← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 146

Sashe 35

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Tirk'ashi
Karshen littafi na d'aya.

*Gaba'daya wadannan shafuka shimfida ne dan ku fahimci labarin da kyau, asalin labarin da turka turkarsa yana littafi na biyu da na uku*
*Bisa soyayyar da kuke yiwa rubutuna ya sanya zan yi muku tsarin VIP.
*In Sha Allah babu jira.
*Babu posting ranar Lahadi*
*Sau biyu za'a yi posting a rana*.
*Ku zo mu yi tafiyar da babu nadama*
*Zaku dara, zaku koka, jikinku zai tsumu, zuciyoyinku zasu motsu. Tunani kuma zai tafi cancanken me zai faru a gaba*.

*Marubuciyar HALIN YAU da SABO DA KAZA*
*Yanzu kuma alk'alaminta yana tafe da BAK'AR TA'ADAH*

*500regular page*
*VIP 1k twice pages*
*2384876855*
*Surayya Ibrahim Dahiru*
*Zenith Bank*.
*Ko*
*7061488065*
*Surayya Dahiru Ibrahim.*
*Opay Bank.*

*08032773332.*

*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*OK NA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*07039269802

*Surayya Dee*
*Yar mutanan Gwaram*

✍️

*WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE, BIYA KUDIN KARATUNKI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*

*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.

*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.

Cikin kasala irin wacce b'acin zuciya ke sababa wa, Baban Marina ya ce "waye kuke ganin ba zai auru ba, tamkar Yabina! Wane ne shi?"
Hatta Dada jikinta ya yi lubus da Baban Marina ya ce Yabinsa a akan idon ta da na y'anuwansa. Wanda hakan na alamta ce wa ya kai makura wajen kawaicin da yake yi amma ba'a yi masa kara.
Daga Baban Tsakiya har na Kasuwa ba wanda ya iya cewa kanzil domin sun shiga yanayi na jin nauyi da borin kunya.
Sun fahimci fishin da yake shinfid'e a fuskar yayan nasu ya tunbatsa.
Sai suka yi dabarar kame wa daga jaye jayen maganar.
Bai sake jiran komai ba, ya mike tare da yiwa Dada sallama ya fice.
Yana fita Baban Tsakiya ya ce "Muna cikin wani irin kalubale a wannan duniyar.
Ace ba dama ku tattauna da dan-uwanka ya fahimce ka, shike nan sai ya zama sanadin tabarbare war al'amura?"
Ya yi k'wafa mai nuna takaicinsa muraran.
Baban Kasuwa yana bu'de baki sai ce wa ya yi "To ai irin wannan al'amarin wuya ne da shi. Tuni Ubangiji yasan al'ummar Manzonsa zamu riski wannan zamanin shi yasa ya saukar mana suratul Yusuf dan ta zama izina ga masu hassada da k'yashi. Ta kuma zama gargadi ga masu hankali.
Wani abin kaicon ma mu babu y'an uba a cikinmu, amma babu yadda za'a yi a ha'du a yi hira da walwala cikin farin-ciki saboda kawai ka fi mutum haske?
Gaskiya zan fa'da miki Dada.
Tunda ke kin isa da shi, ba wanda ya cancanci Yabi sai Tijjani, su rufa wa junansu asiri, shine kuma zai iya biyar da ita, ya yi maganin shak'iyancinta".
Baban Tsakiya ya numfasa ya ce "Tunaninmu d'aya Iliya, sai dai ba lallai ne ya amince ba.
Tunda duk iyashegenta bai yarda ja'irar yarinya ba ce. Zai yi wahalar gaske ya ba shi tunda shi lalacewarsa ta bayyana a gida da dawa.
Ita kuwa mu na kusa ne muka fahimta kawai".
Dada ta saki ajiyar zuciya ta ce "Idan haka ta faru kuwa ina da yakinin mai sunan manya zai nutsu domin komin ginshirarsa ba zai kushe ta ba.
Ubangiji ya kyautata halittarta, gata yar shawalwala da zata da'de tana cin zamaninta".
Suka gintse fuska suna fa'din "Kyaun hali da tarbiya ai sune kyaun mace Dada."
Kawai dai ki sanya baki a ba shi ko ma sarara, domin idan shine mijinta zai karya dukkan lagonta."
Basu tashi ba, sai da suka tabbatar ta gamsu bawa Bulkachuwa auren Yabi fa'ida ne mai yawa a garesu bakid'aya.
Baban Tsakiya ya fi kambaba lamarin, a zuciyarsa kuwa so yake a yi a yi a auren ta tunda kusan kullum sai ya yi mafarkin Jabir ya bijire masa ya aure ta.
Sun ki kwamishina ne dan kada haske ya shiga k'ofar dan-uwansu, tunda sun tabbatar nagartacce ne, basa son ya'yansa su yi k'arfi.
Sun fi son a ce su da y'ay'ensu sune masu fa'da aji.
Auren Bulkachuwa kuwa sun san ba wani fiffika da y'ar iskar yarinyar nan zata yi musu.
Tunda a bayyane yake matu'kar mace bata samu miji na gari ba to rayuwarta ta na'kasa.
Washagari da sassafe Baban Marina ya yi sallamah ya ce ya tafi Azare.
***
Na fito sanye cikin uniform, na isa mashigar zauren Dada dan gaisuwa da kuma biya wa Nasiba. Sai na ji magana k'asa kasa daga dakin Bulkachuwa.
Na kasa kunne dan na ji me yake fa'da.
"Bazan sake turo kowa gidanku ba Bilki. Na yarda ki na sona, amma kuma ai ba zaki iya aurar da kanki ba, dole sai da wakilcin iyayen ki. Kema kin san ina sonki, amma tabbas bazan sake turo kowa da zummar a nema mini aurenki ba".
Na yi fakare, jikina ya yi laushi akan abin da na ji.
Waton ba karamin son Bulkachuwa y'anmata suke yi ba.
Bansan me yasa shi kuma yake da jarumtar juya wa soyayya baya ba, matu'kar aka nemi muzanta shi.
Na tsinci kaina da fa'din "Ina ma irin zuciyar Tijjani nake da ita?" Da tuni na yi watsi da tunanin Jabir da soyayyarsa.
Amma ina! Har yanzu ina jin sonsa, kawai na danne ne dan babu yadda na iya.
Na shiga cikin gidan na tarar da Nasiba ta shirya.
Na gaida Dada kamar yadda na saba.
Sai dai amsa mini da ta yi, ya banbanta da sauran watannin baya. Domin tunda kwamshina ya bayyana mini, da karsashi take amsa mini gaisuwa ta.
Amma a yau cikin wani irin yanayi da na kasa tantace wa.
Sai kuma ta zarce da fa'din "Wanda duk ya yiwa mahaifinsa biyayya ba zai tab'e ba. Ina da tabbacin ko wuta na rura na ce da tsohonku ya shiga zai fa'da ne kawai babu tambihi.
Ina rokonku ku dinga yi masa biyayya, ku yarda ya isa da ku, mussaman ke Yabi da tun shekarar da kika iso duniya ya shiga cikin tala jaurar duniya".
Ta fa'da kuka na subuce mata.
Jikina ya mutu murus a dalilin kalamanta, tunanina ya shiga canke canken akwai al'amarin da zai biyo bayan wannan jirwayen na Dada.
Muna tafe da Nasiba duk uban maganar da take yi mini akan Bulkachuwa na kasa ce mata uffan.
A dalilin zuciyata ta riga ta baci da yadda Dada ta ce wai tunda na iso duniya ubana ya fa'da cikin ibtila'i.
Na sani ba yau ake fa'da ba, Mama ta sha fa'da mini ni din tauraruwa mai wutsiya ce, haka ma ya'yanta su Yaya Indo.
Tun ina damuwa har na zo abin ya daina damuna, domin Baban Marina bai ta'ba yi mini wannan izgilancin ba.
Amma a yau sai na tsinci kaina da jin ciwon furucin Dada kwarai da aniya.
Na dinga hasashen me ya janye mini alfarmar da na a samu y'an watannin nan a idonta?
A daren ranar Babanmu ya zaunar da ni da matansa ya fa'da mana aurena da Alhaji ba zai yiwu ba, bisa wani dalili da bai bayyana mana shi ba.
Ya je shi da Alhaji Tanimu sun bashi ha'kuri. Ya gamsu sun yi masalaha, duk da ya shiga rud'ani sosai.
Ya kuma ce ya yafe duk hidimar da ya yi.
Jikina ya mutu, zuciyata ta tsinke.
Na kasa bu'de baki na yi magana.
Ya sallami matansa suka bar ni da shi.

