalamai ne na nuna soyayya.
'Ya tabbata tana sona din kenan?' Ya ayyana a ransa kafin ya lumshe ido. Baya fatan shiga matsala saboda ita, a rayuwarsa bai ta6a shaawar kasancewa da kowace mace ba face Umminsa, ta makaro, bayajin zata samu wani gurbi a zuciyarsa, saidai kuma ta dan ba shi tausayi.
Ya dan ja guntun tsaki sannan ya mik'e ya tsallake kayan ya shiga harkar gabansa.
"Anya rigar nan zata yimin?"
"Tsaf ma kuwa, tashi ki gwada kedai."
Ba musu ta gwada, ai kam ba karamin kyau ya yi mata ba. Ta cire suka cigaba da duba ledar, harda dan kunne da sark'a fashion mai kyau da agogo, harda turare kala uku da kayan kwalliya, abin bai tsaya anan ba har dasu takalmi fari kalar mayafin da ya sanyomata. Binta banda washe baki babu abinda takeyi, ita kuwa mai abin jikinta sanyi ya k'ara yi. Wayar ta k'ara dagawa tana juyawa.
"Kai Ummi ki godewa Allah, kin samu mijin da ya iya kula da matarsa wallahi."
Murmushi Ummi ta yi.
"Kai Binta, har ya zama mijina?"
"Haka nake miki fata 'yar kanwata, nidai nasan gudunmuwar da zan baki a wannan lokacin idan ya zo."
Dariya kawai Ummi ta yi gami da girgiza kai, a ranta fatan hakan ya ksance takeyi.
Sun dan jima tare da Binta kafin ta mik'e ta yi mata sallama don ta soma hamma na jin bacci. Bayan fitarta ta maida kayan cikin ledar ta yi gefe da su.
Alwala ta d'auro ta gabatar da nafila, ta jima tana addu'o'i kafin ta shafa ta koma makwancinta. Wayar ta k'urawa ido tana jujjuyawa, ta yi nisa cikin tunani wayar ta dauki k'ara.
'Hubbyna.' Shine sunan da ya fito, wani ajiyar zuciya ta saki gami da yin murmushi. Kafin ta dauka kamar yanda ya koyamata yacce zata yi.
Sallama ta soma yi mishi ya amsa.
"Ba ki yi bacci ba, meyasa?"
Ta ji daddadan muryarsa har cikin jini da bargonta.
"Bakomai." Shiru ya dan biyo baya can kuma ya yi magana.
"Ina fatan ba kuka kikayi ba?"
Da mamaki karara akan fuskarta ta girgiza kai.
"Ni..ni banyi kuka ba."
Ya yi murmushi mai sauti.
"Ni kuma jikina ya bani kinyi kuka Ummina, amman dai shikenan. Ya kika ga kayan, sunyi miki ko a chanja?"
'Ni na isa nace basuyi ba?' Ta fada a zuciyarta batare da sanin ya fito fili ba.
"Har kin yi yawa indai awajen Umar Faruk ne. Ni ban ajiyeki nan kusa ba fa. Amma yanzu duk bazaki gane hakan ba sai bayan aurenmu."
Ta lumshe ido tana mai jin wani kaunarsa sabuwa fil a cikin ranta.
"Inama hakan zata faru Yaya Faruk."
Furucin ya yi mishi dadi, ya fahimci ta soma sakin jiki da shi.
"Zai faru in sha Allahu Ummina, ki kwantar da hankalinki har zuwa ranar da Umarul Faruk zai mantar da ke dukkan bakkan ciki da iznin Allah, ranar da zamu kasance mata da miji abin so da alfahari. Matukar ni ne mijinki, bazan k'ara barin ki cikin hali na damuwa ba. Watakil sai kin gaji da ni, don daga ranar da na aureki, na daina zuwa aiki."
Dariya sosai ya bata, sai gashi ta shiga yinta kwarai. Ya lumshe ido gami da k'ara rungume daya daga cikin kananun filon dake saman gadonsa. Shi kadai yasan yanda ya ke jin dariyarta. Ta tsaida dariyar cike da jin kunya. Murya kamar na wanda baya son magana ya ce.
"Naso ace kina gabana kike dariyar nan Ummi, yana daga cikin abinda ban ta6a gani ba daga gareki, kuma zanso na ganin."
Ta sunkuyar da kanta tamkar yana ganinta ta hau wasa da igiyar hular t-shirt din dake jikinta.
"Saida safe Yaya Faruk, bacci nake ji."
"Ko na zo?"
Ta zaro ido kamar yanda ganinta, ya yi 'yar dariya.
"Matsoraciyata, na tabbatar kin tsorata. Shikenan saida safe, kiyi mana adduar fa."
"To."
Daga haka sukayi sallama. Ta bi wayar da kallo tana murmushi. A karshe ta ajiyeta gefe, mikewa ta yi ta yi nafila sannan ta karanta istihara tana kallo a takarda kafin ta shafa ta kwanta.
WASHEGARI....!!!!
Cikin ikon Allah ta tashi da jin kwarin gwuiwa a zuciya da gangar jiki, kaso sitti na damuwarta ya ragu.
Bayan Magriba ya shigo gidan, kai tsaye sashensa ya soma nufa. Bayan ya yi wanka ya nemi Ummi a waya, tana zaune tana harhad'a kayanta sanin da ta yi cewar gobe Asabar kuma a ranar Hajiya ta sanarmata shine na komawarta Kano, wayar ta katseta. Hannu tasa ta dauka, tasan ko waye mai kiran, gabanta na dukan tara-tara ta dauka da sallama. Ya amsa sannan ta gaisheshi.
