Sashe 103
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washegari suka samu bakuncin Haidar da Intisar, Haidar nan ya bar Intisar suka wuce masallaci tare da Faruk kasancewar juma'a ce, Ummi ta saki jiki da Intisar ganin yanda itama ta saki jiki da ita, daman ta riga da ta kusan kammala girkinta, ta taimaka mata suka karasa tana labartamata yanda rainon ciki ya ke da kuma sanadin kumburin kafafunta. "Kai, mata na fama wallahi, Allah dai Ya rabaku lafiya."
. Cewar Ummi jiki a sanyaye dalilin tunanowa da Ummanta, yanzun ko awane hali Saude suke ciki? Allah Masani.
"Amin kedai, fatanmu Allah Ya bamu mai sauki."
"Amin."
Bayan sun kammala suka dawo falo, suma sallah sukayi sannan suka yi zaman hira, kusan ma Intisar ce mai yin rabin hirar. A haka kuma ta gangaro zuwa ga maganar dake sosa ranta inda ta soma magana.
"Ummi ina neman wata alfarma gareki akan kanwata Ikram."
Saida ta ji gabanta ya fadi batare da tasan dalili ba, ta dafe kirji.
"Gareni kuma Anti?"
Ta gyada kai.
"Kwarai kuwa."
Ta girgiza kai.
"Ai a duniya babu abinda za ku nema na kasa yi gareku matukar baifi karfina ba idan har Allah Ya bani ikon yin."
Murmushi Intisar ta yi. Ta soma labartamata yanda akayi tun farko tasan Ummi na son Gidado har zuwa kadan daga hirarsu kwanaki ta dora da fadin.
"Don Allah Ummi ki taimakawa kanwata, na gaskata tana son Gidado da gaske ba wai iyaka baki ya tsaya ba, nasan kuma wannan jarrabawa ce babba ta iso gareta."
'Anya ba mafarki nake ba?' Ummi ta jefawa zuciyarta wannan tambayar....!!
[2/8, 10:05 AM] +234 803 862 6581: DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
122
Ta kasa gaskata lamarin, gani ta ke yi kamar ba idanunta biyu ba, dafa hannunta da Intisar ta yi ne yasa ta dago kai tana dubanta kamar wata wawuya.
"Kar ki yi wani zargi akan haka, nasan wacece Ikram, wallahi da ace karya ta ke yi da maganar kafin ta iso kunnenki ta ruguje don bazan amince mata ba saidai iyakar gaskiyarta ta nuna kuma ta furtamin na ji."
Ummi ta numfasa kafin ta dora daya hannunta saman na Intisar tana murmushi.
"Anti da ki ke kiran Ikram da kanwarki, nima 'yar uwa na dauketa, ina mata kallon jinina, wallahi ko kusa ba wani zargin nake ba, kawai dai abin ne na ji shi banbarakwai saidai tunawa da na yi Allah Shi ke da wannan ikon, yasa na ji zuciyata ta wanku kuma na kara gaskata faruwar hakan. Na tausayawa Ikram matuka kuma in sha Allahu zan taimakamata, saidai ta saka a ranta shi aure nufin Allah ne, idan Allah Ya yi matarsa ce ita to ba makawa zata zama idan kuwa ba matarsa bace..."
Sai ta yi shiru, Intisar dake kallonta kallo na burgewa tana mai kara jin kaunar halayya irinta Ummi wanda ya sha bamban da mafi yawa cikin mutane ta fadada murmushin.
"Karki damu, munsan komai kaddara ne, in sha Allahu na tabbatar ba za mu ji kunya ba."
Ummi ta murmusa. A kasan ranta ta shiga damuwa, ta ina zata faro? Tasan sanarwa Gidado abu ne mai sauki saidai kuma da wane ido zata dubi Hafsa matarsa? Batasan kalar nata kishin ba, kada fa ta rik'eta a zuciya?
