← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 99 OF 146

Sashe 99

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*Masu bu'katar kayan gyara na chadi gangariya, su yi mini magana. 08032773332*
Amma da yake Yaya Ummi yar'uwa ce ta gaske sai da ta bani kayan nan duka. Kazar ma ta ce zata daho mini idan na kusa arba'in. Cikin dabara na kirgi ku'din da na samu a barka na sawa y'arta mai d'an dama a aljihunta.
A haka na kwashe sati hud'u da haihuwa. Tijjani ya fara rawar kai da son na koma gidanmu haka nan. Tunda na warware.
Idan ya fara wannan maganar shiriritar da ita nake yi.
Da safe an yiwa yara wanka suna ta barci tamkar basu ne masu kwana ido biyu suna kuka mai tsananin gaske ba. Amma da gari ya waye ba za'a sake jin motsinsu ba. Yini suke suna barci.
Ranar da muka yi kwanaki talatin ya iso daga Bauchi. Ya zaune kan sallaya a tsakar d'akin Gwaggo. Ya ci abincin da aka kawo masa. Ya kalle ni ya ce "Little ki girmama al'kawari. Ba irin cika bakin da baki yi mini ba akan idan kin haifi namiji suna na mussaman zaki saka mini. Cikin ikon Ubangiji kin haifo har biyu amma har yau ban ji sunan nawa ba. Anya kin yi daidai kuwa?"
Na dauke kai ina murmushin kunya. Tare da ce wa "gaggawa ne da kai. Ka bari sai mun koma gidanmu zan fara fa'da maka."
Ya yi murmushi ya ce "Gaskiya na matsu fa'da mini na ji kawai".
Na yi dariya na yi shiru.
Ya zuba mini ido sosai ya ce "So nake ku koma, mu yi kwanaki ka'dan kafin mu fara ha'da kayanmu. Kin san mun kusa cika wa'adin kudinmu. Bazan sake biya ba. Idan na samu dama a Bauchi nake son na samu k'aramin gida mu koma can. Zirga zirgar zata mini yawa ga tsadar ku'din mota. Zan fa'da wa su Baba zamu k'aura zuwa Bauchi."
A sanyaye na ce "Allah ya k'ara budi."
Domin na shiga zullumin yadda zan rasa jama'ar da nake da ita, tunda bazan samu jama'a a Bauchi kamar yadda na yi shura a Toro ba.
Ya ce "Ameen Asiyata! Amma fa ban bar waccar maganar ba.
Dai-dai lokacin Haneef ya fara kuka da alamun razana ya yi. Da azama ya dauko shi, ya shiga tofa masa addu'a. Sai kuwa ya yi shiru. Ya bu'de idonsa kirr yana kallon Babansa. Da murmushi Tijjani ya ce "Halo Babana, how you doing today?"
Na murmusa na ce "Kana jiran amsa ne?"
Ya ce "ko bai amsa ba, ya ji ni. Yasan yana tare da Babansa ba ki ga ya yi shiru ba?"
Na ce "Hakane".
Daga hakan ya tsoma hannu a baki ya fara tsotso.
Tijjani ya ce "shima shan hannu ya fara?"
Na ce "Eh! Shi ne ma yake yi kawai. Hamim din da ya fara, yanzu ya gane nono, baya yarda ya sha hannu, wannan yafi shi hakuri".
Ya d'aga shi ya ce "To ba shi ya sha kada a dinga amfani da hakurinsa ana barinsa da yunwa."
Na karb'e shi na gyara na fara shayar da shi. Tijjani ya tsura mini ido yana kallon yadda k'irjina suka cika, suna tsaye tunda k'ananu ne.
Ya kasa hakuri ya dauko Hamim da yake barcinsa ya ce "Ka ji Momi ta ce "Ba ka da hakuri. Baban Marina da ka ci sunansa kuwa hakurinsa mai yawa ne".
Shi bai bu'de ido ba. Barcinsa kawai yake yi.
Ya ce "Ta shi kai ma ka sha".
Na ce "kana shigowa, ina kwantar da shi. A koshe yake."
Ya kankace ido ya ce "Ba kya kewata ko little?"
Na ji kunya irin sosai. Na kawar da fuskata ba tare da na ce kanzil ba.
Ya yi kasa da murya ya ce "Na yi matu'kar gajiya. Na matsu sosai".
Na kasa amsa masa.
Ya sake ce wa "Yaushe Baba ya ce zaki koma?".
Murya babu amo na ce "idan mun yi arba'in mana. Ai yanzu ma saboda kukan yaran nan ne ya barmu da ana yin sati uku zai tattaramu."
Ya nisa ya ce "Idan ta kukansu ne ai zan iya da su Asiyata."
Na yi dariya na ce "baka san kalar kukan da suke yi ba ne."
Ya ce "Da gaske nake yi miki, zan bar komai na ji da su. Kinsan yadda nake jinsu a raina kuwa?"
Na girgiza kai na ce "Ina zan sani? Amma ni da su waye a gaba?"
Ya tillike da dariya sosai ya ce "Yanzu kishin ki har da y'ay'an ki Asiya?".
Na cuna baki na ce "Yo daga tambaya sai ka hau sarhutu".
Ya murmusa ya ce "Yaushe zasu fiki, to wa ya haifa mini su?"
Na murmusa ka'dan.
Ya ce then fa'da mini sunan da kika ce".
"Oh Allah! Bari na fa'da maka tunda kai gajen hakuri gare ka. Baban 2. Shike nan?"