"Ki shirya Ummi, na dawo ina sama, da zarar na kammala abinda nakeyi zan sauko mu je."
Ji ta yi kamar ta saki fitsari, ta daure ta gyada kai don bakinta ya yi mata nauyi. Shaf ta mance ma waya ce suke yi.
"Ummi, meyafaru kuma?"
Ya tambaya a sanyaye. Sai lokacin ta dan samu ta yi magana.
"Bakomai, zan shirya."
Ya yi murmushi mai sauti.
"Ko kefa."
Daga nan sukayi sallama. Ta yi k'uri tana duban wayar kafin kuma ta ajiyeta.
"Allah ka saukaka mana." Ta fada a fili, tana mai amsawa kanta.
Shigowar Binta ya katseta, ta amsa sallamarta. Binta ta k'araso.
"Naga fa Yalla6ai ya dawo."
Ummi ta yi murmushin karfin hali.
"Munyi waya yanzu, yana nan kan bakansa, yanzun ma cewa ya yi na shirya."
Binta ta jinjina kai.
"Sai ki tashi, hakanan za ki je kedai kiyita addua a ranki."
Ta saka kayan, Binta ta gyaramata fuskarta, ta yi mata daurin dankwali mai hawa-hawa irin na zamani. Ta taimaka mata da sanya dan kunne da sark'an. Sai kuma ta saki baki tana kallonta.
"Masha Allah, wallahi Ummi na k'ara ganin abinda Yalla6ai ya hango wajenki, Ummi bakiyi kalar 'yan aiki ba."
Ummi ta girgiza kai bata iya cewa komai ba don a yanzun ita kadai tasan yanayin da ta ke ciki.
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
65
Mik'ewa ya yi ya koma daki ta bishi da kallo cikin jin wani shauki na kaunarsa.
'Kaico, Yaya Faruk an kusa rabamu.'
Ta fad'a a ranta, jikinta yana bata cewa komai ya zo karshe, watakil harda zamanta cikin zuri'ar tasu gaba d'aya, tasan maganar Antinta ya kusa tabbata wanda ta ce.
'Karki manta matsayinmu awajen mutanen nan, mu 'yan aiki ne, ba su daukemu komai ba face wannan Ummi. Bar ganin suna mana dariya, duk sadda muka bari wasu lamura suka afku ranar zasu tunamana cewar mu kaskantu ne awajensu, ranar zasu tunamana matsayinmu na marasa galihu.'
Hannunsa ta ji saman fatar fuskarta yana sharemata ruwan hawaye. Ta dubeshi, fuskarsa kai ka rantse bai ta6a dariya ba.
"Kinaso muyi fad'a kenan, na tsani nayita nanata magana d'aya. Karki so ki ji yanda nakejin zuciyata idan kina kuka, amma ke naga kamar kin fison damuwata."
Karo na biyu da ta ji tana son fadamishi damuwarta.
"Kayi hakuri Yaya Faruk, saidai gani nakeyi kamar an kusa yimin katanga da kai."
Ya zubamata ido baice uffan ba, hannunsa tuni ya sauke daga saman fuskarta. Can kuma ya soma magana.
"Fata nagari lamiri, ki saka a ranki in sha Allah babu wani abu da zai yanke alak'armu har ya zuwa aurenmu da rayuwar auren. Banaso kina kawo komai a ranki. Yau idan da dama, kada ki rage bacci ki tashi mu yiwa junanmu addua akan Allah Ya za6amana abinda yafi alheri. Kin iya karanta istihara?"
Ta girgiza kai.
"Ban iyaba, saidai ina da Hisnul muslim."
Ya gyada kai.
"Ki yi adduar istihara a yau Ummi, in sha Allah zamu ga daidai a lamuranmu. Ga wannan."
Ya mik'amata wata leda, ta sa hannu ta kar6a.
"Shi nakeso ki saka gobe idan na kiraki a waya, kinji?"
Ta gyada kai.
"Yauwa."
Daga nan ya sallameta ya yi mata rakiya har suka sauka daga matattakala sannan ya tsaya ta wuce.
"Zan kiraki." Ya fada da muryar rad'a. Ta dubeshi ta murmusa ya yi mata alamun (kiss) da baki, a kunyace ta wuce da sauri. Daga haka ya koma sama.
Bayan ya kammala dukkan wasu ayyuka, ya soma duba kyaututtukan da yan uwa da abokan arziki suka ba shi, sai a yau ya samu wannan damar. Turaruka sunfi komai yawa, agogo kuwa kusan biyar ya samu, wasu kuwa kayan kwalam ne har da katina kala-kala. Hankalinsa ya kai ga na Ihsan, yasa hannu ya dauka ya bude. Kamshi ya soma ziyartar hancinsa....!
Wani hadadden agogo ne sai kuma zobe na azurfa. Murmushi ya yi sadda ta ci karo da kati mai dauke da kalaman so. Ya bude ya karanta.
"My friends told me that falling in love would be the most beautiful feeling in the world. After I fell in love with you, I realized that even the most beautiful feeling in the world would look ugly against your love. Frm Ihsan Modibbo."
Ya ta6e baki kadan, ya cigaba da daga sauran katinan, duk kalamai ne na nuna soyayya.
'Ya tabbata tana sona din kenan?' Ya ayyana a ransa kafin ya lumshe ido. Baya fatan shiga matsala saboda ita, a rayuwarsa bai ta6a shaawar kasancewa da kowace mace ba face Umminsa, ta makaro, bayajin zata samu wani gurbi a zuciyarsa, saidai kuma ta dan ba shi tausayi.
Ya dan ja guntun tsaki sannan ya mik'e ya tsallake kayan ya shiga harkar gabansa.