*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATTUN SAIWOWI NA MUSSAMAN KUMA GANGANRIYA DAGA CHADI*
*IDAN KINA DA KANWA KI DIYAR DA ZAKI AURAR TO KI ZO KI JARRABA WADANNAN KAYAN DA BABU ASARA KO ALGUS A CIKINSU*.
*SANNAN KE MA DA KIKA KWANA BIYU A DAKI AKWAI BUKATAR KI SABUNTA KANKI*
*AKWIA SAIWOWIN SANYI*
AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR KAZA*
*AKWAI SAIWOWIN DAHUWAR TATTABATU*
*AKWIA SAIWOWIN TSUMI*
*AKWAI PACKAGE DIN MAGANIN SANYI SADIDAN*
*AKWIA PACKAGE DIN AMARYA*
*AKWAI PACKAGE DIN MAIJEGO*
*AKWAI KAYAYYAKIN MASU INGANCI A FARASHI MAI RAHUSA*.
*AKWAI GORAN TULA SYRUP*
*AKWAI GORAN TULA FRUIT*
*INA AIKAWA KO WANNE GARI A FAD'IN TARAYYAR NIGERIA*
*, SO SU MINI MAGANA TA WANNAN LAMBAR 08032773332*
*DAN ALLAH SERIOUS BUYER'S*
Chapter 35 · 0% Book details