Da'di ya kama shi, ya washe baki dukkan hak'oransa suka bayyana ya ce "Na gamsu da suna na mussaman ne. Ke kuma Maman 2?".
Na juyar da fuska ina murmushi na ce "A a ni ba Mama ba ce."
Ya ce to me ce ce?"
"Yaya".
Ya sake cewa wanne irin Yaya kuma?. Ko da yake tare zaku taso tunda kin yi haihuwar wuri. Amma dai su ce miki Ammi tunda ba kya son Mama".
Na ce "To."
Su Hanif basu bar kuka ba sai da muka kusan arba'in. Kafin lokacin kuwa sun yi girma na ban mamaki tamkar sun yi watanni biyu. Amma tunda ana fa'din da Bulkachuwa suke kama dole su yi girma.
Ana jibi zamu yi arba'in Baba ya ce a shirya ni, domin ranar da na cika arba'in zan koma dakina.
Haka Gwaggo ta hau shirya mini kayanmu, tana ha'de su waje guda. Sannan k'anwar mahaifiyarta ce zata zo ta zauna ta taya ni rainon tagwaye har su dan yi k'wari.
Ranar da muka yi arba'in tun da sassafe Tijjani ya zo daukarmu, ko kunyar su Baba baya ji.
Baban kuwa bai yarda ya tafi da ni ba. Kayanmu dai ya yi ta diba yana kaiwa. Mama Baba ya ce ta rakamu, bayan ya dauko shatar mota ta fara kaimu asibiti a yiwa yara allurar rigakafi. A cewarsa baza mu hau mashin da jinjirai a kwasar musu sanyi ba.
Mamah ta tab'e baki ta ce "Alhaji da alamu dai y'ay'an Yabi sun zarta na kowa daraja a wajen ka".
Kai tsaye ya ce "To ai su tudu biyu suka ci, kin san Tijjani ne ubansu. Jikokin Hauwa ne fa".
Takaici ya kume ta ainun.
Ni kuma na dinga mata kallon ko sai yaushe zata daina Bak'ar Ta'adar rashin ri'ke girmanta. A shekarun ta ai ta wuce ta dinga irin k'ananun maganganu marasa kan gado. Wanda babu azanci a cikinsu sai tarin k'yashi da hassada.
Akan dole ta raka ni, a asibitin duk inda muka wulga sai an yi sha'awar tagwaye tare da yi musu addu'a. Wajen goma da rabi na safiya muka gama da asibitin sannan muka zarce gidan.
Muka tarar da gidan a gyare tamkar ina ciki. Ban yi mamaki ba domin ya riga ya saba da gyaran gida.
Jimawa ka'dan ta yi mini sallama tabi motar ta tafi abin ta.
Tijjani ya tisa ni gaba da rawar jiki. A sanyaye na ce "Duk gajiyar asibitin da na sha. Ka bari mana dare ya yi".
Ya hau jijjiga kai yana fa'din "Ba zan iya ba. Na yi hakuri Asiya! Ke ma kin sani. Kawai ki bani hadin kai. Da daddare rainon twins zan yi, ke kuma ki yi barcinki son ran ki".
A hankali na ce "Dama dai ba Baban 2 ba ne".
Ya yi dariya ya ce "me kika ce?"
Na girgiza kai tare da cewa "Ban ce komai ba".
Ya mikar da ni, ya ja ni zuwa d'akin. Na yi turus ganin su Hamim kwance akan sabuwar katifa madaidaiciya daga gefe. Hakan ya saka dakin ya cike. Na zuba ido ina kallon yadda ya shimfida zanen gado sosia, su kuma ya jere su, duk da akwai tazara a tsakaninsu. Na ce "wannan katifar fa?"
Ya ce "Tasu ce. Tunda ba ni da halin siya musu gado, shine na siya musu katifa. Kinsan ba yarda zan yi su dinga shiga tsakiyarmu ba. Can ne makwancinsu. Idan sun yi kuka zan koma na kwanta a cikinsu".
Na yi k'aramar dariya ban ce komai ba.
Ya ja ni jikinsa ya rungume tsam tsam yana shakar kamshin jikina. Al'amarin da ya biyo baya ba mai sau'ki ba ne. Na gamsu ya yi kewata, na kuma gasgata shi da ya ce a matse ya ke. Duk yadda na takura a dalilin yadda kayan chadi suka saka na matse, na daure na bar shi ya samu nutsuwa.
Shi kuma sai fa'din "anya ba cs aka miki ba little? Ni ban ji alamun tana nan twins suka fito ba".
Ni dai ban bude baki na ce masa uffan ba, amma ni da kaina na gasgata kyaun saiwowin da na yi amfani da su. Na ji dadin maganin sanyin da na sha ba ka'dan ba.

*Domin samun naku kayan gyara na mussaman, ko maganin sanyi sadidan.*
*SAIWOWINE da ake kawo su daga Chad da Sudan gangariya. Ku tuntu'be ni a kai-tsaye ta manhajar WhatsApp*
08032773332.

*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*IDAN KUWA KINA SON YIN RIGISTA DAN FARA KASUWANCIN KAWAI KI TUNTUBETA DAN KUWA DA KYAKKWAR ZUCIYA ZATA MU'AMALANCE KI*
*07039269802*

*Annur food Delicious Nig*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*

*Wannan page din tukuici ne ga masu comments akan littafin BAK'AR TA'ADA*
Chapter 99 · 0% Book details