Sashe 73
Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abubuwa da yawa suka shiga dawo mishi tamkar a mafarki, shi dai yasan sadda aka haifi Ummi da irin kauna da so da ya nunamata har izuwa sadda ya soma tsanarta, karshe kuma yana ji yana gani aka turata aiki ba tare da ya ji ko digon damuwa ba. Daga nan kuwa komai da ya shafi Ummi ya mance, Mariya kadai ya ke yiwa kallon diyarsa.
Me zai cewa Allah ranar da Ya tsaidashi da tambayar amanar da Ya ba shi?
Sai kawai ya soma kuka gami da jawo Ummi jikinsa.
"Ummi ki gafartamin, na yi babban kuskure a rayuwa, na tabbata idan ba ki yafemin ba Allah bazai yafemin ba, na yi watsi da lamuran rayuwarki."
Yana kaiwa nan Yaha kamar jira ta ke ta cafe, tiryan-tiryan ta bada labarin yanda sukayi da Saude akan Ummi na cewar bata kaunar ko kusa ta k'ara takowa Ringim har su hadu da shi.
Ya dago ya dubi Saude da babu inda ba ya kadawa a jikinta tsabar tsoro, cikin alamu na rashin gaskiya ta hau fadan borin kunya.
"Ke Yaha ashe bakar munafuka ce mai shirin kashe auren sunna? Yaushe mukayi haka dake? Inace Malam da kansa ya ce a kaita aikatau?"
Malam Balarabe da har lokacin ita ya ke kallo ya mike yana tunano yanda ta dunga iko da shi har ta rabashi da diyarsa, baisan lokacin da ya cira hannu ya kwasheta da mari ba wanda ya sanyata soma fitsari a wando, kafin ta yi wani yunkurin ya k'ara marinta a daya gefen kuncin. Babu wanda cikinsu ya yi yunkurin hanashi sai Babban Yaya da Ridwan, Faruk kuwa ko gezau baiyiba sai ma wani murmushi da ya ke yi, acikin ransa kuwa godiya kawai ya ke yi ga Ubangiji Ma ji rokon bawa.
Ummi kuwa kuka ta ke yi don ganin lamuran ta ke tamkar a mafarki, tana kukan tana hadawa da dariya. Bata gama mamaki ba sai sadda ta ji marin da Malam ya kwashe Saude da shi.
"Allah Ya isa tsakanina da ke makira! Azzaluma!! Mai fuska biyu!!! Kin cuceni Saude na yi da na sanin aurenki, bana fatan k'ara koda kwakkwaran awa ne tare da ke! Ki ficemin na sakeki! Na sakeki!! Yanda ki ka cuceni ki ka cutarmin da d'iya kema in sha Allah zaayi miki fin haka, duniya ce cikinta muke!!"
Ya dan numfasa kafin ya dora, daidai lokacin wayar Hajiya Babba ta yi kara ganin lambar mijinta ne yasa ta fita wajen cike da tsantsar mamaki da wani mugun tausayin Ummi da mahaifinta.
Malam Balarabe ya nuna Saude da yatsa.
"Hasiya ta daukeki abokiyar zama ba kishiya ba, Hasiya ta bauta miki tamkar kanwarki, abinda Hasiya ta yi miki ko kanwarki da ku ka fito ciki daya ba za ta yi miki ba, yan uwan Hasiya suna miki kallon mutuniyar arziki, ko alheri ne zasu yi, basa ta6a bambantaki da jininsu, ashe ke din da zuciya biyu ki ke tare da su? Da har ki ka kasa rike Ummi riko na gaskiya da amana? Kin cutar da ni! Ni bani da tabbacin ko kina wani abin, amma ina rantsuwa da Allah bansan yanda akayi na kuntata rayuwar diyata ba."
Sai kuma ya sunkuya cikin zubar hawaye wata razananniyar k'ara Saude ta sanya, ta nufi hanyar waje tana fadin.
"Daman Bokanya ta fad'a! Wayyo na shiga uku na lalace!! Allah Ya tsinemaka Balarabe, Allah Ya sa ka gamu da nau'ikan azabobi kala-kala, wayyo ni Saude!!"
Haka ta ke tafe tana surutai kamar wata sabuwar kamu, burinta ta isa ga Bokanya. Mariya zata bi bayan uwarta, Malam ya janyoya a fusace, ta isa ga Yaha tana ajiyar zuciya don ta tsorata yau da babannata.
Hajiya Babba da mijinta suka bi Saude da kallo, ta dubi mijinnata.
"Wannan itace kishiyar uwar Ummin. Bari na shiga na gani."
