Sashe 131
Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
95&96.
*HAJIYA HANNE ADO ABDULLAHI?*
*MARUBUCIYAR WANKA DA GARI DA KUMA WACE CE UWA?*
*KUN TUNA IRIN BAJINTAR TA AKAN RUBUTUN ADABI DA TARBIYA?*
*TO ITA MA TAKANAS NA SAMO MUKU LITTAFANTA DOMIN KUN SANI TA YI RUBUTU MASU MA'ANA*.
*LITTAFAN DA YAWA, AMMA AKWAI DISCOUNT DOMIN SO NAKE KU YI TA SIYAWA Y'AYA'NKU DA KANNENKU LITTAFAI MASU DARASI DA MA'ANA*.
*INA MUKU ALBISHIR AKWAI DUKKAN TSOFAFFIN LITTAFAN MARUBUCIYA HAJIYA SALIHA ABUBAKAR ZARIA*
*ZAKU SAME SU SOFT COPIES, A HANNUNA*
*SANNAN SABO DAL NA KAN HANYA*
*HAKA NAN AKWAI WASU DAGA CIKIN LITTAFAN MARUBUCIYA HAJIYA HAFSAT C SODANGI, SUMA SOFT COPIES KAZALIKA ITAMA SABON LITTAFIN TA MA KAN HANYA*
*BA DA JIMAWA BA ZAN ZO MUKU DA SU*.
*08032773332*
*INA MATUKAR GODIYA BISA ADDU'ARKU DA KUMA KAUNARKU GA RUBUTUNA*
*WANNAN SHAFIN SADAUKARWA NE TARE DA GODIYA GA DUKKAN WADANDA SUKA SAKA KUDINSU SUKA SIYI WANNAN LABARIN DON JADDADA MINI SOYAYYA DA KUMA KARFAFA GUIWA*
*NA GODE, NA GODE*.
Auren Aliyu ya samu tasgado. Ba akan komai ba sai akan an kai suka gidansu amaryar cewar d'an-uwansa dan safarar kwaya me gwamnati ta rufe shi Shima ana kyautara zaton yana da BAK'AR TA'ADA. Muna ji muna ga ni aka hana Yaya Aliyu aure ba a akan laifinsa ba. Dama Kuma Babaiba son inda ya dauko auren ba, yar babban attajirice. A raina na Jin ciwon yadda mutanan yau suke yiwa mutane hukunci da laifin yan'uwansu ko na dangunsu alhalin Allah da kansa baya bawa da laifin mahaifansa bare kuma laifin d'an-uwansa. A zuciyata tamkar na ce masa ya nemi Iklima da a yanzu take kwalejin koyon aikin jinya da ke Azare, tana shekarar karshe. A kansu a aka zurfafa karatu ba tare da aure ba a gidanmu. Sun kammala sakandire babu samarin aure. Hakan ya sanya Jabir samowa kannensa gurbin karatu a inda yake koyarwa. Gabadaya mun tafi a cewa iyayensa suka hana ya had'a da ita. Hakan da muka gani ya sanya ni da su Yaya Salisu muka yi kundubalar saka Iklima a Health Technology Azare.
A tsaye take cak, doguwa mai cukar halitta kuma fara tas. Na tabbatar ba zai tankwabe ta ba, amma ina jin tsoron na furta.
Dan haka sai na tsiri gayyato ta hutu a karshen watan da na tabbatar yana yi mana jele. Akai akai suke haduwa kuwa. Su yi ta cakar juna tunda shi ma mai zolaya ne. Ni kuwa na dinga fad'in "um um fa Yaya Aliyu kada fa reshe ya juye da mujiya."
Wani lokacin ya yi dariya ya waske, wani lokacin kuma ya ce "Ba Wani reshe da zai juye, yarinya kankanuwa, raini dai nake son jawo masa.
Baba kuwa idan ta ji ya ce haka sai ta ce "Saboda ka kallafawa ranka son ka auri sa'aninka. Ban da haka ai itacw daidai da kai ".
A duk sadda Babah ta fad'i hakan dad'i ne yake matukar kama ni. Ina ganin nasara a kudirina.
Matukar yana gidan ita zan saka ta yi masa girki, ta dafa masa zobo. Wani lokacin ya yi godiya ya kwashi girki. Wani lokacin ya ce "Tunda na zama matar yayansa na ture girme mini da ya yi, nake mu'amalantarsa a matsayin k'anina. Ban da haka me yake hana ni na yi masa hidima da kaina sai na saka yarinya ta yi masa."
