← Book details Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 80 OF 146

Sashe 80

Bakar Taada Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read

✍️
*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.

*Oriflame products*
*Daga make up artist din Guduyo*
*Idan kina bukatar Oriflame products ko wanne irin ne, ko Kuma kina sha'awar yin register da su*. *Ki tuntubemi babbar dealer din su Aisha lame*
*Ina kuma fad'a muku akwai da daddan ganyen shayi na Lame Tea*
*Akwai pop corn*
*07036662633*

57&58.
Yini na yi cikin farin ciki. Domin Baban Marina tunda ya dawo cin abinci da azahar, bai fita ba. Zama ya yi muke hira ni da shi domin ba k'aramin da'din ganina ya yi ba.
Sai da aka fara kiran sallar la'asar sannan muka yi sallama ya fice.
Sai dare kuwa muka tafi kamar yadda ya yi mini al'kawari. Albarka na sha ta daga wajen mahaifana har da Dada ma.
A k'ofar gida ina shirin d'ale wa mashin din, sai ga Baban Tsakiya. Na yi kamar ban gan shi ba, na dauke kai. Tijjani ya mini inkiyar na gaishe shi amma na waske. Sai shine da kansa ya ce "Tijjani wannan ba Yabi ba ce?".
Kafin ya ba shi amsa Na rusuna ka'dan na ce "Baban Tsakiya ina yini".
Ya ce "Ai har yanzu ba zaki daina kama suna da inkiya ba?" Ban ce komai ba daga hakan. Na haye mashin d'in ko kunyarsa ban ji ba. Duk da yana kallona haka na dafa Tijjani da zan hau din, tunda har yau ba zai shafa mini lafiya ba.
Ya kad'a kai ya ce "Tijjani Allah ya k'ara maka hakuri da juriya".
Ya kasa amsa masa, amma gaba'daya na ga ya yi wani iri.
Kafin ya ja mashin din sai ga J ya fito da alamu tare suke da mahaifin nasa.
Ya mika wa Tijjani hannu suka gaisa.
Hasken solar da gwamnati ta kafa akan layika ta haske fuskokinmu tunda muna da ita a k'ofar gidanmu.
Karon farko da na kalle shi ban ji wani abu na so ko na burge wa ya taso mini ba.
Domin ko ranar da muka je gidansa yin barka sai da tsumin sonsa ya taso mini.
Na bu'de baki na ce Yaya J ina yini, ya Baby?"
Da wani irin yanayi ya ce "Lafiya k'alau Yabi. Ya kike, ya ruwa?"
Na amsa da Alhamdulillah".
Daga haka Tijjani ya ja mashin dinsa muka wuce.
Lafiya k'alau muka isa gidan, muka gama uzzirinmu muka kwanta. Tsawon lokaci ina jiran na ji hannunsa a jikina shiru. Na dinga mutsu mutsu, amma bai motsa ba. Da k'yar na samu barci ya sure ni. Da asuba ma hakan ya yi, ga shi ya riga ya sabar mini da al'amarin dare da asuba basa wuce mu sai idan fashin sallah nake yi. Shi ma sai mun yi abubuwan da zamu samu nutsuwa.
Na rasa yadda zan yi, domin kunya ta hana na fara kai hannuna gare shi.
Na daure dai nima na share. Muka koma barci. Ni na fara tashi, na gyara gidan, na duba na ga akwai taliyar hausa. Nasan kuma yana sonta sosai. Sai kawai na d'ora jolof d'in ta.
Ina shirin gamawa na ga ya fito ya yi band'aki. Can kuma ya fito da brush dinsa ya zauna daga gefe ya yi, sannan ya mayar ya ajiye.
Maimakon ya shigo kicin ya taya ni mu k'arasa kamar yadda ya saba sai kawai na ga ya yi falo.
Na fara jin wani iri a dalilin sauyinsa. Na dinga tunanin me ya faru. Amma na kasa gano ko na yi masa wani abu.
Na gama, na tafasa shayi. Na ha'da komai na kai falon.