Gen. Ahmad ya jinjina kai yana mai bin Saude da kallo cike da jimami.
"Baba ni ban ta6a rik'onka a zuciyata ba, duk wani abu da ka yimin na yafemaka, nima ina rokon gafararka har..."
"Kul Hasiya, kar ki ce komai, ni nan ba ki ta6a yimin laifin komai ba, ni ne mai laifin daman. Yanzu kuma tunda gaskiya ta fito, in sha Allahu bazan k'ara aikata makamancin hakan ba."
Dariya kawai ta ke yi tana hawaye, suka hada ido da Faruk ya mikomata hankicif ta kar6a.
"Alhamdulillah, yau ranar sa'a ce. Allah Ya k'ara kauda shaidan."
Cewar Yaha kenan, sai lokacin hankalin Malam ya dawo jikinsa, ya dubi su Hajiya Babba da su Faruk.
"Sannunku, ina wuni."
Nan matasan wadanda mamaki da farinciki ya cika, suka gaisheshi sannan ya juya suka gaisa da Hajiya.
"Saidai ban gane fuskokin ba?"
Ya karashe da duban Ummi fuskarsa cike da fara'a. Itama yau bakinnata ya k'i rufuwa, kafin ta ce komai Yaha ta koro mishi bayanin ko su su waye da kuma abinda ke tafe da su, ta k'ara da fad'in.
"Maigidan ma yana k'ofa tsaye." Jin haka yasa Malam Balarabe mikewa da sauri yana fadin.
"Ya Salam." Daga haka ya fita ya shigo da Daddy soron gidan, bayan sun gaisa.
Tabarma Ummi suka shimfida musu, matasan suka fita waje sai Yaha da su Hajiya a tsakar gidan suna magana kan lamarin Ummi, Mariya kuwa ta yi gum sai kallonsu da ido.
Bayan Daddy ya zauna, suka k'ara gaisawa. Malam Balarabe ya hau mishi godiya sosai da addu'o'i game da taimakonsu ga diyarsa wacce aka so wulakanta rayuwarta.
"Ba komai, wannan yiwa kaine ai."
Cewar Daddy. A karshe ya koro mishi bayanin dake tafe da su. Malam ya yi shiru yana nazari, can kuma ya soma magana.
"Hakika na yi farinciki matukar gaske da wannan magana, sannan na yabawa karamci irinnaku da har ku ka taso daga Abuja zuwa nan don Ummi, tabbas kun kasance cikin mutane masu daraja DAN ADAM, ko don wannan bazan hana Umar auren Hasiya ba. Saidai ina neman wata alfarma daga wajenka Yalla6ai."
Daddy ya gyara zama kadan.
"Ina sauraronka Baba."
"Na yi kuskuren da zan so gyarashi kafin komai ya faru. Ummi da ka ke gani, babu wanda ta sani cikin dangin uwa da na ubanta. Hakazalika ni kaina na manta rabona da zuwa wajen yan uwana. Ina neman alfarmar soma zagayawa da ita muje ta ga dangi idan yaso daga baya sai ayi zancen aurensu. Ina fatan hakan ba zai zamto matsala..."
Cikin 'yar dariya Daddy ya ce.
"Haba Baba, wannan ba matsala bace. Tabbas gaskiya ka fad'i, saidai me zai hana a tsaida lokaci idan yaso kafin zuwan lokacin an zaga dangin?"
Malam Balarabe ya yi shiru, idan ya aminta da hakan tabbas ya kwasowa kanshi aiki babba, yanzu me ya mallaka na aurar da Ummi cikin wadannan mutanen 'yan babban gidan? Ya dan girgiza kai yana duban Daddy.
"Ka yi hakuri Yalla6ai, ni mutum ne da yasan girman alk'awari! In sha Allahu Hasiya bata da miji sai Umar matukar tana sonsa. Ku kwantar da hankalinku, a satinnan in sha Allahu zan wuce da Hasiya."
Cikin gamsuwa Daddy ya jinjina kai.
"Bakomai Baba, hakan ma ya yi, Allah Ya k'ara dankon zumunci."
Cike da jindadi Malam Balarabe ya amsa kafin kuma Daddy ya mik'e.
"Bari mu wuce dare yana yi mana."
Sukayi musayar lambar waya sannan Malam Balarabe ya shiga ciki ya yi kiran Hajiya akan zasu wuce. Ummi ta yi musu rakiya don kuwa ita kanta yanzu zumudin kwana ta ke yi wajen mahaifinta ko ta dandani gatan da ta ke burinsa a rayuwa wanda ta rasa zamanin kuruciya.
