← Book details Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 116

Sashe 38

Dan Adam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

    Amina da Ummi sune suka taimaka wajen fidda jakunkuna, Ummi a sace sai sharar hawaye take yi don har cikin zuciyarta bata so zaman garin Abuja, ga kuma fargabar kada Faruk ya yi wani abun da zai janyo mutan gidan su fahimci manufarsa a kanta. 
   Haka suka tafi banda Adnan wanda ya ce ko zai koma ba yanzu ba. Mami dai ganin bai gama hucewa ba ne yasa ta kyaleshi. 
    Ummi ta juya jikinta a sanyaye zata koma ciki, Ihsan da suka hada ido harara da dallara mata, Adnan kuws murmushi ya sakarmata.
  "'Yar Abuja." Ya fada cikin tsokana, murmushin yak'e ta yi mishi. Tana shirin barin wajen ta tsinci muryar Ihsan bayan Hajiya Babba ta riga ta koma ciki tana fadin.
  "Rashin dangi ne yasa ta ke yawo daga nan zuwa can, duk dai abin mutum bazai chanja iyaye ba. Kauyen dai da ake gudu nan ne asali."
   Daga haka ta tsinci muryar Adnan yana mata sababi bayan ya kai mata bugu ta kauce. Daidai da su Intisar basu ji dadin abinda ta aikata ba.
  "Bansan halin wa kika biyo ba, don danginmu ba ma wulakanta mutum, muna girmama DAN ADAM daidai gwargwado." Cewar Intisar kenan sannan ta juya ciki ranta babu dadi.
  Haka suka watse suka bar Ihsan cike da k'ara jin haushi da tsanar Ummi a nata ganin duk a kanta akeyi mata hakan. 
    Ita kuwa Ummi duk yanda ta so shigewa daki kai tsaye don kanta da ta ke ji yana sarawa ga kuma wani kuka da ya ke tahomata hakan bai samu ba sakamakon kiran da Hajiya Babba ta yi mata. Ta karasa ta durkusa cikin ladabi.
  "Gani Hajiya."
Hajiya ta dubeta fuska a sake.
"Yauwa Ummi, sai kuma kika ga an barki a wajena ko? To ina so muyi zama na tsakani da Allah da ke, daman na riga nasan da kyawawan halayenki daga bakin Madina, ki k'ara a kan hakan. Gyaranki na dakina ne sai falon sama da kuma wannan na k'asan. Sauran dakunan kuwa suna karkashin kulawar Binta. Girki daman ba aikinku bane da wanke-wanke, kinji ko? Akwai mai yi na kwanaki ma ganin bak'i da yawa yasa nake cewa ku shiga, fatan kin fahimceni?"
  Ummi ta jinjina kai, ranta ko digon farinciki babu sakamakon har lokacin ranta a tsananin 6ace ya ke. 
     "Na fahimta Hajiya kuma in sha Allah zan kiyaye zan kula."
    Hajiya Babba ta ji dadin furucinta ta sakarmata murmushi.
  "Na lura dai ranki bai miki dadi ba akan zaman da za ki yi anan, karki damu, na dan lokaci ne, da zarar na sanya an samomin wata za ko tafo, mai yiwuwa ma tare da su Ihsan."
   Jin an k'ara ambaton Ihsan sai ta ji duk zancen ya gundureta, ta daure ta k'akalo murmushi.
  "Lah bakomai Hajiya, ai can da nan din duk daya ne."
   Daga haka Hajiya ta sallameta. Tana shiga daki ta zube saman katifa, a hankali maganganun Ihsan suka dawo mata kawai sai ta fashe da kuka sosai har tana sheshshek'a. Wannan rayuwa ta soma isarta, Ihsan ta soma kaita bango, abin nata yana neman wuce gona da iri, ko don tana ganin ita din bata da wani karfin ikon da zata kwaci 'yancinta ne? To wane 'yanci ma ta ke da shi a yanzun tunda ba wani babban jigo abin tunk'ahonta wanda zai iya yin wani kata6us akan lamuranta? Kewar mahaifiyarta yafi komai damunta, ko babu komai ta tabbatar ba zata watsar da ita kamar yanda Mahaifinta ya yi ga rayuwarta ba. 
   A karshe dai wani sashe na zuciyarta ya yi ta nusar da ita da muhimmancin Yarda da Kaddara, haka har dai zuciyarta ta danyi sanyi ta mike don d'auro alwalar La'asar.