Na yi dariya na ce "Yaya Aliyu ko a lahira wani na cin arzkin wani ai"
Ba'a d'auki lokaci mai yawa ba ya fara fad'awa tarkonmu. Domin idan ya zo bai ganta ba, ya dinga tambayar me ya hana ta zuwa. Ko ba hutu suke yi ba, da sauran tambayoyi. Da na fahimci hakan kuwa sai na dakatar da zuwan nata. Domin so nake ya taka ya neme ta a inda take ba wai sai ya ganta dan ya zo ba.
Ilai kuwa wanne tudu wanne gangare ya silala yake zuwa daga haka har suka had'a kansu.
Tunda aka garkame Tijjani ban yi farin ciki har zuciyata ba sai akan wannan al'amarin. Domin dai Na tabbatar Aliyu mutumin kirki ne. Sannan Babah uwace ta gari bayan haka Ikilima zata auri mai rufin asiri. Zamu sake zargowa k'ofarmu wani hasken.
Bugu da kari y'aya'nmu zasu kasance cikinsu guda. Tunda shi da Tijjani daya ne, haka ni da ita.
Da maganar ta fasu a gidan Marina a lokacin da iyayensa suka je nema amsa aurenta. Ba abin da ba'a ce ba. Bak'in ciki muraran har ce wa aka yi ai k'aramin likita ne, wasu kuwa cewa suka yi ba ma likita ba ne. Malamin tsafta ne. Shi dai Baban Marina ya ce ya basu. Mu kuma dukkanin y'aya'n sa muka goyi bayan al'amarin. Aka saka aure idan ta kammala makaratan da wata daya, watanni biyar masu zuwa.
**
Alhaji Auta yana zaune al'amarin duniya ya sake damalmale masa. Gabadaya kasuwa ta juya masa baya fiye da bara. Fatan da yake yi akan kamfani ya kyamaci filin Tijjani saboda an kama shi da laifi bai ci ba. Har asiri yake nema akan su saki filin amma shiru. Su kuwa kamfani sunce riba suke nema. A wajen suke samun gamsuwa, babu ruwansu da laifin Tijjani. Idna lokacin da zasu biya ya yi, zasu tuntubi iyalinsa.
Ya rasa inda zai saka ransa. Jiya aoa kama babban dansa a cikin sahun y'an kidnaffing.
Dazu kuma k'aramin dansa aka kama shi da yana yuwa yarinya yar shekaru uku lalata a cikin gidansa. Gabadaya kwanciyar hankali da nutsuwa ta yi masa tutsu. Ya rame, ya zama tamkar mai ciwon sida, tsufa ya keto masa na ban mamaki.
Yana kishingide amma damuwa ta yi masa k'awanya. Wai shine naira dubu take yi masa wahalar rik'e wa?. Zullimi ya kama shi, idan akwai Bakar Taadar da ya yi ta dame shi bata wuce had'a kai da aka yi da shi wajen yiwa dan amininsa kazafin da yake kulle tsawon shekara guda ba. Ya yi shiru yana tuna irin yadda Tijjani yake zuwa yana gaishe shi cikin girmamawa. Akai akai yake yi masa alheri a matsayinsa na aminin ubansa kuma ubangidansa a kasuwa. Amma shaid'an da hassada suka saka ya jagoranci zaluncin da aka yi masa.
Kuka shabe shabe da hawaye. Ya rasa ta inda zai warware wannan k'ullin da suka yi.
Kan dole ya kira diaya abokin sharrin nasa, wanda yaro ne a kansa dan ba zai girme wa Bulkachuwa ba. Ya dauka murya a shak'e ya ce "Alhaji kana mini waya da ta wuce kaidar hankali gaskiyar magana na ke fad'a maka. Nima nema nake idan zan samu, ka fitine ni da bani bani gaskiya".
Da zullimi ya ce "Ba rokon zan yi ba Haladu! Maganar Tijjani zan yi maka. Gaskiya na yi abin da ya sha mini kai. A harzuke ya ce "To ni me zan yi maka? Ina ce Kai ka kawo shawarar, Kai ka kitsa yadda za'a yi? Ni kawai na karba a hannunsa tare da bawa haro ya ba shi. Hatta lambar wayar da aka kira shi, kai ka siya tun kuma a ranar ka taune shi. Kai ka yiwa Yan sandar hanya shunensa tare da bada lambar motarsa. Kaine zaka yi dakon zunubin ka. Idan ka yi kuskuren saka ni a ciki kuwa Wallahi sai na bata maka suna a idon duniya. Sannan sai na lahanta ka."
Kuka wiwi ta k'wace wa Alhaji Auta tamkar mace.
Ta ya ya zai kubutar da Tijjani?