Faruk ji ya ke tamkar kada ya tafi, shikenan kuma za suyi nesa da juna? Ya kafamata ido, itama a sace take kallonsa. Gaba daya sai ya bata tausayi ganin yanda jikinsa ya yi sanyi, shi fa gani ya ke tamkar za'a rabasu ne.
Hajiya ta yiwa Yaha kyauta mai tsoka hakanan Ummi itama, suka rabu zuciyoyinsu cike da kewar juna musamman ga masoyan da basu ji tattaunarwar iyayennasu maza ba.
Bayan tafiyarsu suka koma ciki, yaran makwafta sai bin Ummi suke da kallo tamkar tauraruwa. Matan makwafta kuwa wadanda suke jin komai har da dan lekensu don kawai su ga bak'in birni da kuma Ummi. Ai kuwa yara aka yita cika gidan ganin Ummi, da yawansu ma basu santa ba, wadanda suka santa duk sunyi aure a yanzun. Ummi sai hawaye ta ke yi, ta dubi kanwarta Mariya wacce har lokacin ta ke dan kuka-kuka hankalinta na ga mahaifiyarta. Ta jawota jikinta ta rungume.
"Mariya ko?"
Mariya ta gyada kai. Murmushi Ummi ta yi cikin hawaye ta shafi kanta.
"Ni yayarki ce, sunana Ummi."
Jin haka Mariya ta yi kuri da ido tana dubanta, Malam Balarabe dake alwalar sallar Magriba yana duban Ummi diyarsa tamkar ya maidata ciki tsabar so da kauna ta uba da da. Komai na Ummi da murmushinta, sanyin maganarta duk irin na Hasiya mahaifiyarta ne, take ya tsinci zuciyarsa ta cika da kewar Hasiya, matar da aka yi musu auren zumunci kenan don kuwa iyayensu aminan juna ne.
"Tashi ki dora alwala kinji Hasiya. Bari naje masallaci."
Ya fada yana dubanta bayan ya idar da alwala, ta amsa da to tana mai jin ranta tas, bayan fitarsa ta cika ruwa a butan ta soma alwala tana duban Mariya wacce ta makure a lungu, daga sun hada ido sai Mariyan ta dauke kai. Murmushi kawai ta yi don ta tausayamata, rashin uwa ai ba dadi. Yanzun ko ina uwar ta tafi?
*** *** ***
Saude da Habiba gaban Bokanya....
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
90
RINGIM
Me zai cewa Allah ranar da Ya tsaidashi da tambayar amanar da Ya ba shi?
Sai kawai ya soma kuka gami da jawo Ummi jikinsa.
"Ummi ki gafartamin, na yi babban kuskure a rayuwa, na tabbata idan ba ki yafemin ba Allah bazai yafemin ba, na yi watsi da lamuran rayuwarki."
Yana kaiwa nan Yaha kamar jira ta ke ta cafe, tiryan-tiryan ta bada labarin yanda sukayi da Saude akan Ummi na cewar bata kaunar ko kusa ta k'ara takowa Ringim har su hadu da shi.
Ya dago ya dubi Saude da babu inda ba ya kadawa a jikinta tsabar tsoro, cikin alamu na rashin gaskiya ta hau fadan borin kunya.
"Ke Yaha ashe bakar munafuka ce mai shirin kashe auren sunna? Yaushe mukayi haka dake? Inace Malam da kansa ya ce a kaita aikatau?"
Malam Balarabe da har lokacin ita ya ke kallo ya mike yana tunano yanda ta dunga iko da shi har ta rabashi da diyarsa, baisan lokacin da ya cira hannu ya kwasheta da mari ba wanda ya sanyata soma fitsari a wando, kafin ta yi wani yunkurin ya k'ara marinta a daya gefen kuncin. Babu wanda cikinsu ya yi yunkurin hanashi sai Babban Yaya da Ridwan, Faruk kuwa ko gezau baiyiba sai ma wani murmushi da ya ke yi, acikin ransa kuwa godiya kawai ya ke yi ga Ubangiji Ma ji rokon bawa.
Ummi kuwa kuka ta ke yi don ganin lamuran ta ke tamkar a mafarki, tana kukan tana hadawa da dariya. Bata gama mamaki ba sai sadda ta ji marin da Malam ya kwashe Saude da shi.