   Yana zaune saman kujera a ofis cike da dumbin tunani da damuwa, ya daga kai ya dubi agogon bangon dake a ofishin nasu, agogon ya nuna karfe hudu saura mintuna uku, ya ja guntun tsaki gami da dafe goshinsa. Ya san zuwa wannan lokacin sun wuce, tabbacin farin cikinsa ta tafi saidai hausawa sun ce garin masoyi baya nisa, yasan ko yaushe ya yi niyya muddin ranar babu aiki zai iya kai mata ziyara. Saidai zai so matuk'a tafiyar ta kasance babu ita.
  'Akan wane dalili?' Cewar sashe na zuciyarsa, ya runtse ido gami da jingina kansa jikin kujera.

DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR

51
   "Ummi, ina muka kwana a zancenmu na jiya? Abin nufi me kika fahimta da yanayin da muke ji game da juna a zukatanmu?"
  Ta girgiza kai ta daure ta ce. "Babu."

Ya yi wani murmushi.
"Ai nasan zaayi haka." Ba ta ce komai ba, shi kuwa saida ya ja fasali sannan ya cigaba da magana. 
   "Kin sani kamar yanda na sani Ummi, amma mu ajiye wannan a gefe."
Shiru ya dan biyo baya kafin ya dora.
"Bani tarihin rayuwarki idan da hali."