*Saiwowin maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
95&96.
*HAJIYA HANNE ADO ABDULLAHI?*
*MARUBUCIYAR WANKA DA GARI DA KUMA WACE CE UWA?*
*KUN TUNA IRIN BAJINTAR TA AKAN RUBUTUN ADABI DA TARBIYA?*
*TO ITA MA TAKANAS NA SAMO MUKU LITTAFANTA DOMIN KUN SANI TA YI RUBUTU MASU MA'ANA*.
*LITTAFAN DA YAWA, AMMA AKWAI DISCOUNT DOMIN SO NAKE KU YI TA SIYAWA Y'AYA'NKU DA KANNENKU LITTAFAI MASU DARASI DA MA'ANA*.
*INA MUKU ALBISHIR AKWAI DUKKAN TSOFAFFIN LITTAFAN MARUBUCIYA HAJIYA SALIHA ABUBAKAR ZARIA*
*ZAKU SAME SU SOFT COPIES, A HANNUNA*
*SANNAN SABO DAL NA KAN HANYA*
*HAKA NAN AKWAI WASU DAGA CIKIN LITTAFAN MARUBUCIYA HAJIYA HAFSAT C SODANGI, SUMA SOFT COPIES KAZALIKA ITAMA SABON LITTAFIN TA MA KAN HANYA*
*BA DA JIMAWA BA ZAN ZO MUKU DA SU*.
*08032773332*
*INA MATUKAR GODIYA BISA ADDU'ARKU DA KUMA KAUNARKU GA RUBUTUNA*
*WANNAN SHAFIN SADAUKARWA NE TARE DA GODIYA GA DUKKAN WADANDA SUKA SAKA KUDINSU SUKA SIYI WANNAN LABARIN DON JADDADA MINI SOYAYYA DA KUMA KARFAFA GUIWA*
*NA GODE, NA GODE*.
Auren Aliyu ya samu tasgado. Ba akan komai ba sai akan an kai suka gidansu amaryar cewar d'an-uwansa dan safarar kwaya me gwamnati ta rufe shi Shima ana kyautara zaton yana da BAK'AR TA'ADA. Muna ji muna ga ni aka hana Yaya Aliyu aure ba a akan laifinsa ba. Dama Kuma Babaiba son inda ya dauko auren ba, yar babban attajirice. A raina na Jin ciwon yadda mutanan yau suke yiwa mutane hukunci da laifin yan'uwansu ko na dangunsu alhalin Allah da kansa baya bawa da laifin mahaifansa bare kuma laifin d'an-uwansa. A zuciyata tamkar na ce masa ya nemi Iklima da a yanzu take kwalejin koyon aikin jinya da ke Azare, tana shekarar karshe. A kansu a aka zurfafa karatu ba tare da aure ba a gidanmu. Sun kammala sakandire babu samarin aure. Hakan ya sanya Jabir samowa kannensa gurbin karatu a inda yake koyarwa. Gabadaya mun tafi a cewa iyayensa suka hana ya had'a da ita. Hakan da muka gani ya sanya ni da su Yaya Salisu muka yi kundubalar saka Iklima a Health Technology Azare.
A tsaye take cak, doguwa mai cukar halitta kuma fara tas. Na tabbatar ba zai tankwabe ta ba, amma ina jin tsoron na furta.
Dan haka sai na tsiri gayyato ta hutu a karshen watan da na tabbatar yana yi mana jele. Akai akai suke haduwa kuwa. Su yi ta cakar juna tunda shi ma mai zolaya ne. Ni kuwa na dinga fad'in "um um fa Yaya Aliyu kada fa reshe ya juye da mujiya."
Wani lokacin ya yi dariya ya waske, wani lokacin kuma ya ce "Ba Wani reshe da zai juye, yarinya kankanuwa, raini dai nake son jawo masa.
Baba kuwa idan ta ji ya ce haka sai ta ce "Saboda ka kallafawa ranka son ka auri sa'aninka. Ban da haka ai itacw daidai da kai ".
A duk sadda Babah ta fad'i hakan dad'i ne yake matukar kama ni. Ina ganin nasara a kudirina.
Matukar yana gidan ita zan saka ta yi masa girki, ta dafa masa zobo. Wani lokacin ya yi godiya ya kwashi girki. Wani lokacin ya ce "Tunda na zama matar yayansa na ture girme mini da ya yi, nake mu'amalantarsa a matsayin k'anina. Ban da haka me yake hana ni na yi masa hidima da kaina sai na saka yarinya ta yi masa."