Muka fara karyawa amma babu doguwar hira yadda ya saba mini.
Muna zaune, jigum jigum yaro ya yi sallamah daga ba'kin k'ofa ya ce "Wai ana sallama da Tijjani".
Na zabura na ce "Kai shigo". Ya shigo na kare masa kallo, gaba'daya ba zai wuce shekaru takwas ba.
Na zare masa ido a dalilin na ji haushin gatsa sunan da ya yi. Na ce "Ba zaka ce ana sallama da maigidan ba sai ka wani gatsa sunasa tamkar sa'an ka. Zaka iya fa'din sunan Babanku gatsal?"
Yaron ya yi shiru yana kallona da alamu ma tsorata ya yi kada na rufe shi da duka.
Sai lokacin Bulkachuwa ya ce "Kai je ka ce "Ina zuwa".
Ya mik'e ya bar ni.
Tunda ya fita sai yamma ya dawo. Bai ce mini ga inda ya je ba, nima ban tambaya ba. Na gabatar masa da ruwa da abinci na yi tafiyata wajen k'unshina. Domin na fara jin haushin daddaurewar da yake yi mini haka siddan.
Haka da daddare ma ya sake matse wa bai ta'ba ni ba.
Kwanaki uku ke nan, muna haka, na fara k'osawa domin gaskiya ya riga ya yi mini sabo a harkar, tun ina turjiya, ina raki har na zama yar hannu da al'amarin nasa. Sannan na fahimci nima irin halittarsa ce da ni. Ina son harkar, ina jin da'din ta.
Ban sani ba ko ya fahimci hakan ne shi yasa zai fara yi mini gayya.
Sai na yun'kura zan tambaye shi dalilin sauyinsa sai na yi maza na fasa. Ina jaddada wa zuciyata na ja ajina. Shi da yake namiji ma ya yi jarumtar runtsi idonsa daga gare ni, sai ni mace ce zan k'osa?.
Dan haka na yi hakuri, na zuba masa ido, amma gaba'daya bana cikin nutsuwa. Mussaman idan ya shek'a kwalliya ya baza turare sai na ji tamkar na yi tsalle na mak'ale shi.
Sai ya fita nake samun damar na yi kukana. Ina ayyana wai ni Tijjani yake yiwa wannan wula'kancin haka siddan dan ya fahimci na fara sonsa.
Na fara zargin akwai abin da yake yi a waje da ya sanya yake iya kawar da kansa a kaina.
Gaba'daya na rasa sukuni. Na yi wani iri.
Ranar da muka yi kwana hudu a cikin wannan halin. Gaba'daya ya juye mini, tamkar ba shine mai rawar jiki da tsoron ganin fishina ba. Tamkar ba shine mai kulafacina kamar me ba.
Ranar da wuri ya shigo. Na yi wanka na sanya riga da wando silky. Wando iya guiwa rigar ma iya tsayinta kenan wando kawai ta rufe.
Na taje gashina da yake a tsefe na mulke shi da man gashi na kwakwa da asalain man alaiyadi. Na dauko turarena na mai maiko na oudi na murtsike hannayena da jikina har ma da gashin. Na sake dauko turaren active woman da Tijjani ya canja mini na bi jikina na feshe. Na saka hula marar nauyi kalar kayan barcin nawa.
Na fita na same shi yana kallon labaran NTA Bauchi.
Na zauna ya dago ya kalle ni. Domin na tabbatar kamshina ya kai masa caffa mai yawa.
Na sassauta na ce "Wai mun b'ata ne?"
Cikin nutsuwa ya ce "Da yaushe?"
Na yi sakare ina kallonsa. Na numfasa na ce"Ai tambayar ka na yi."
Ya girgiza kai ya ce "To ke mun b'ata ne?"
Na rasa me zan ce masa ma. Na nisa na ce "Nasan bamu b'ata ba. Amma na ga ka sauya ne".
Ya daure fuska ya ce "Tun yaushe na canja d'in?"
Na ce "Tun kwanaki hudu, tun ranar da ka kai ni gida".
Ya yi shiru tsawon lokaci kafin ya bu'de baki ya ce "Kuma sai yau kike bu'katar sanin dalilin sauyin nawa saboda baki d'auke ni a bakin komai ba?"