'Rayuwata?' Ta yi tambayar a ranta. Ganin ta yi shiru ya k'ara magana.
"Look Ummi, ki saki jikinki da ni please, ba ma ke ba, ni kaina ban yi sabo da hakan ba, sai kin zauna da Faruk za ki fahimci ko waye shi. Ban fiye sakin jiki da mutane na yi hira har haka ba, da dai cikin brothers na ne ko Hajiyata. So please Ummi ki min alfarmar nan, ki saki jiki da ni, ina so nan gaba ma mufi haka kusanci kinji ko?"  Ya k'arashe cikin rad'a gami da yin murmushi mai sauti, baiwar Allah idanunta suka cika da kwalla, ga samu ga rashi. Tana son abinda ba za ta ta6a samunsa ba don a yanzun da ya ke magana ji ta ke yi tamkar ana k'ara rura mata wutar kaunarsa. Bata ba shi amsa ba face ta shiga labartamasa labarinta iyakar wanda ta sani banda wanda batasani ba kuma bata ta6a samun labari ba, wato na zamantakewar mahaifinta da mahaifiyarta. To mai labarta matan ma ba shiga sabgarta ya ke yi, bai dauketa matsayin 'ya ba.
   Tiryan-tiryan ta ke bashi labari tana yi tana zubda ruwan hawaye har ta kai yanda aka kawota aikatau. 
   Tana kaiwa karshe ta cigaba da kuka mai kona zuciya, ba don komai ba sai tunanin rashin gatanta da kuma na son abinda ba zata ta6a samu ba.
   Tattausan hannunsa ta ji a saman kumatunta yana share mata fuska, baki ta saki tana kallonsa, ba kwayar idanunta ya ke kallo ba, kyakkyawan farar fatarta ta ke kallo yayinda ya cigaba da magana yana murmushi mai kama da yak'e, fuskarsa dauke da damuwa da tausayi.
       "Kinzo inda za'a share miki hawaye da taimakon Allah, idan har Faruk na numfashi, in sha Allah zai zame miki haske a rayuwarki. A yanzu ta bakinki nake son ji."
  Sai lokacin ya dubeta, ita kuwa idanunta a lumshe suke sakamakon yatsunsa da ke akai yana sharemata kwalla. Daidai lokacin kuma ya dauke hannunsa daga kanta. Ummi bugun kirjinta k'aruwa kawai ya ke yi, ita dai bata ta6a jin yanayin nan kan kowa ba sai shi, ta kasa dubansa, anya kuwa zata iya daukar shawarar Antinta Amina? Kai, dole ta dauka don Antinta ba zata cuceta ba.
    "Kin yarda kin amince mu k'ulla alak'ar da zata kai mu ga AURE? Ta wannan hanyar kadai zan iya taimakon rayuwarki Ummina."
    Kamar ta tashi ta ruga a guje ta ke jinta, Faruk dama ya muryarsa ta ke wajen sanyi kamar mace ballantana kuma yana cikin yanayi na shaukin so da kauna. Ta dan matsa don rage kusancin da ya yi mata. 
    "Kayi hakuri, ni babu wani abu da nake ji game da kai, ban dauke ka komai ba sai dan uwan Yaya Adnan kuma iyayen gidana, ka yi hakuri, bazan iya jefa zuciyata cikin abinda zan wahala ba."
   Daga haka ta kwashi wayoyinsa ta mik'a mishi, saidai ba shi da niyyar kar6a, asalima idanu ya zubamata yana murmushi. Ganin haka yasa ta ajiyewa a kujerar da ta mik'e zata tafi.
  "Ji mana."
  Ta tsaya cak gami da juyowa. Ya dauke wayoyinsa ya dubeta.
"Dawo ki zauna."
   Ba musu ta dawo ta zauna tana share hawayen saman fuskarta.
  Ya dawo ta gabanta ya durkusa. 
"Hey, kalli tsakar idanuna ki ce ba ki amince ba."
  Ta kauda kanta tana jin tamkar ta fashe da kuka gaba daya ita ta gama tsorata ganin Faruk dagaske ya ke babu wani sassaunci. 
    "Ummi say something please, ki ce wani abu mana."
   Ya fada cikin shagwa6a66iyar muryar da bai fiye amfani da ita ba sai ko a gaban Hajiyarsa. Ta girgiza kai.
  "Ni ban amince ba."
  Ya dubeta na sakanni ya na murmushi.
  "Dagaske ba ki amince ba?"
Ya fad'a yana mai kwaikwayon muryarta, abin ya so bata dariya ta kuwa saki murmushi.
  "Masha Allah, ko kefe. Naji wannan kuma nagode, amsa tuni na sameshi, hirar ce nakeson muyi don bakisan yanda nakejin dadin ganinki bane."
  Shiru babu wanda ya k'ara magana, can kuma ya sauke ajiyar zuciya ya kunna wayoyinsa. 
  "Goma har ta kusa."
  Ya fad'a yana duban wayar, can kuma ya mik'e ya sanya wayoyin a aljihun wandonsa, ya yi amfani da tafukan hannayensa ya dafa gwuiwarsa gami da sunkuyowa yana dubanta.
  "Saida safe."
Ta gyada kai sannan ta gifta ta mike tsaye da sauri don daman tun dazu ta soma jin tsayuwar motoci a harabar gidan ta tabbatar yanzun su Mami sun iso. 
   "Allah Ya tashemu lafiya."
  Daga haka ta yi gaba da sauri, koda ta isa ga kofar saida ta kasa jurewa ta juyo kanta ta dubeshi, shi ba shi ma da niyyar barin wajen don komawa ya yi ya zauna. Su ka yi ido hud'u da shi, ta dauke kanta da sauri-sauri ta bar wajen tana ji yana fad'in.
  "Ko na zo ne?"
Bata ko juyo ba balle ta tanka mishi. Ya yi murmushi karo na ba adadi sannan ya kwantar da kansa jikin kujera, kai tsaye hotonta ya lalubo wanda ya yi mata a wata rana da ta ke zaune tana wanki a (garden) da kuma na zanen da ya yi mata.
  "Ke tawa ce in sha Allah."
DAN ADAM
@RUFAIDA OMAR
Chapter 38 · 0% Book details