'Komai na Allah ne, zai taimakemu.' Cewar wani 6angare na zuciyarta. Shigowar mazan ne ya katse tunanin kowaccensu, dukkansu cikin fararen kaya, sunyi kyau hakanan kamanninsu ya kara bayyana sai hira suke yi har suka karaso falon. Suka yi musu sannu da zuwa, nan suka zauna, ba kunya Faruk ya zauna kusa da matarsa gami da riko hannunta.
"Ummina na dawo, kinsan addu'ar da na yi mana?"
Kunya ta kamata, Haidar ya ja guntun tsaki yana dariya.
"Daman haka ka ke? Ina maka kallon wani mutum da baisan komai ba, ashe-ashe?"
Faruk ya shafi sumarsa yana taya Intisar dariyar da ta ke yi. Ummi kuwa kanta na kasa tana murmushi gami da kokarin zare hannunta cikin na Faruk saidai hakan ya gagara.
Baice mishi komai ba saima ya sanya bakinsa saitin kunnen Ummi.
"Addua na yi akan Allah Ya bamu twins."
Ai da sauri ta mike ta na fadin.
"Nan za'a kawo muku abinci ko acan za ku ci?"
Su Haidar da ke dariya suka mike yana taimakawa matarsa.
"Ina zamu wahalar da ke? Wannan Angon naki ba shi da ta ido gwara muyi-muyi mu tattara mubar gidannan."
Faruk ya shagwa6e fuska.
"Kai brother."
Cikin dariya Intisar ta dubi mijinta.
"Don Allah ka kyaleshi hakanan." Ta yi maganar cikin kasa da murya don har lokacin ba wani sabo ta yi da Faruk ba, ya ja karan hancinta yana dariya.
"Ke bakisan waye wannan ba da ba zaki tausayamishi ba."
Murmushi ta yi kawai suka rankaya gaba daya wajen tebur.
Bayan gama ci da sha kuma suka dawo falon inda Haidar da Faruk suka wuce sashen Faruk din suka barsu, nan kuma hira sosai suka shiga yi, Ummi ta sake sosai da Intisar wannan karon har suna kyakyata dariya. Sai kara yabawa da halin Ummi ta ke yi, ashe haka ta ke da dadin sha'ani?
Ba su suka bar gidan ba sai yamma, tana zaune itama Faruk ya ce ta shirya su fita. Har tsalle ta yi don murna ta fada daki, mayafi kawai ta dora saman maroon lace din dake jikinta ta sanya takalmi mai tudu mai kalar bak'i da maroon. A kofa sukayi kici6us da gogannata, bai chanja kaya ba, ya karemata kallo, ta yi mishi kyau ta kara haske. Ya shafi gefen fuskarta.
"Bazan gaji da fadamaki ina sonki ba."
Murmushi ta yi cikin jin wani sanyi a ranta.
"Nima haka."
Ya dago ha6anta.
"Kema me?"
Ta lumshe ido tana murmushi.
"Ina sonka."
Ya ji dadi gami da sumbatar le66anta.
"Nagode Ummina, muje ko?"
Yana rike da hannunta suka fita, kai tsaye wajen ice-cream suka nufa, nan suka siya suka yi zaman sha, saidai ko mintuna uku basu yi ba ya kasa jurewa ya ce ta taso su sha a mota, gani ya ke yi kowa a wajen ita ya ke kallo, kusan ma baisan ta fishi murna da hakan ba don kuwa gani ta ke yi yan matan gaba daya na wajen idanunsu akan mijinta suke. Bayan mota suka zauna kamar zai shige jikinta, yana bata tana ba shi, ba zato aka kwankwasa musu gilashi, suka dubi wajen kadan daman suka bude, ya karasa sauke gilas din batare da ya matsa daga jikin matarsa ba, wata budurwa ce sanye cikin kananun kaya kanta ko kallabi babu. Ta daga mishi yatsu tana mishi wani kallo bayan ta dubi Ummi dake gefensa. Irin zaman da sukayi ya nunamata alakar dake tsakaninsu, wato dai matarsa ce. Sai ta ji ta kasa maganar da ke bakinta.