"Allah Ya isa tsakanina da ke makira! Azzaluma!! Mai fuska biyu!!! Kin cuceni Saude na yi da na sanin aurenki, bana fatan k'ara koda kwakkwaran awa ne tare da ke! Ki ficemin na sakeki! Na sakeki!! Yanda ki ka cuceni ki ka cutarmin da d'iya kema in sha Allah zaayi miki fin haka, duniya ce cikinta muke!!"
Ya dan numfasa kafin ya dora, daidai lokacin wayar Hajiya Babba ta yi kara ganin lambar mijinta ne yasa ta fita wajen cike da tsantsar mamaki da wani mugun tausayin Ummi da mahaifinta.
Malam Balarabe ya nuna Saude da yatsa.
"Hasiya ta daukeki abokiyar zama ba kishiya ba, Hasiya ta bauta miki tamkar kanwarki, abinda Hasiya ta yi miki ko kanwarki da ku ka fito ciki daya ba za ta yi miki ba, yan uwan Hasiya suna miki kallon mutuniyar arziki, ko alheri ne zasu yi, basa ta6a bambantaki da jininsu, ashe ke din da zuciya biyu ki ke tare da su? Da har ki ka kasa rike Ummi riko na gaskiya da amana? Kin cutar da ni! Ni bani da tabbacin ko kina wani abin, amma ina rantsuwa da Allah bansan yanda akayi na kuntata rayuwar diyata ba."
Sai kuma ya sunkuya cikin zubar hawaye wata razananniyar k'ara Saude ta sanya, ta nufi hanyar waje tana fadin.
"Daman Bokanya ta fad'a! Wayyo na shiga uku na lalace!! Allah Ya tsinemaka Balarabe, Allah Ya sa ka gamu da nau'ikan azabobi kala-kala, wayyo ni Saude!!"
Haka ta ke tafe tana surutai kamar wata sabuwar kamu, burinta ta isa ga Bokanya. Mariya zata bi bayan uwarta, Malam ya janyoya a fusace, ta isa ga Yaha tana ajiyar zuciya don ta tsorata yau da babannata.
Hajiya Babba da mijinta suka bi Saude da kallo, ta dubi mijinnata.
"Wannan itace kishiyar uwar Ummin. Bari na shiga na gani."
Gen. Ahmad ya jinjina kai yana mai bin Saude da kallo cike da jimami.
"Baba ni ban ta6a rik'onka a zuciyata ba, duk wani abu da ka yimin na yafemaka, nima ina rokon gafararka har..."
"Kul Hasiya, kar ki ce komai, ni nan ba ki ta6a yimin laifin komai ba, ni ne mai laifin daman. Yanzu kuma tunda gaskiya ta fito, in sha Allahu bazan k'ara aikata makamancin hakan ba."
Dariya kawai ta ke yi tana hawaye, suka hada ido da Faruk ya mikomata hankicif ta kar6a.
"Alhamdulillah, yau ranar sa'a ce. Allah Ya k'ara kauda shaidan."
Cewar Yaha kenan, sai lokacin hankalin Malam ya dawo jikinsa, ya dubi su Hajiya Babba da su Faruk.
"Sannunku, ina wuni."
Nan matasan wadanda mamaki da farinciki ya cika, suka gaisheshi sannan ya juya suka gaisa da Hajiya.
"Saidai ban gane fuskokin ba?"
Ya karashe da duban Ummi fuskarsa cike da fara'a. Itama yau bakinnata ya k'i rufuwa, kafin ta ce komai Yaha ta koro mishi bayanin ko su su waye da kuma abinda ke tafe da su, ta k'ara da fad'in.
"Maigidan ma yana k'ofa tsaye." Jin haka yasa Malam Balarabe mikewa da sauri yana fadin.
"Ya Salam." Daga haka ya fita ya shigo da Daddy soron gidan, bayan sun gaisa.
Tabarma Ummi suka shimfida musu, matasan suka fita waje sai Yaha da su Hajiya a tsakar gidan suna magana kan lamarin Ummi, Mariya kuwa ta yi gum sai kallonsu da ido.
Bayan Daddy ya zauna, suka k'ara gaisawa. Malam Balarabe ya hau mishi godiya sosai da addu'o'i game da taimakonsu ga diyarsa wacce aka so wulakanta rayuwarta.
"Ba komai, wannan yiwa kaine ai."
Cewar Daddy. A karshe ya koro mishi bayanin dake tafe da su. Malam ya yi shiru yana nazari, can kuma ya soma magana.
"Hakika na yi farinciki matukar gaske da wannan magana, sannan na yabawa karamci irinnaku da har ku ka taso daga Abuja zuwa nan don Ummi, tabbas kun kasance cikin mutane masu daraja DAN ADAM, ko don wannan bazan hana Umar auren Hasiya ba. Saidai ina neman wata alfarma daga wajenka Yalla6ai."