Ga mamakina sai na shiga rud'u na ce "To ai kai ne zaka fa'da mini."
Ya girgiza kai ya ce "Babu damuwa ki cigaba da zaman jiran na fa'da miki".
Idona ya ciko da k'walla. Na zuba masa ido sosai na nuna kaina da yatsana na ce "Ni kake wula'kantawa saboda kawai ka shiga ka fita kasa na saba da kai ko?.
Ai shike nan na gode".
Daga hakan na kifa kaina a hannun kujerar na fashe da kuka mai tsananin gaske.
Ya taso da azama ya zauna kusa da ni. Ya ru'ko ni na fizge tare da ce wa "Ba ruwanka da ni, komai kake yi na barwa Allah. Ka cigaba da yi mini wula'kanci komai lokaci ne ai, watarana ba zaka yi ba".
Ya sake tarairayo ni jikinsa yana kamo weak points dina. Jikina ya fara tsuma. Amma na sake k'wace wa na mike, cikin muryar kuka na ce "Bana so Tijjani, ka bari na fa'da maka".
Na fice na yi d'akina ina kuka sosai.
Sai da ya yi wanka sannan ya shigo d'akin har lokacin kuma ina dukunkune ina kuka sosai.
Sai da ya yi shafa'i da wutiri sannan ya tarar da ni a gadon.
Bai kwanta ba. Ya zauna ya kaurara murya ya ce "Asiya tashi mu yi magana."
Na share shi, na k'i na nuna ma na ji shi.
Ya saka hannunsa biyu ya d'aga ni ya zaunar da ni.
Na sake yun'kurin koma wa na kwanta dan na nuna masa ba ni da lokacinsa, sai kawai na ji ya bu'de murya sosai ya ce "Wallahi idan kika kwanta idan ranki sun kai dubu ki tabbatar sai na bisu d'aya bayan d'aya na b'ata su."
Jin ya rantse sai na zauna din. Amma na tattaro dukkan fishi na yab'a a fuskata.
Ya jima yana kallon yadda nake tunbatsa.
Shima ya d'aure tasa fuskar ya ce "Ki saurare ni da kunnen basira Asiya Toro".
Jin ya fadi wannan sunan na sake hassala ainun.
Ya furzar da iskar baki ya ce "Ranar da muka je gida kin wula'kanta ni, kin tozarta ni!
Watannin baya na fa'da miki, ba zai yiwu a gabana ki wula'kanta iyayenmu ba. Idan kin ture girmansu na k'annen mahaifinki ne, to ki sani baki isa ki ture nasabarsu da ni ba. Ina kuma da hak'kin ki mutunta iyayena. Dole ne, wajibi ne Asiya ki mutunta mini dangin uwata matu'kar kina son mu zauna lafiya. Ba zai yiwu ina aurenki kuma in zuba miki ido ki dinga yin rashin mutunci ba. Bilhiillazi wannan ne karon k'arshe da zaki ga wani cikin iyayenmu ki k'i gaishesu, ko ki yi musu gaisuwar je ka na yi ka".
Na fara kuka ina ce wa "To ina ruwanka ne kam. Kai baka ga irin k'iyayyar da suke yi mini ba? Saboda baka kishina, saboda kai sun yarda gyatumarka yar'uwarsu ce shiyasa kake ganin bekena. Duk abubuwan da suke yiwa ubanmu baku da kaico. Ai ka sani ba sai na fa'da ba, ko auren nan nawa sun yi sanadinsa ne dan kawai suna ganin bazan cigaba ba.
Amma da sun tabbatar zan samu nutsuwa a cikinsa a sai sun rugurguza shi. Yanzu ma kuwa nasan akwai lokacin da zai zo da zasu rabamu tunda zuciyarsu mai k'yashi ce."
Ya buge mini baki ya ce "Kada ki kuskura ki fa'di maganar banza a kansu a gabana. Dole fa ki mutunta su a matsayin surakanki tunda ke kin yanke nasabar da ta hada ku".
Cikin gigita na ce "To ka sake ni, bana son yin surukuta da su. Kai ma bana sonka Tijjani".
Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
* Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*
Chapter 80 · 0% Book details