Fuskarsa kamar bai ta6a dariya a duniya ba, ita kanta Ummin fuskarta daure tamau tana jin zuciyarta na wani zafi, ashe haka kishi ya ke?
"Lafiya dai?" Cewar Faruk cikin kakkausar murya. Duk saita daburce, ganinsa dazun yana murmushi ta dauka bazai yi wuyar aminta da ita ba, yanzun kuwa sai ta raina kanta.
"Sorry, na dauka wani face da na sani ne, ashe ba shi bane."
Ya dan daga gira kadan bai kara kallonta ba ya daga gilas ya rufe! Sum-sum tabar wurin gayu na mata dariya.
Ya ja tsaki.
"Mata kenan, sun maida kansu tamkar karnuka."
Ummi dai ba ta ce komai ba, jin shirun ne yasa shi dubanta, ta miko mishi ice-cream dinta.
Ya hada har hannun ya rike ba tare da ya saki ba ya ce.
"Lafiya dai?"
Ta girgiza kai tana murmushin yak'e.
"Bakomai ya isheni ne."
Ta fada tana kokarin danne hawayen da ke son zubomata, duk da ranta ya yi sanyi da irin yanda ya yiwa budurwar nan saidai ta kasa fidda kishin a ranta. Ya gane hakan, ta kuma kara burgeshi, ya juya ya cigaba da shan ice-cream din, cikin kara son zolayarta ya ce.
"Haka fa yan matannan suke tsareni ko a ofis, saidai ni ba ruwana da kowaccensu. Bakiga ma wata ba kyakkyawa da ita.."
Bude kofar da ya ga ta yi ne yasa shi yin shiru, fita ta yi ta dawo gaba ta zauna. Ba tare da ta dubeshi ba ta soma magana cikin rawar murya.
"Don Allah mu tafi kaga Magriba ta kusa."
Baice uffan ba har ya kammala shan ice-cream dinsa, ya goge bakinsa da tissue kafin ya tsallako gaba ya zauna mazaunin direba.
Ya dubeta bayan ya sanya bak'in gilashinsa wanda ke kara mishi kyau.
"Wai ni fushin nan na menene?"
Ta girgiza kai.
"Bakomai."
Ya rausaya kai kawai ya tada motar ya ja, har suka isa gida rediyo ne kawai ke aiki.
Suna shiga ta fada dakinta ta ajiye mayafi sannan ta shiga bandaki ta dauro alwala ganin an soma kiraye-kirayen sallah, shima ganin haka yasa bai bi ta kanta ba saida ya je ya yi alwala ya fice masallaci. Bayan ta idar ta yi ta rokon Allah akan ya sauwaka mata zafin kishin da ta ke ji a ranta game da Faruk. Babu abinda ke tayar da hankalinta face furucinsa na a ofis dinsa ma ana mata na takura mishi. Kenan ma abin dadi ya ke mishi ko? Ai kawai sai ta sanya kuka. Jin motsin mutum ta yi a kofar dakin, hakan yasa ta saurin goge fuskarta. Ya karaso ciki ya zauna a kasa gefen dardumar da ta ke zaune.
"Ni ne ko?"
Ta kauda kai gami da kokarin mikewa, ya ja hannunta ta koma ta zauna suna fuskantar juna.
"Ki yi hakuri, Ummina da ace zasu burgeni da tun kafin na ganki na soki su zan fara so saboda nasha ganin ire-irensu, amman babu daya da ta ta6a kwantamin cikinsu, sam ba su daga cikin kalar matar da nakeson aure infact ma ni ban ta6a son wata ba bayan ke, bana fatan kuma Allah Ya jarabceni da son wata din bayan ke."
Ta ji ranta ya yi sanyi, tasan banda ma abin kishi ina ita ina wani kishi da wasu bayan tasan matsayinta wajen mijinnata?