Daddy ya gyara zama kadan.
"Ina sauraronka Baba."
"Na yi kuskuren da zan so gyarashi kafin komai ya faru. Ummi da ka ke gani, babu wanda ta sani cikin dangin uwa da na ubanta. Hakazalika ni kaina na manta rabona da zuwa wajen yan uwana. Ina neman alfarmar soma zagayawa da ita muje ta ga dangi idan yaso daga baya sai ayi zancen aurensu. Ina fatan hakan ba zai zamto matsala..."
Cikin 'yar dariya Daddy ya ce.
"Haba Baba, wannan ba matsala bace. Tabbas gaskiya ka fad'i, saidai me zai hana a tsaida lokaci idan yaso kafin zuwan lokacin an zaga dangin?"
Malam Balarabe ya yi shiru, idan ya aminta da hakan tabbas ya kwasowa kanshi aiki babba, yanzu me ya mallaka na aurar da Ummi cikin wadannan mutanen 'yan babban gidan? Ya dan girgiza kai yana duban Daddy.
"Ka yi hakuri Yalla6ai, ni mutum ne da yasan girman alk'awari! In sha Allahu Hasiya bata da miji sai Umar matukar tana sonsa. Ku kwantar da hankalinku, a satinnan in sha Allahu zan wuce da Hasiya."
Cikin gamsuwa Daddy ya jinjina kai.
"Bakomai Baba, hakan ma ya yi, Allah Ya k'ara dankon zumunci."
Cike da jindadi Malam Balarabe ya amsa kafin kuma Daddy ya mik'e.
"Bari mu wuce dare yana yi mana."
Sukayi musayar lambar waya sannan Malam Balarabe ya shiga ciki ya yi kiran Hajiya akan zasu wuce. Ummi ta yi musu rakiya don kuwa ita kanta yanzu zumudin kwana ta ke yi wajen mahaifinta ko ta dandani gatan da ta ke burinsa a rayuwa wanda ta rasa zamanin kuruciya.
Faruk ji ya ke tamkar kada ya tafi, shikenan kuma za suyi nesa da juna? Ya kafamata ido, itama a sace take kallonsa. Gaba daya sai ya bata tausayi ganin yanda jikinsa ya yi sanyi, shi fa gani ya ke tamkar za'a rabasu ne.
Hajiya ta yiwa Yaha kyauta mai tsoka hakanan Ummi itama, suka rabu zuciyoyinsu cike da kewar juna musamman ga masoyan da basu ji tattaunarwar iyayennasu maza ba.
Bayan tafiyarsu suka koma ciki, yaran makwafta sai bin Ummi suke da kallo tamkar tauraruwa. Matan makwafta kuwa wadanda suke jin komai har da dan lekensu don kawai su ga bak'in birni da kuma Ummi. Ai kuwa yara aka yita cika gidan ganin Ummi, da yawansu ma basu santa ba, wadanda suka santa duk sunyi aure a yanzun. Ummi sai hawaye ta ke yi, ta dubi kanwarta Mariya wacce har lokacin ta ke dan kuka-kuka hankalinta na ga mahaifiyarta. Ta jawota jikinta ta rungume.
"Mariya ko?"
Mariya ta gyada kai. Murmushi Ummi ta yi cikin hawaye ta shafi kanta.
"Ni yayarki ce, sunana Ummi."
Jin haka Mariya ta yi kuri da ido tana dubanta, Malam Balarabe dake alwalar sallar Magriba yana duban Ummi diyarsa tamkar ya maidata ciki tsabar so da kauna ta uba da da. Komai na Ummi da murmushinta, sanyin maganarta duk irin na Hasiya mahaifiyarta ne, take ya tsinci zuciyarsa ta cika da kewar Hasiya, matar da aka yi musu auren zumunci kenan don kuwa iyayensu aminan juna ne.
"Tashi ki dora alwala kinji Hasiya. Bari naje masallaci."
Ya fada yana dubanta bayan ya idar da alwala, ta amsa da to tana mai jin ranta tas, bayan fitarsa ta cika ruwa a butan ta soma alwala tana duban Mariya wacce ta makure a lungu, daga sun hada ido sai Mariyan ta dauke kai. Murmushi kawai ta yi don ta tausayamata, rashin uwa ai ba dadi. Yanzun ko ina uwar ta tafi?
*** *** ***
Saude da Habiba gaban Bokanya....
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
90
RINGIM