Na yi dariya na ce "Yaya Aliyu ko a lahira wani na cin arzkin wani ai"
Ba'a d'auki lokaci mai yawa ba ya fara fad'awa tarkonmu. Domin idan ya zo bai ganta ba, ya dinga tambayar me ya hana ta zuwa. Ko ba hutu suke yi ba, da sauran tambayoyi. Da na fahimci hakan kuwa sai na dakatar da zuwan nata. Domin so nake ya taka ya neme ta a inda take ba wai sai ya ganta dan ya zo ba.
Ilai kuwa wanne tudu wanne gangare ya silala yake zuwa daga haka har suka had'a kansu.
Tunda aka garkame Tijjani ban yi farin ciki har zuciyata ba sai akan wannan al'amarin. Domin dai Na tabbatar Aliyu mutumin kirki ne. Sannan Babah uwace ta gari bayan haka Ikilima zata auri mai rufin asiri. Zamu sake zargowa k'ofarmu wani hasken.
Bugu da kari y'aya'nmu zasu kasance cikinsu guda. Tunda shi da Tijjani daya ne, haka ni da ita.
Da maganar ta fasu a gidan Marina a lokacin da iyayensa suka je nema amsa aurenta. Ba abin da ba'a ce ba. Bak'in ciki muraran har ce wa aka yi ai k'aramin likita ne, wasu kuwa cewa suka yi ba ma likita ba ne. Malamin tsafta ne. Shi dai Baban Marina ya ce ya basu. Mu kuma dukkanin y'aya'n sa muka goyi bayan al'amarin. Aka saka aure idan ta kammala makaratan da wata daya, watanni biyar masu zuwa.
**
Alhaji Auta yana zaune al'amarin duniya ya sake damalmale masa. Gabadaya kasuwa ta juya masa baya fiye da bara. Fatan da yake yi akan kamfani ya kyamaci filin Tijjani saboda an kama shi da laifi bai ci ba. Har asiri yake nema akan su saki filin amma shiru. Su kuwa kamfani sunce riba suke nema. A wajen suke samun gamsuwa, babu ruwansu da laifin Tijjani. Idna lokacin da zasu biya ya yi, zasu tuntubi iyalinsa.
Ya rasa inda zai saka ransa. Jiya aoa kama babban dansa a cikin sahun y'an kidnaffing.
Dazu kuma k'aramin dansa aka kama shi da yana yuwa yarinya yar shekaru uku lalata a cikin gidansa. Gabadaya kwanciyar hankali da nutsuwa ta yi masa tutsu. Ya rame, ya zama tamkar mai ciwon sida, tsufa ya keto masa na ban mamaki.
Yana kishingide amma damuwa ta yi masa k'awanya. Wai shine naira dubu take yi masa wahalar rik'e wa?. Zullimi ya kama shi, idan akwai Bakar Taadar da ya yi ta dame shi bata wuce had'a kai da aka yi da shi wajen yiwa dan amininsa kazafin da yake kulle tsawon shekara guda ba. Ya yi shiru yana tuna irin yadda Tijjani yake zuwa yana gaishe shi cikin girmamawa. Akai akai yake yi masa alheri a matsayinsa na aminin ubansa kuma ubangidansa a kasuwa. Amma shaid'an da hassada suka saka ya jagoranci zaluncin da aka yi masa.
Kuka shabe shabe da hawaye. Ya rasa ta inda zai warware wannan k'ullin da suka yi.
Kan dole ya kira diaya abokin sharrin nasa, wanda yaro ne a kansa dan ba zai girme wa Bulkachuwa ba. Ya dauka murya a shak'e ya ce "Alhaji kana mini waya da ta wuce kaidar hankali gaskiyar magana na ke fad'a maka. Nima nema nake idan zan samu, ka fitine ni da bani bani gaskiya".
Da zullimi ya ce "Ba rokon zan yi ba Haladu! Maganar Tijjani zan yi maka. Gaskiya na yi abin da ya sha mini kai. A harzuke ya ce "To ni me zan yi maka? Ina ce Kai ka kawo shawarar, Kai ka kitsa yadda za'a yi? Ni kawai na karba a hannunsa tare da bawa haro ya ba shi. Hatta lambar wayar da aka kira shi, kai ka siya tun kuma a ranar ka taune shi. Kai ka yiwa Yan sandar hanya shunensa tare da bada lambar motarsa. Kaine zaka yi dakon zunubin ka. Idan ka yi kuskuren saka ni a ciki kuwa Wallahi sai na bata maka suna a idon duniya. Sannan sai na lahanta ka."
Kuka wiwi ta k'wace wa Alhaji Auta tamkar mace.
Ta ya ya zai kubutar da Tijjani?