Ta sauke kanta kasa tana murmushi, abin ya ba shi dariya.
Ranar kam sai a hankali....!!!
"Allah Sarki." Shine furucin da Amina ta yi bayan gama sauraron jawabin Ummi game da Ikram. Amina ta cigaba da magana....!
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
123
. Cewar Ummi jiki a sanyaye dalilin tunanowa da Ummanta, yanzun ko awane hali Saude suke ciki? Allah Masani.
"Amin kedai, fatanmu Allah Ya bamu mai sauki."
"Amin."
Bayan sun kammala suka dawo falo, suma sallah sukayi sannan suka yi zaman hira, kusan ma Intisar ce mai yin rabin hirar. A haka kuma ta gangaro zuwa ga maganar dake sosa ranta inda ta soma magana.
"Ummi ina neman wata alfarma gareki akan kanwata Ikram."
Saida ta ji gabanta ya fadi batare da tasan dalili ba, ta dafe kirji.
"Gareni kuma Anti?"
Ta gyada kai.
"Kwarai kuwa."
Ta girgiza kai.
"Ai a duniya babu abinda za ku nema na kasa yi gareku matukar baifi karfina ba idan har Allah Ya bani ikon yin."
Murmushi Intisar ta yi. Ta soma labartamata yanda akayi tun farko tasan Ummi na son Gidado har zuwa kadan daga hirarsu kwanaki ta dora da fadin.
"Don Allah Ummi ki taimakawa kanwata, na gaskata tana son Gidado da gaske ba wai iyaka baki ya tsaya ba, nasan kuma wannan jarrabawa ce babba ta iso gareta."
'Anya ba mafarki nake ba?' Ummi ta jefawa zuciyarta wannan tambayar....!!
[2/8, 10:05 AM] +234 803 862 6581: DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
122
Ta kasa gaskata lamarin, gani ta ke yi kamar ba idanunta biyu ba, dafa hannunta da Intisar ta yi ne yasa ta dago kai tana dubanta kamar wata wawuya.
"Kar ki yi wani zargi akan haka, nasan wacece Ikram, wallahi da ace karya ta ke yi da maganar kafin ta iso kunnenki ta ruguje don bazan amince mata ba saidai iyakar gaskiyarta ta nuna kuma ta furtamin na ji."
Ummi ta numfasa kafin ta dora daya hannunta saman na Intisar tana murmushi.
"Anti da ki ke kiran Ikram da kanwarki, nima 'yar uwa na dauketa, ina mata kallon jinina, wallahi ko kusa ba wani zargin nake ba, kawai dai abin ne na ji shi banbarakwai saidai tunawa da na yi Allah Shi ke da wannan ikon, yasa na ji zuciyata ta wanku kuma na kara gaskata faruwar hakan. Na tausayawa Ikram matuka kuma in sha Allahu zan taimakamata, saidai ta saka a ranta shi aure nufin Allah ne, idan Allah Ya yi matarsa ce ita to ba makawa zata zama idan kuwa ba matarsa bace..."
Sai ta yi shiru, Intisar dake kallonta kallo na burgewa tana mai kara jin kaunar halayya irinta Ummi wanda ya sha bamban da mafi yawa cikin mutane ta fadada murmushin.
"Karki damu, munsan komai kaddara ne, in sha Allahu na tabbatar ba za mu ji kunya ba."
Ummi ta murmusa. A kasan ranta ta shiga damuwa, ta ina zata faro? Tasan sanarwa Gidado abu ne mai sauki saidai kuma da wane ido zata dubi Hafsa matarsa? Batasan kalar nata kishin ba, kada fa ta rik'eta a zuciya?
'Komai na Allah ne, zai taimakemu.' Cewar wani 6angare na zuciyarta. Shigowar mazan ne ya katse tunanin kowaccensu, dukkansu cikin fararen kaya, sunyi kyau hakanan kamanninsu ya kara bayyana sai hira suke yi har suka karaso falon. Suka yi musu sannu da zuwa, nan suka zauna, ba kunya Faruk ya zauna kusa da matarsa gami da riko hannunta.
"Ummina na dawo, kinsan addu'ar da na yi mana?"
Kunya ta kamata, Haidar ya ja guntun tsaki yana dariya.
"Daman haka ka ke? Ina maka kallon wani mutum da baisan komai ba, ashe-ashe?"
Faruk ya shafi sumarsa yana taya Intisar dariyar da ta ke yi. Ummi kuwa kanta na kasa tana murmushi gami da kokarin zare hannunta cikin na Faruk saidai hakan ya gagara.
Baice mishi komai ba saima ya sanya bakinsa saitin kunnen Ummi.
"Addua na yi akan Allah Ya bamu twins."
Ai da sauri ta mike ta na fadin.
"Nan za'a kawo muku abinci ko acan za ku ci?"
Su Haidar da ke dariya suka mike yana taimakawa matarsa.
"Ina zamu wahalar da ke? Wannan Angon naki ba shi da ta ido gwara muyi-muyi mu tattara mubar gidannan."
Faruk ya shagwa6e fuska.
"Kai brother."
Cikin dariya Intisar ta dubi mijinta.
"Don Allah ka kyaleshi hakanan." Ta yi maganar cikin kasa da murya don har lokacin ba wani sabo ta yi da Faruk ba, ya ja karan hancinta yana dariya.
"Ke bakisan waye wannan ba da ba zaki tausayamishi ba."
Murmushi ta yi kawai suka rankaya gaba daya wajen tebur.
Bayan gama ci da sha kuma suka dawo falon inda Haidar da Faruk suka wuce sashen Faruk din suka barsu, nan kuma hira sosai suka shiga yi, Ummi ta sake sosai da Intisar wannan karon har suna kyakyata dariya. Sai kara yabawa da halin Ummi ta ke yi, ashe haka ta ke da dadin sha'ani?
Ba su suka bar gidan ba sai yamma, tana zaune itama Faruk ya ce ta shirya su fita. Har tsalle ta yi don murna ta fada daki, mayafi kawai ta dora saman maroon lace din dake jikinta ta sanya takalmi mai tudu mai kalar bak'i da maroon. A kofa sukayi kici6us da gogannata, bai chanja kaya ba, ya karemata kallo, ta yi mishi kyau ta kara haske. Ya shafi gefen fuskarta.
"Bazan gaji da fadamaki ina sonki ba."
Murmushi ta yi cikin jin wani sanyi a ranta.
"Nima haka."
Ya dago ha6anta.
"Kema me?"
Ta lumshe ido tana murmushi.
"Ina sonka."
Ya ji dadi gami da sumbatar le66anta.
"Nagode Ummina, muje ko?"
Yana rike da hannunta suka fita, kai tsaye wajen ice-cream suka nufa, nan suka siya suka yi zaman sha, saidai ko mintuna uku basu yi ba ya kasa jurewa ya ce ta taso su sha a mota, gani ya ke yi kowa a wajen ita ya ke kallo, kusan ma baisan ta fishi murna da hakan ba don kuwa gani ta ke yi yan matan gaba daya na wajen idanunsu akan mijinta suke. Bayan mota suka zauna kamar zai shige jikinta, yana bata tana ba shi, ba zato aka kwankwasa musu gilashi, suka dubi wajen kadan daman suka bude, ya karasa sauke gilas din batare da ya matsa daga jikin matarsa ba, wata budurwa ce sanye cikin kananun kaya kanta ko kallabi babu. Ta daga mishi yatsu tana mishi wani kallo bayan ta dubi Ummi dake gefensa. Irin zaman da sukayi ya nunamata alakar dake tsakaninsu, wato dai matarsa ce. Sai ta ji ta kasa maganar da ke bakinta.
Fuskarsa kamar bai ta6a dariya a duniya ba, ita kanta Ummin fuskarta daure tamau tana jin zuciyarta na wani zafi, ashe haka kishi ya ke?
"Lafiya dai?" Cewar Faruk cikin kakkausar murya. Duk saita daburce, ganinsa dazun yana murmushi ta dauka bazai yi wuyar aminta da ita ba, yanzun kuwa sai ta raina kanta.
"Sorry, na dauka wani face da na sani ne, ashe ba shi bane."
Ya dan daga gira kadan bai kara kallonta ba ya daga gilas ya rufe! Sum-sum tabar wurin gayu na mata dariya.
Ya ja tsaki.
"Mata kenan, sun maida kansu tamkar karnuka."
Ummi dai ba ta ce komai ba, jin shirun ne yasa shi dubanta, ta miko mishi ice-cream dinta.
Ya hada har hannun ya rike ba tare da ya saki ba ya ce.
"Lafiya dai?"
Ta girgiza kai tana murmushin yak'e.
"Bakomai ya isheni ne."
Ta fada tana kokarin danne hawayen da ke son zubomata, duk da ranta ya yi sanyi da irin yanda ya yiwa budurwar nan saidai ta kasa fidda kishin a ranta. Ya gane hakan, ta kuma kara burgeshi, ya juya ya cigaba da shan ice-cream din, cikin kara son zolayarta ya ce.
"Haka fa yan matannan suke tsareni ko a ofis, saidai ni ba ruwana da kowaccensu. Bakiga ma wata ba kyakkyawa da ita.."
Bude kofar da ya ga ta yi ne yasa shi yin shiru, fita ta yi ta dawo gaba ta zauna. Ba tare da ta dubeshi ba ta soma magana cikin rawar murya.
"Don Allah mu tafi kaga Magriba ta kusa."
Baice uffan ba har ya kammala shan ice-cream dinsa, ya goge bakinsa da tissue kafin ya tsallako gaba ya zauna mazaunin direba.
Ya dubeta bayan ya sanya bak'in gilashinsa wanda ke kara mishi kyau.
"Wai ni fushin nan na menene?"
Ta girgiza kai.
"Bakomai."
Ya rausaya kai kawai ya tada motar ya ja, har suka isa gida rediyo ne kawai ke aiki.
Suna shiga ta fada dakinta ta ajiye mayafi sannan ta shiga bandaki ta dauro alwala ganin an soma kiraye-kirayen sallah, shima ganin haka yasa bai bi ta kanta ba saida ya je ya yi alwala ya fice masallaci. Bayan ta idar ta yi ta rokon Allah akan ya sauwaka mata zafin kishin da ta ke ji a ranta game da Faruk. Babu abinda ke tayar da hankalinta face furucinsa na a ofis dinsa ma ana mata na takura mishi. Kenan ma abin dadi ya ke mishi ko? Ai kawai sai ta sanya kuka. Jin motsin mutum ta yi a kofar dakin, hakan yasa ta saurin goge fuskarta. Ya karaso ciki ya zauna a kasa gefen dardumar da ta ke zaune.
"Ni ne ko?"
Ta kauda kai gami da kokarin mikewa, ya ja hannunta ta koma ta zauna suna fuskantar juna.
"Ki yi hakuri, Ummina da ace zasu burgeni da tun kafin na ganki na soki su zan fara so saboda nasha ganin ire-irensu, amman babu daya da ta ta6a kwantamin cikinsu, sam ba su daga cikin kalar matar da nakeson aure infact ma ni ban ta6a son wata ba bayan ke, bana fatan kuma Allah Ya jarabceni da son wata din bayan ke."
Ta ji ranta ya yi sanyi, tasan banda ma abin kishi ina ita ina wani kishi da wasu bayan tasan matsayinta wajen mijinnata?
Ta sauke kanta kasa tana murmushi, abin ya ba shi dariya.
Ranar kam sai a hankali....!!!
"Allah Sarki." Shine furucin da Amina ta yi bayan gama sauraron jawabin Ummi game da Ikram. Amina ta cigaba da magana....!
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
123